Sashe 38
Kwantan Bauna Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Karen sai da yayi wata girgiza gashin jikin sa ya mik'e sannan ya fara nufo ta a hankali yana sake zaro harshen sa, idanun sa ma da jikin sa abin tsoro ne shiyasa tunda ya tunkaro ta ta runtse idanun ta tana salati dan ta tabbatar k'arshen tane yazo babu abinda zai hana Karen bai kashe ta ba. Razananniyar k'arar da tayi shine ya saka su kallon inda take da gaggawa.
*KWANTAN ƁAUNA*
©️ *Nana Haleema.*
*Book 1*
*018.*
Cizo ya kawo mata karen shine ya saka ta yin k'ara ta kulle idanun ta tana jiran taji sukar hakoran sa a a naman ta amma sai taji shiru, ta bud'e idanun ta a hankali taga karen baya gaban ta kamar d'azu ta juya gefen ta ta ganshi a tsaye ya juyo yana kallon ta kusa da wanda bata tantance waye ba. A hankali yake takowa yazo kusa da ita suka had'a ido sai jikin ta ya cigaba da tsuma ya had'e hannayen ta waje guda tana kuka amma ta kasa magana.
D'auke kai yayi daga kanta ya kalli wad'anda suka sato ta sai suka zube a k'asa cikin girmamawa hannun su na jinjina d'aya yace, "Tuba muke ranka ya dad'e, zamu aikata abinda ka umarce mu yanzu, ka yafe mana zamu yi."
"Aliyu ya saka ku kawo ta nan?" Ya fad'a a tausashe cikin muryar sa mara hayaniya wacce bata fita sosai yana kallon su.
Sai a sannan suka gane bafa Aliyu ne a gaban su ba babar giwa ce da kanta sai jikin su ya k'ara kaimi wajan tsuma d'aya yace, "Kayi mana aikin gafara ranka ya dad'e. Yarima Aliyu ne ya umarce mu da mu kawo ta nan mu sakar mata Bobby ya cize ta sannan muyi abinda muke so da ita. Mun tuba wallahi baza mu sake aikata hakan ba." Kai Asad yake girgizawa kaf yasan plan d'in nasu sune da Aliyun basu san ya sani bane amma tunda yasa a fara tracking d'inta yasan da haka.
Kallon da yayi musu ya saka jiki su rawa suka fara fad'in, "Kiyi hak'uri yarinya muma ba san ran mu bane ba wallahi saka mu akayi babu yadda zamu yi, kiyi hak'uri ki yafe mu." Kanzil Rauda bata ce ba sai kuka da take mai tsuma zuciya ya sake kallon su duk sai suka sake diriricewa dan basu fahimcin kallon na meye ba.
D'aya ne ya mik'e da sauri ya kawo mata sandinan ta guda biyu yace, "kiyi hak'uri." Da hannu yayi musu alamun da su wuce su tafi a da sauri suka hau mota suka ja da gudu. Dawo da kallon sa yayi kanta yadda jikin ta yake tsuma tana kuka hakan ya tabbatar masa da ba k'aramin tsoro take ji ba sai ta sake bashi tausayi yana so yayi mata magana amma bai san me zaice ba.
Yana tsaye tana kuka sai da ta gaji dan kanta sannan ta fara k'ok'arin tashi tsaye, bata iya tsayuwa da k'afafun ta hakan ya saka tashi yake gagarar ta ganin sai juyi take kamar wancan lokacin ya saka shi mik'ar da ita tsaye ya bata sandar ta rik'e sai kuma ta dafe kai da hannayen ta guda biyu jin yadda yake sarawa. Bata daina kuka bai kuma ce komai ya juya wajan motar sa ya shiga karen shiga mazaunin baya ya dawo da motar daidai kusa da ita amma har lokacin bai ce k'ala ba.
Wajan take kallo babu alamun abin hawa in tak'i shiga motar ta cuci kanta dan bata san a inda take ba balle tabi hanyar da zata sami mota, tana so ta shiga amma rashin yi mata magana da baiyi ba ya saka take shakka kar ta shiga ya wulaqanta ta.
Sauke glass d'in gefen ta yayi da hannu yayi mata alama da ta shiga a sanyaye ta ja handle d'in motar ya bud'e, so take ta fara saka sanda guda d'aya sannan ta shiga sai ta shigo da d'ayar amma ta kasa ta rasa yadda zatayi. Babu tsammani taga ya fito daga motar ya dawo inda take ya karb'o guda d'aya ya saka a ciki ta saka k'afar ta mai lafiyar ta shiga cikin motar, saka mata d'aya sandar yayi kana ya kulle k'ofar ya zaga ya shiga.
Ganin ta yayi duk a tsorace tana kallon baya ya juya yaga Bobby ya san shi take jin tsoro bai ce komai ba yaja motar. kuka take cigaba da yi tana goge idanun ta har lokacin jikin ta bai daina rawa ba shi kuma bai ce mata ci kan ki ba tuk'i yi a nutse. Kukan ya dame shi har tsakiyar kansa yake jin kuka amma bai san me zaice mata ba shiyasa yayi shiru ya jure abinda yake ji ya cigaba da tafiya.
Ba tare da tayi zato ba taji sun tsaya tana d'ago kai ta gan su a k'ofar gidan su d'an hasken kwan solar da ya haske wajan gidan nasu duk da babu wani haske sosai amma dai yafi babu ya haska wajan, kallon sa tayi ta kalli gidan nasu ta tabbatar fa nan ne mamaki da tsoro suka yi mata yawa tunanin ta a ina ya san gidan su?.
"Kina da Yaya?." A sama taji maganar tasa ta juyo ta kalle shi sai taga kamar ba shine yayi maganar ba dan bama ita yake kallo ba. Idanu ta goge ta girgiza kai alamun a'a kafin tace, "Bani dashi."
"Mahaifi?" Ya sake fad'a bai kalle ta ba har lokacin.
"Ina dashi" ta bashi amsa muryar ta na rawa sosai.
Sai da ya kusa kwashe sakan hamsin sannan yace, "kice ana sallama dashi" ya fad'a yana danna lock d'in motar ta bada sautin k'ut alamun ta bud'e. "Na gode. kayi hak'uri da abinda na fad'a maka a baya ban san kai bane ba, ka bawa d'an uwan ka hak'uri ya fita a rayuwata nasan nayi kuskure duk da laifin sane amma na karb'i laifin." ta fad'a murya na rawa sosai.
Yadda maganar take rawa shine ya jawo hankalin sa ya kalle ta yaga yadda hawaye suke ambaliya daga idanun sa sai yaji rauni ya sake mamaye ko ina na jikin sa zuciyar sa na harbawa da sauri-sauri wani abu nayi masa yawo tun daga yatsan sa har cikin kansa.
"Allah ya saka maka da alkhairi ya biya maka dukkan buk'atun ka na duniya, na gode ka taimake ni Allah ya taimake ka kai ma" ta sake fad'a tana bud'e motar ta saka sandar ta sannan ta sauka ta d'auki d'ayar ta kulle motar ta nufi cikin gidan su. Da kallo ya bita yana kallo ta cikin wani abu mai kama da kewa a zuciyar sa da shauki wanda bai tab'a jin makamancin sa ba a kan kowa sai ita kawai, duk takun da zatayi sai zuciyar sa ta buga hakan ya saka shi dafe zuciyar sa yaji tana harbawa a guje kamar zata faso k'irjin sa ta fito.
Gidan yaga ta shiga ya sauke numfashi yana k'arewa gidan kallo tausayin ta na sake ninka na baya a zuciyar sa.
A can gidan kuwa ana ganin shigar ta Umma ta mik'e tana fad'in, "Alhamdulillah! Malam gata ta dawo" ta fad'a tana nufo Rauda da idanun ta suke cike da kwallah har lokacin. Rik'e ta tayi tana kallon fuskar ta tace, "Rauda ina kika tsaya? Meya faru kike kuka?." Tare suke tafiya har suka k'arasa kan kujerar da take zama ta zauna Umma ta kalli Khairi tace, "Kawo mata ruwa."
Da sauri ta tashi ta kawo ruwa a kofi Umma ta bata tasha ta sauke numfashi hannun ta dafe da kanta da yake mata ciwo.
Baba yace, "Sannu Rauda, daga ina kike Shamsiyya ta sanar dani tun la'asar kika baro gidan ta gashi har anyi i'sha yanzu?." Numfashi take yi kafin tace, "Baba ana sallama da kai a waje." Baba yace, "Waye yake sallamar?."
"Wanda ya taimake ni" ta fad'a tana haki jin hakan ya saka Baba fita bai kuma cewa komai ba.
"Ummulkhairi kawo mata abinci taci" Umma ta fad'a tana kallon Khairi. Mik'ewa Khairi tayi ta d'auko mata abinci ta kawo mata ta karb'a ta bud'e dan taga meye a ciki, shinkafa ce da miya ta sauke numfashi tunda Anas ya aiko musu da abinci suke ci suke sha a gidan shiyasa take bashi babban matsayi a zuciyar ta.
Kad'an ta fara cin abincin duk jikin ta babu dad'i haka ta fara ci gaban ta sai fad'uwa yake ba tare da tasan dalilin faruwar hakan ba.
Shigowar Baba da sallama ya saka suka amsa har ya k'araso ya zauna ya kalle su dukkan su har da Inna da Rahma yace, "Yayan wanda ya kad'e Rauda ne. abin mamakin y'ay'an sarkin katagum ne." A tare k'irjin su ya buga har da ita Rauda d'in dan bata san waye ya buge ta ba daman. Umma tace, "ko da naji, yadda yaron da ya buge ta yake da izza kana kallon sa kasan jinin sarauta ne."
Baba yace, "tunda ya buge ta ranar da ya dawo da safe ya kwanta ciwo har yanzu bai farfad'o ba yana kwance, shi wannan d'in yayan sane duk da kamar ana masa dole in yana magana har wani yatsine fuska yake yi yace min yana so a madadin k'anin sa zai saka ayi mata aikin k'afar ta a waccan k'asar ta larabawa meye ma sunan ta...." ya fad'a yana yin shiru alamun tunani.
"Yauwa Misra, gobe zai aiko a d'auke ta a kai ta can ofishin da ake yin fasko na tafiya ayi mata cikin satin nan yake so ayi mata aikin. Yace kuma na baku hak'uri bai san da mara lafiyar da wuri ba da tuni anyi mata magani." Umma da take sauraren sa ta sauke numfashi tace, "Shi ya akayi yanzu ya san da ita?." Baba ya kalle ta yace, "Ai bazai miki k'arya ba."
"nidai Malam ina jin tsoro aikin baza'a yi a k'asar nan ba har sai anje Misra? Kuma haka zamu bada ita daga shi sai ita aje ayi mata aiki muna nan baki sake?."
*KWANTAN ƁAUNA*
©️ *Nana Haleema.*
*Book 1*
*018.*
Cizo ya kawo mata karen shine ya saka ta yin k'ara ta kulle idanun ta tana jiran taji sukar hakoran sa a a naman ta amma sai taji shiru, ta bud'e idanun ta a hankali taga karen baya gaban ta kamar d'azu ta juya gefen ta ta ganshi a tsaye ya juyo yana kallon ta kusa da wanda bata tantance waye ba. A hankali yake takowa yazo kusa da ita suka had'a ido sai jikin ta ya cigaba da tsuma ya had'e hannayen ta waje guda tana kuka amma ta kasa magana.
D'auke kai yayi daga kanta ya kalli wad'anda suka sato ta sai suka zube a k'asa cikin girmamawa hannun su na jinjina d'aya yace, "Tuba muke ranka ya dad'e, zamu aikata abinda ka umarce mu yanzu, ka yafe mana zamu yi."
"Aliyu ya saka ku kawo ta nan?" Ya fad'a a tausashe cikin muryar sa mara hayaniya wacce bata fita sosai yana kallon su.
Sai a sannan suka gane bafa Aliyu ne a gaban su ba babar giwa ce da kanta sai jikin su ya k'ara kaimi wajan tsuma d'aya yace, "Kayi mana aikin gafara ranka ya dad'e. Yarima Aliyu ne ya umarce mu da mu kawo ta nan mu sakar mata Bobby ya cize ta sannan muyi abinda muke so da ita. Mun tuba wallahi baza mu sake aikata hakan ba." Kai Asad yake girgizawa kaf yasan plan d'in nasu sune da Aliyun basu san ya sani bane amma tunda yasa a fara tracking d'inta yasan da haka.
Kallon da yayi musu ya saka jiki su rawa suka fara fad'in, "Kiyi hak'uri yarinya muma ba san ran mu bane ba wallahi saka mu akayi babu yadda zamu yi, kiyi hak'uri ki yafe mu." Kanzil Rauda bata ce ba sai kuka da take mai tsuma zuciya ya sake kallon su duk sai suka sake diriricewa dan basu fahimcin kallon na meye ba.
D'aya ne ya mik'e da sauri ya kawo mata sandinan ta guda biyu yace, "kiyi hak'uri." Da hannu yayi musu alamun da su wuce su tafi a da sauri suka hau mota suka ja da gudu. Dawo da kallon sa yayi kanta yadda jikin ta yake tsuma tana kuka hakan ya tabbatar masa da ba k'aramin tsoro take ji ba sai ta sake bashi tausayi yana so yayi mata magana amma bai san me zaice ba.
Yana tsaye tana kuka sai da ta gaji dan kanta sannan ta fara k'ok'arin tashi tsaye, bata iya tsayuwa da k'afafun ta hakan ya saka tashi yake gagarar ta ganin sai juyi take kamar wancan lokacin ya saka shi mik'ar da ita tsaye ya bata sandar ta rik'e sai kuma ta dafe kai da hannayen ta guda biyu jin yadda yake sarawa. Bata daina kuka bai kuma ce komai ya juya wajan motar sa ya shiga karen shiga mazaunin baya ya dawo da motar daidai kusa da ita amma har lokacin bai ce k'ala ba.
Wajan take kallo babu alamun abin hawa in tak'i shiga motar ta cuci kanta dan bata san a inda take ba balle tabi hanyar da zata sami mota, tana so ta shiga amma rashin yi mata magana da baiyi ba ya saka take shakka kar ta shiga ya wulaqanta ta.
Sauke glass d'in gefen ta yayi da hannu yayi mata alama da ta shiga a sanyaye ta ja handle d'in motar ya bud'e, so take ta fara saka sanda guda d'aya sannan ta shiga sai ta shigo da d'ayar amma ta kasa ta rasa yadda zatayi. Babu tsammani taga ya fito daga motar ya dawo inda take ya karb'o guda d'aya ya saka a ciki ta saka k'afar ta mai lafiyar ta shiga cikin motar, saka mata d'aya sandar yayi kana ya kulle k'ofar ya zaga ya shiga.
Ganin ta yayi duk a tsorace tana kallon baya ya juya yaga Bobby ya san shi take jin tsoro bai ce komai ba yaja motar. kuka take cigaba da yi tana goge idanun ta har lokacin jikin ta bai daina rawa ba shi kuma bai ce mata ci kan ki ba tuk'i yi a nutse. Kukan ya dame shi har tsakiyar kansa yake jin kuka amma bai san me zaice mata ba shiyasa yayi shiru ya jure abinda yake ji ya cigaba da tafiya.
Ba tare da tayi zato ba taji sun tsaya tana d'ago kai ta gan su a k'ofar gidan su d'an hasken kwan solar da ya haske wajan gidan nasu duk da babu wani haske sosai amma dai yafi babu ya haska wajan, kallon sa tayi ta kalli gidan nasu ta tabbatar fa nan ne mamaki da tsoro suka yi mata yawa tunanin ta a ina ya san gidan su?.
"Kina da Yaya?." A sama taji maganar tasa ta juyo ta kalle shi sai taga kamar ba shine yayi maganar ba dan bama ita yake kallo ba. Idanu ta goge ta girgiza kai alamun a'a kafin tace, "Bani dashi."
"Mahaifi?" Ya sake fad'a bai kalle ta ba har lokacin.
"Ina dashi" ta bashi amsa muryar ta na rawa sosai.
Sai da ya kusa kwashe sakan hamsin sannan yace, "kice ana sallama dashi" ya fad'a yana danna lock d'in motar ta bada sautin k'ut alamun ta bud'e. "Na gode. kayi hak'uri da abinda na fad'a maka a baya ban san kai bane ba, ka bawa d'an uwan ka hak'uri ya fita a rayuwata nasan nayi kuskure duk da laifin sane amma na karb'i laifin." ta fad'a murya na rawa sosai.
Yadda maganar take rawa shine ya jawo hankalin sa ya kalle ta yaga yadda hawaye suke ambaliya daga idanun sa sai yaji rauni ya sake mamaye ko ina na jikin sa zuciyar sa na harbawa da sauri-sauri wani abu nayi masa yawo tun daga yatsan sa har cikin kansa.
"Allah ya saka maka da alkhairi ya biya maka dukkan buk'atun ka na duniya, na gode ka taimake ni Allah ya taimake ka kai ma" ta sake fad'a tana bud'e motar ta saka sandar ta sannan ta sauka ta d'auki d'ayar ta kulle motar ta nufi cikin gidan su. Da kallo ya bita yana kallo ta cikin wani abu mai kama da kewa a zuciyar sa da shauki wanda bai tab'a jin makamancin sa ba a kan kowa sai ita kawai, duk takun da zatayi sai zuciyar sa ta buga hakan ya saka shi dafe zuciyar sa yaji tana harbawa a guje kamar zata faso k'irjin sa ta fito.
Gidan yaga ta shiga ya sauke numfashi yana k'arewa gidan kallo tausayin ta na sake ninka na baya a zuciyar sa.
A can gidan kuwa ana ganin shigar ta Umma ta mik'e tana fad'in, "Alhamdulillah! Malam gata ta dawo" ta fad'a tana nufo Rauda da idanun ta suke cike da kwallah har lokacin. Rik'e ta tayi tana kallon fuskar ta tace, "Rauda ina kika tsaya? Meya faru kike kuka?." Tare suke tafiya har suka k'arasa kan kujerar da take zama ta zauna Umma ta kalli Khairi tace, "Kawo mata ruwa."
Da sauri ta tashi ta kawo ruwa a kofi Umma ta bata tasha ta sauke numfashi hannun ta dafe da kanta da yake mata ciwo.
Baba yace, "Sannu Rauda, daga ina kike Shamsiyya ta sanar dani tun la'asar kika baro gidan ta gashi har anyi i'sha yanzu?." Numfashi take yi kafin tace, "Baba ana sallama da kai a waje." Baba yace, "Waye yake sallamar?."
"Wanda ya taimake ni" ta fad'a tana haki jin hakan ya saka Baba fita bai kuma cewa komai ba.
"Ummulkhairi kawo mata abinci taci" Umma ta fad'a tana kallon Khairi. Mik'ewa Khairi tayi ta d'auko mata abinci ta kawo mata ta karb'a ta bud'e dan taga meye a ciki, shinkafa ce da miya ta sauke numfashi tunda Anas ya aiko musu da abinci suke ci suke sha a gidan shiyasa take bashi babban matsayi a zuciyar ta.
Kad'an ta fara cin abincin duk jikin ta babu dad'i haka ta fara ci gaban ta sai fad'uwa yake ba tare da tasan dalilin faruwar hakan ba.
Shigowar Baba da sallama ya saka suka amsa har ya k'araso ya zauna ya kalle su dukkan su har da Inna da Rahma yace, "Yayan wanda ya kad'e Rauda ne. abin mamakin y'ay'an sarkin katagum ne." A tare k'irjin su ya buga har da ita Rauda d'in dan bata san waye ya buge ta ba daman. Umma tace, "ko da naji, yadda yaron da ya buge ta yake da izza kana kallon sa kasan jinin sarauta ne."
Baba yace, "tunda ya buge ta ranar da ya dawo da safe ya kwanta ciwo har yanzu bai farfad'o ba yana kwance, shi wannan d'in yayan sane duk da kamar ana masa dole in yana magana har wani yatsine fuska yake yi yace min yana so a madadin k'anin sa zai saka ayi mata aikin k'afar ta a waccan k'asar ta larabawa meye ma sunan ta...." ya fad'a yana yin shiru alamun tunani.
"Yauwa Misra, gobe zai aiko a d'auke ta a kai ta can ofishin da ake yin fasko na tafiya ayi mata cikin satin nan yake so ayi mata aikin. Yace kuma na baku hak'uri bai san da mara lafiyar da wuri ba da tuni anyi mata magani." Umma da take sauraren sa ta sauke numfashi tace, "Shi ya akayi yanzu ya san da ita?." Baba ya kalle ta yace, "Ai bazai miki k'arya ba."
"nidai Malam ina jin tsoro aikin baza'a yi a k'asar nan ba har sai anje Misra? Kuma haka zamu bada ita daga shi sai ita aje ayi mata aiki muna nan baki sake?."