Sashe 36
Kwantan Bauna Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Habiba tace, "y'ar hutu. Lafiya kike nema na?." Rauda tace, "Yan uwa ina cikin matsala ne." A tare suka had'a baki wajan fad'in, "Wacce irin matsala kuma?."
Shiru Rauda tayi tana kallon su kafin ta kwashe duk abinda ya faru tayi ta fad'a musu kafin ta d'ora da fad'in, "tunda kika ce min har fyad'e ya yiwa y'ar sarkin Zamfara na tsorata ku taimaka min dan Allah."
Girgiza kai suke yi cikin mamaki da tsoro Habiba tace, "Mahaukaci kika ce masa Rauda? Tabd'ijam na rantse da Allah bai k'yale ki ba kina nan a zuciyar sa sai ya d'auki mataki a kan ki, ya yiwa yar masu kud'i da mulki balle irin mu?." Sai ta fashe da kuka tana fad'in, "Dan girman Allah ku taimaka min ku nema min mafita wallahi tsoron sa nake ji, ni ko zuwa ne zanyi na bashi hak'uri indai zai yafe min."
Habiba tayi shiru tana tunanin m a fita kafintace, "mafita d'aya ce kawai abinda za'ayi zuwa zamuyi mu samu Asad ki fad'a masa duk abinda ya faru tunda a gaban sa akayi, ki sanar dashi tsoro kike ji kuma kinyi dana sanin yi masa rashin kunya dan Allah ya bashi hak'uri kar yayi maki komai, in anyi sa'a zai iya k'yalewa in Asad d'in ya saka baki."
Walida tace, "To kince sai ya kwana uku bai fito ba a ina zamu gan shi?." Habiba tace, "yana sadaka ai da kansa ranar juma'a bayan masallaci indai yana k'asar nan, ranar zamu je masa in ba ranar ba wallahi bamu da ikon ganin sa."
"Juma'a yayi nisa Habiba, kafin juma'ar zai iya sakawa ayi min wani abun, dan Allah a canja shawara. Ni tsoron abinda zai min nake yi bawai tsoron sa ba, ga Ummana bana so ta shiga wani yanayi mara dad'i a kaina shiyasa hankalina ya tashi sosai" Rauda ta fad'a cikin tashin hankali tana hawaye tana kallon su.
Cikin kwantar da murya Habiba tace, "Na rantse da Allah Rauda da ina da damar ganin Asad a yau zamu je wajan sa amma ban isa ba, Fulani ta saka an k'arawa b'angaren su tsaro sabida abinda ya faru dashi kwanaki kusa da wajan ma baki isa kaje ba sai da dalili. ki bari sai ranar jama'ar in Allah ya nuna mana sai muje ki same shi na tabbatar bazai bari a cutar dake ba, Kafin ranar ki ta addu'a Allah zai kawo miki sauk'i."
"Habiba in ya yi min wani abun na shiga uku dan Allah ku taimake ni. Ba kaina nake ji ba Ummana nake ji, abinda Baba zai yiwa Umma shi nake jin tsoro" ta fad'a cikin kuka sosai. Tausayi ta basu suka dinga rarrashin ta Habiba tace, "Allah yana tare dake wallahi bai isa ya cutar dake ba. Amma zan je yanzu in naga yana nan zan roƙe shi zance masa zan kawo ki ki masa bayanin komai in yaso sai naje na dawo muje wajan sa dake."
Rauda tace, "tashi kije Habiba." Habiba ta mik'e tsaye tace, "Walida zo muje, duk yadda ake ciki zan dawo" ta fad'a tana fita daga gidan suka barta tana sharb'ar kuka.
Haka ta zauna zaman jiran su har la'asar basu dawo ba Umma ma bata dawo ba sai biyar sannan Khairi ta shigo ita da Khalil da Sammani, bayan shigowar su ba jima Habiba ta shigo tunda taga fuskar ta tana ba'a yi nasara ba. Kusa da ita ta zauna ta kalle ta tace, "Wallahi duk yadda naso ganin Asad abin ya gagara, amma kiyi hak'uri gobe zan same shi in Allah ya yarda." Idanun Rauda yayi rau-rau zatayi kuka Habiba tace, "kiyi hak'uri dan Allah, haba komai zai tafi daidai in Allah ya amince ki yadda dani wallahi zan masa magana. Kamar ba ke ba kinbi kin rud'e keda na sanki da dakakkiyar zuciya wacce babu tsoro a cikin ta."
Kai ta girgiza tace, "Habiba wannan fad'an yafi k'arfina, bawai ina jin tsoron saba bane ina jin tsoron abinda zaiyi min ne Habiba."
"In sha Allah babu abinda zai miki."
"Na gode Habiba." Habiba ta mik'e tace, "Kar ki damu zan neme shi gobe in Allah ya amince."
"Na gode" ta furta a hankali daga haka sukayi sallama ta tafi.
Fitar ta ba jimawa Umma ta dawo su ma su Rahma suka dawo, bayan anyi sallar magriba Baba ya dawo bayan yaci abinci ya shigo tsakar gidan ya zauna ya kalli Rauda yace, "Rauda." Tace, "Na'am Baba."
"D'azu Anas ya kira ni ya sanar dani tafiya ta taso masa ta gaggawa bai samu yayi magana da likitan naki ba, amma ba jimawa zaiyi ba da zarar ya dawo za'ayi komai a gama. Ya aiko da waya yace dan Allah a baki yana so ku dinga magana na kuma karb'a, gata" ya fad'a yana mik'a mata ledar Khairi da take kusa dashi ta karb'a ta mik'a mata.
Umma ta kalli Baba ta kasa jure abinda take ranta tace, "Malam wai ka bawa yaron nan auren Rauda ne?." Ya kama k'ugu yace, "Me yasa kika tambaya?."
"Sabida naga kana karb'ar hannun sa da yawa, tsakani da Allah bai kamata ba a dinga karb'ar kud'in yaron nan ko abin hannun sa ba tunda ba'a yi auren su ba, ko maganar aure fa bata shiga tsakanin su ba."
Baba yace, "to fad'a min ke kika haife ta, dad'in ta nima dani aka haife ta ba ke kad'ai kika kawo ta duniya ba. Na riga na bashi auren ta koda bana raye shi zata aura ba wani ba, ko ban isa bane ba?" Ya fad'a yana kallon Umma. Umma bata kuma cewa komai ba ta kawar da kai yaja tsaki ya fita.
Rauda tunda aka bata wayar ta rik'e a hannun ta ko bud'ewa ta kasa yi sabida ba wannan ne a zuciyar ta ba abinda yake zuciyar ta daban wannan daban, sai da suka shiga d'aki zasu kwanta sannan Khairi ta bud'e wayar a kwalin ta ta ciro ta kunna har da sim card a kai, Khairi ta kalle ta taga ba ita take kallo ba tace, "Anty Rauda keda kike da burin rik'e waya yau Allah ya cika miki burin ki amma ban ga kina farin ciki ba."
Umma tace, "ta yaya zatayi farin ciki ana zubar mata k'ima wajan saurayi ana karb'ar komai daga hannun sa?, ai farin ciki ba nata ba." Rauda ta kalli wayar hannun Khairi ta ganta mai kyau babba ga bayan ta nan da logo d'in Samsung. D'auke kai tayi ta kwanta kawai bata ce komai ba domin ita ba wannan ne yake damun ta ba.
*☆☆☆*
Asad kuwa da ya bar gida gidan su Jidda ya tafi ya riga ya cewa Mama zashi baya son sab'a alqawari a rayuwar sa musmman ma maganar Mama. Kasancewar gidan sa ba bak'on sa bane Mama tana aiko shi wani lokacin har cikin gidan ya ajjiye motar.
Fita yayi daga motar ya shiga cikin gidan da sallama ya samu falon babu koma sai k'anwar Jidda mai suna Eman.
Ganin sa ta saka tayi murmushi tace, "Yaya Aliyu ina wuni."
"Lafiya, Ina Mum?."
"Tana sama bara na fad'a mata" ta fad'a tana hawa sama. Bai zauna ba ya tsaya a tsaye kafin ta lek'o tace, "Tace ka hayo." Ba musu ya k'arasa stairs d'in ya hau saman a nutse ba tare da wata fargaba ba. A babban falo ya tarar dasu ita da Jidda a zaune ganin sa ya saka Jidda mik'ewa ta k'araso gare shi da niyar hugging d'in sa.
Baya yayi yana kallon ta ta k'asan ido, sanye take da riga da wando yan kanti kanta babu d'ankwali gashin ta ya sauka har kafad'a tayi kyau kamar baturiya, ganin kallon da yayi mata sai gaban ta ya fad'i ta kauce ya k'arasa ya zauna kana yace, "Mum ina wuni."
"Lafiya lau Aliyu, Ya Maman?."
"Lafiya lau" ya furta a tak'aice bai kuma cewa komai ba.
Jin shiru ya saka Mum ta kalle shi dan tasan Aliyu baya wannan dabi'ar in yazo gidan da tuni ya rungume Jidda sun koma gefe suna hirar su tace, "Aliyu kayi shiru yau kamar ba kai ba."
"Asad!" Ya furta a tak'aice bai kalli Mum d'in ba. Jin abinda yace ya saka Mum da Jidda suka kalli Juna Mum ta d'aga mata gira suna murmushi Mum tace, "Au daman Asad ne ka barni ina ta kiran ka da Aliyu?." Baice komai ba itama bata damu yace ba dan tasan bazai ce ba ta kalli jidda tace, "Jeki ki kawo masa abin tab'awa mana kin tsaya kina kallon sa." Da sauri ta juya ta sauka Mum tayi murmushi tana kallon sa tace, "nidai nayi mamaki nasan Aliyu baya irin wannan bakuntar a gidan nan."
In table d'in dake gaban sa ya amsa to tabbas shima ya bata amsa sai ma kawar da kansa gefe da yayi yana jin sa a takure, bata damu ba dan tasna halin sa daman a lokacin Rauda ta dawo da tray a hannun ta ta ajjiye masa ta zauna a gefen sa Mum ta mik'e ta basu waje. Suna zaune shiru babu mai magana zuciyar sa ta tafi tunanin kenan daman ta saba hugging d'in Aliyu duk wanda yazo tunda gashi da ta ganshi ta d'auka shine har ta nufo shi da niyar hugging d'in sa. Cize baki yayi Allah ya sani baya son yaga wani ya rabi abinda aka ce nasa ne indai har da gaske nasa d'in ne baya so yaga wani abun ya rabe shi, baya son hakan sam.
"My Asad" ta furta a hankali tana kallon sa. Bai kalle ta ba ya sauke ajiyar zuciya yace, "Zaki iya d'aukar wayar ki?" Ya fad'a da harshen laranci. Kallon sa tayi alamun bata gane ba tace, "Bana jin Arabic." Yamutsa fuska yayi yace, "Take your phone."
"Okay." ta furta tana d'aukar wayar ta. Sai kuma ya tsaya kallon wayar tasa tunawa da yayi bashi ma fa da number ta balle suyi chart ya fad'a mata abinda ya kawo shi.
D'an k'aramin tsaki yaja ya ajjiye wayar kamar zai magana sai kuma ya fasa.
Shiru Rauda tayi tana kallon su kafin ta kwashe duk abinda ya faru tayi ta fad'a musu kafin ta d'ora da fad'in, "tunda kika ce min har fyad'e ya yiwa y'ar sarkin Zamfara na tsorata ku taimaka min dan Allah."
Girgiza kai suke yi cikin mamaki da tsoro Habiba tace, "Mahaukaci kika ce masa Rauda? Tabd'ijam na rantse da Allah bai k'yale ki ba kina nan a zuciyar sa sai ya d'auki mataki a kan ki, ya yiwa yar masu kud'i da mulki balle irin mu?." Sai ta fashe da kuka tana fad'in, "Dan girman Allah ku taimaka min ku nema min mafita wallahi tsoron sa nake ji, ni ko zuwa ne zanyi na bashi hak'uri indai zai yafe min."
Habiba tayi shiru tana tunanin m a fita kafintace, "mafita d'aya ce kawai abinda za'ayi zuwa zamuyi mu samu Asad ki fad'a masa duk abinda ya faru tunda a gaban sa akayi, ki sanar dashi tsoro kike ji kuma kinyi dana sanin yi masa rashin kunya dan Allah ya bashi hak'uri kar yayi maki komai, in anyi sa'a zai iya k'yalewa in Asad d'in ya saka baki."
Walida tace, "To kince sai ya kwana uku bai fito ba a ina zamu gan shi?." Habiba tace, "yana sadaka ai da kansa ranar juma'a bayan masallaci indai yana k'asar nan, ranar zamu je masa in ba ranar ba wallahi bamu da ikon ganin sa."
"Juma'a yayi nisa Habiba, kafin juma'ar zai iya sakawa ayi min wani abun, dan Allah a canja shawara. Ni tsoron abinda zai min nake yi bawai tsoron sa ba, ga Ummana bana so ta shiga wani yanayi mara dad'i a kaina shiyasa hankalina ya tashi sosai" Rauda ta fad'a cikin tashin hankali tana hawaye tana kallon su.
Cikin kwantar da murya Habiba tace, "Na rantse da Allah Rauda da ina da damar ganin Asad a yau zamu je wajan sa amma ban isa ba, Fulani ta saka an k'arawa b'angaren su tsaro sabida abinda ya faru dashi kwanaki kusa da wajan ma baki isa kaje ba sai da dalili. ki bari sai ranar jama'ar in Allah ya nuna mana sai muje ki same shi na tabbatar bazai bari a cutar dake ba, Kafin ranar ki ta addu'a Allah zai kawo miki sauk'i."
"Habiba in ya yi min wani abun na shiga uku dan Allah ku taimake ni. Ba kaina nake ji ba Ummana nake ji, abinda Baba zai yiwa Umma shi nake jin tsoro" ta fad'a cikin kuka sosai. Tausayi ta basu suka dinga rarrashin ta Habiba tace, "Allah yana tare dake wallahi bai isa ya cutar dake ba. Amma zan je yanzu in naga yana nan zan roƙe shi zance masa zan kawo ki ki masa bayanin komai in yaso sai naje na dawo muje wajan sa dake."
Rauda tace, "tashi kije Habiba." Habiba ta mik'e tsaye tace, "Walida zo muje, duk yadda ake ciki zan dawo" ta fad'a tana fita daga gidan suka barta tana sharb'ar kuka.
Haka ta zauna zaman jiran su har la'asar basu dawo ba Umma ma bata dawo ba sai biyar sannan Khairi ta shigo ita da Khalil da Sammani, bayan shigowar su ba jima Habiba ta shigo tunda taga fuskar ta tana ba'a yi nasara ba. Kusa da ita ta zauna ta kalle ta tace, "Wallahi duk yadda naso ganin Asad abin ya gagara, amma kiyi hak'uri gobe zan same shi in Allah ya yarda." Idanun Rauda yayi rau-rau zatayi kuka Habiba tace, "kiyi hak'uri dan Allah, haba komai zai tafi daidai in Allah ya amince ki yadda dani wallahi zan masa magana. Kamar ba ke ba kinbi kin rud'e keda na sanki da dakakkiyar zuciya wacce babu tsoro a cikin ta."
Kai ta girgiza tace, "Habiba wannan fad'an yafi k'arfina, bawai ina jin tsoron saba bane ina jin tsoron abinda zaiyi min ne Habiba."
"In sha Allah babu abinda zai miki."
"Na gode Habiba." Habiba ta mik'e tace, "Kar ki damu zan neme shi gobe in Allah ya amince."
"Na gode" ta furta a hankali daga haka sukayi sallama ta tafi.
Fitar ta ba jimawa Umma ta dawo su ma su Rahma suka dawo, bayan anyi sallar magriba Baba ya dawo bayan yaci abinci ya shigo tsakar gidan ya zauna ya kalli Rauda yace, "Rauda." Tace, "Na'am Baba."
"D'azu Anas ya kira ni ya sanar dani tafiya ta taso masa ta gaggawa bai samu yayi magana da likitan naki ba, amma ba jimawa zaiyi ba da zarar ya dawo za'ayi komai a gama. Ya aiko da waya yace dan Allah a baki yana so ku dinga magana na kuma karb'a, gata" ya fad'a yana mik'a mata ledar Khairi da take kusa dashi ta karb'a ta mik'a mata.
Umma ta kalli Baba ta kasa jure abinda take ranta tace, "Malam wai ka bawa yaron nan auren Rauda ne?." Ya kama k'ugu yace, "Me yasa kika tambaya?."
"Sabida naga kana karb'ar hannun sa da yawa, tsakani da Allah bai kamata ba a dinga karb'ar kud'in yaron nan ko abin hannun sa ba tunda ba'a yi auren su ba, ko maganar aure fa bata shiga tsakanin su ba."
Baba yace, "to fad'a min ke kika haife ta, dad'in ta nima dani aka haife ta ba ke kad'ai kika kawo ta duniya ba. Na riga na bashi auren ta koda bana raye shi zata aura ba wani ba, ko ban isa bane ba?" Ya fad'a yana kallon Umma. Umma bata kuma cewa komai ba ta kawar da kai yaja tsaki ya fita.
Rauda tunda aka bata wayar ta rik'e a hannun ta ko bud'ewa ta kasa yi sabida ba wannan ne a zuciyar ta ba abinda yake zuciyar ta daban wannan daban, sai da suka shiga d'aki zasu kwanta sannan Khairi ta bud'e wayar a kwalin ta ta ciro ta kunna har da sim card a kai, Khairi ta kalle ta taga ba ita take kallo ba tace, "Anty Rauda keda kike da burin rik'e waya yau Allah ya cika miki burin ki amma ban ga kina farin ciki ba."
Umma tace, "ta yaya zatayi farin ciki ana zubar mata k'ima wajan saurayi ana karb'ar komai daga hannun sa?, ai farin ciki ba nata ba." Rauda ta kalli wayar hannun Khairi ta ganta mai kyau babba ga bayan ta nan da logo d'in Samsung. D'auke kai tayi ta kwanta kawai bata ce komai ba domin ita ba wannan ne yake damun ta ba.
*☆☆☆*
Asad kuwa da ya bar gida gidan su Jidda ya tafi ya riga ya cewa Mama zashi baya son sab'a alqawari a rayuwar sa musmman ma maganar Mama. Kasancewar gidan sa ba bak'on sa bane Mama tana aiko shi wani lokacin har cikin gidan ya ajjiye motar.
Fita yayi daga motar ya shiga cikin gidan da sallama ya samu falon babu koma sai k'anwar Jidda mai suna Eman.
Ganin sa ta saka tayi murmushi tace, "Yaya Aliyu ina wuni."
"Lafiya, Ina Mum?."
"Tana sama bara na fad'a mata" ta fad'a tana hawa sama. Bai zauna ba ya tsaya a tsaye kafin ta lek'o tace, "Tace ka hayo." Ba musu ya k'arasa stairs d'in ya hau saman a nutse ba tare da wata fargaba ba. A babban falo ya tarar dasu ita da Jidda a zaune ganin sa ya saka Jidda mik'ewa ta k'araso gare shi da niyar hugging d'in sa.
Baya yayi yana kallon ta ta k'asan ido, sanye take da riga da wando yan kanti kanta babu d'ankwali gashin ta ya sauka har kafad'a tayi kyau kamar baturiya, ganin kallon da yayi mata sai gaban ta ya fad'i ta kauce ya k'arasa ya zauna kana yace, "Mum ina wuni."
"Lafiya lau Aliyu, Ya Maman?."
"Lafiya lau" ya furta a tak'aice bai kuma cewa komai ba.
Jin shiru ya saka Mum ta kalle shi dan tasan Aliyu baya wannan dabi'ar in yazo gidan da tuni ya rungume Jidda sun koma gefe suna hirar su tace, "Aliyu kayi shiru yau kamar ba kai ba."
"Asad!" Ya furta a tak'aice bai kalli Mum d'in ba. Jin abinda yace ya saka Mum da Jidda suka kalli Juna Mum ta d'aga mata gira suna murmushi Mum tace, "Au daman Asad ne ka barni ina ta kiran ka da Aliyu?." Baice komai ba itama bata damu yace ba dan tasan bazai ce ba ta kalli jidda tace, "Jeki ki kawo masa abin tab'awa mana kin tsaya kina kallon sa." Da sauri ta juya ta sauka Mum tayi murmushi tana kallon sa tace, "nidai nayi mamaki nasan Aliyu baya irin wannan bakuntar a gidan nan."
In table d'in dake gaban sa ya amsa to tabbas shima ya bata amsa sai ma kawar da kansa gefe da yayi yana jin sa a takure, bata damu ba dan tasna halin sa daman a lokacin Rauda ta dawo da tray a hannun ta ta ajjiye masa ta zauna a gefen sa Mum ta mik'e ta basu waje. Suna zaune shiru babu mai magana zuciyar sa ta tafi tunanin kenan daman ta saba hugging d'in Aliyu duk wanda yazo tunda gashi da ta ganshi ta d'auka shine har ta nufo shi da niyar hugging d'in sa. Cize baki yayi Allah ya sani baya son yaga wani ya rabi abinda aka ce nasa ne indai har da gaske nasa d'in ne baya so yaga wani abun ya rabe shi, baya son hakan sam.
"My Asad" ta furta a hankali tana kallon sa. Bai kalle ta ba ya sauke ajiyar zuciya yace, "Zaki iya d'aukar wayar ki?" Ya fad'a da harshen laranci. Kallon sa tayi alamun bata gane ba tace, "Bana jin Arabic." Yamutsa fuska yayi yace, "Take your phone."
"Okay." ta furta tana d'aukar wayar ta. Sai kuma ya tsaya kallon wayar tasa tunawa da yayi bashi ma fa da number ta balle suyi chart ya fad'a mata abinda ya kawo shi.
D'an k'aramin tsaki yaja ya ajjiye wayar kamar zai magana sai kuma ya fasa.