Sashe 45
Kwantan Bauna Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Wannan ba komai bane ba Sadiya na fara maganin yarinyar shi ba wani abin damuwa bane in nace bana so zance ya k'are; ita yarinyar ita nake so na jawa kunne ko dan tasan wutsiyar rak'umi tayi nesa da k'asa. Ina so tasan ruwa fa ba sa'an kwando bane, ta banbance tsakanin zare da abawa." ta girgiza kai cikin gamsuwa tace, "Haka ne, yana da kyau mu tauna tsakuwa dan aya taji tsoro. Amma wanne mataki kika d'auka a zuciyar ki wanda kike gani zamu aiwatar dashi?."
Mama ta kalle ta tace, "Shiyasa na kira ki domin inaso ko meye a aiwatar dashi yau bana son b'ata lokaci." Mum tayi jim tana tunani kafin tace, "Mu saka a d'auko ta a sace ta mu bata wahala sosai a sake b'alla k'afar ta ta kinga in aka mata haka zata shiga hankalin ta." Mama ta girgiza kai tace, "Shawara ce mai kyau wannan amma bazata yu ba, in labarin ya bayyana daga baya sunan mai martaba zai b'aci a garin nan za'a dinga yawo dashi ace nice na aikata hakan. Canja wata."
Mum tace, "Haka ne. Mu tura mutane su je gidan ayi mata dukan tsiya ita da iyayen ta inda dama a b'alla ta a b'alla iyayen ta a kuma yi musu kyakykyawan warning wanda zai shiga jikin su, kin ga zasu ji tsoro dukkan su bama ita kad'ai ba har da iyayen ta."
Mama tayi murmushi cikin jin dad'in maganar tace, "Wannan shawarar tayi d'ari bisa dari da kuma ita zamuyi amfani; amma fa bana son aje da wani dogari daga gidan nan dan tonuwar wannan maganar ma b'ata suna ne a idanun mutanen gidan nan balle mutanen gari, k'askanci ne a wajena ace yaron dana fi so cikin y'ay'ana yana bibiyar wata y'ar talakawa. Inaso aje dake domin kiyi musu kyakykyawan warning wanda zasu shiga hankalin su." Mum tace, "Wannan ki d'auka an gama ranki ya dad'e, zan samu mutane a waje muje muyi duk abinda kika ce ai abu ne mai sauk'i."
Mama ta girgiza kai tace, "kuje a fara aiwatar da komai yanzu bana son b'ata lokaci Sadiya ke kin sani." Ba musu Mum ta mik'e tace, "An gama ranki ya dad'e" tana gama fad'ar hakan ta fita daga gidan da sauri.
Mum na fita gida ta koma Jidda bata nan gidan babu kowa jikin ta har rawa yake dan tama fi Mama son d'aukar mataki a kan Rauda ta d'auki abinda zata d'auka ta fita daga gidan da sauri. Mata da maza ta had'a duka ta biya su aka tafi gidan su Rauda lokacin rana ta bud'e sosai.
Rauda na zaune akan kujerar da ta saba zama ita da Umma da Inna bata nan sauran sun tafi makaranta, Baba ne ya fito daga d'aki bai fita da wuri ba Umma tace, "Malam kaji ashe duk abinda aka kawo gidan nan ba Anas ne ya bayar ba?." Baba ya kalle su yace, "kamar yaya kenan?."
"Jiya take yiwa Anas mganar magani yake cewa shi duk abinda aka kawo bashi ya bayar ba, hankalina duk ya tashi ban san abin wanda muke ci ba wallahi, da alhairi yake neman mu ko akasin sa duk bamu sani ba." Baba yace, "Bashi bane ba? Kuma Rauda ba wasa yake miki ba kuwa?."
Rauda tace, "Ya rantse min da Allah akan bashi bane ba." Baba cikin mamaki yace, "To amma dashi muka yi maganar ta kawai, da shi muka yi maganar keke napep d'in nan ya akayi wani daban yasan da ita?." Umma tace, "abinda ya d'aure min kai nima kenan." Shiru Baba yayi sai shiru can kuma yace, "Koma dai waye tunda ba sata nayi ba ai shikenan, ban kuma rok'i mutum ba Allah ne ya kawo min tsuntsu daga sama a gashe akan me zan ki ci ni kuwa?."
Umma tace, "Amma malam ya kamata a bincika." Baba yace, "Na bincika ina? Nida ke da kowa bamu sanshi ba ina zanje na bincika nace ga wanda nake nema nida ban sanshi ba?; kar ki d'aga min hankali ina zaune lafiya dan Allah."
"Assalamu Alaikum!" Aka fad'a daga soron gidan aka wuce Baba suka shigo cikin gidan mata uku maza biyu sai Mum ta hud'u. Baba da yake kallon ikon Allah ganin maza garada sun shige shi sun shiga tsakar gidan sa kai tsaye babu izinin sa ya k'araso yana kallon su yace, "Malamai lafiya kuka shigo min gida kai tsaye haka?."
Mum ta k'are masa kallo ta kalle gidan tace, "Au wai wannan gida ne?, ni na d'auka wani kango wanda y'an zaman banza suke zama suna shaye-shaye da yiwa yara fyad'e muka shigo, wai ashe gida" ta fad'a tana kallon wanda suka shigo sai suka fashe da dariya har da tafawa. Rauda ta kalle su tace, "Malamai lafiya zaku shigowa mutane gida kai tsaye?." Jin yadda tayi maganar cikin tsiwa ya saka Mum kallon ta tace, "Oh kece gurguwar kenan, astagafirullah" ta fad'a tana dariya kafin tace, "Yadda aka kwatanta min munin ki ma ashe kin wuce wajan, wannan sai kace ragowar y'an wuta; wanne bak'in zunubi kuka aikata kuka haifo wannan?" Mum ta fad'a tana kallon Baba tana nuna Rauda.
Rahma ta mik'e tace, "Dallah malamai me ya kawo ku gidan mu har kuke fad'a mana maganar banza?." Mum tace, "Koma gefe keda uwar ki y'an kallo ne. wajan ita da uwarta da uban ta muka zo ba ku ba, so ki tsaya kiyi kallo in kina da waya ki d'auko ki fara d'aukar video."
"Wacece ke da zaki zo kina fad'a mana maganar banza da wofi?" Umma ta fad'a tana mik'ewa tsaye. Baba yace, "Malama lafiya me ya kawo ku gidan nan?." Ta juya ta kalli Baba tace, "Jan kunne nazo nayi muku gabad'ayan ku akan gangancin da kuke neman aikatawa, ina so ku jawa y'ar ku kunne ta fita hanyar wanda take cikin hanyar sa, babu shi babu ita domin shi d'in ba sa'an ta bane tazarar su kamar tazarar sama da k'asa ne. Yafi k'arfin ta ya kuma fi k'arfin dangin ku gabad'aya."
Baba da gaban sa ya fad'i nan take Anas yazo ransa amma baice komai ba sai yace, "Akan wa kuke magana?." Mum ta gyara tsayuwa ta tofar da yawu tace, "Wannan gidan ai sai ka d'auki ciwo, bari kuga" ta fad'a tana d'auko facemask a jaka ta saka sannan tace, "Ina magana ne akan ASAD! Wanda kuka kamowa kurwa kuka asirice shi baya ganin kowa sai waccan bak'ar annobar, kaja mata kunne zata d'auko ruwan dafa kanta matuk'ar bata fita hanyar sa ba zatayi dana sanin da bata tab'a yin irin sa ba har abada."
Rauda dake zaune cikin fusata tace, "Waye Asad? Meye shi suna ne ko gari?, mutum ne ko aljani?" Ta fad'a cikin masifa tana kallon Mum da ba ita take kallo ba. Mum ta juyo ta kalle ta tace, "kin sanshi ai basai na fad'a miki ba, tunda har kuka iya bin bokaye kuke so ku kamo zuciyar sa ai kinfi kowa sanin sa. ke banda tsaurin ido ma da kwad'ayi irin na jikar talakawa ina ke ina Asad?, kalle ki fa kamar wacce aka d'auko daga cikin bak'in gawayi, tsabar bak'in da yake fuskar ki sai a d'auka jikar shaid'an ce ke, kalli k'afar ki abinda ya rage miki hawa kan titi ki fara bara amma ki fara tunanin Asad dan talauci ya toshe miki kwakwalwar ki."
"Kece dak'ik'iya mara hankali wacce bata san darajar d'an adam ba babu girma sai na jiki, shi wanda kike magana a kai bansan da zaman sa bama balle na d'aga idanuna na kalle shi, dan haka kija bak'ak'en k'afafun ki a fitar mana daga gida" ta fad'a cikin rashin kunya tana mata ihu. Mum ta girgiza kai tace, "lallai yarinya zan nuna miki ni ba sa'ar yin ki bace, ga sa'a ta nan" ta fad'a tana tsinkawa Umma dake tsaye mari ba zato babu tsammani. Baba ya yunk'uro zai zo wajan mazan suka rike shi gam ta juya yana kallon sa ransa a b'ace yace, "Ke wacce irin mahaukaciya ce shashasha? Ya zaki shigo har cikin gidana ki saka hannu ki daki matata?."
"Dan na nunawa y'ar ka itace abokiyar yina ba ita ba, kuma....." saukar marin da taji a tata fuskar ya hana ta k'arasawa ta juyo a razane taga Rauda a tsaye da sandinan ta tana wuci cikin b'acin rai Mum na juyowa a fusace Rauda ta sake bata wani sabon marin da batayi tsammani ba. Cikin fusata da rashin kunya da yatsa ta nuna ta tace, "A kaf duniya babu wanda ya isa ya tab'a min iyayena k'yale shi ciki kuwa har dake, in zafin kai kike ji dashi na fiki, in rashin kunya ce itama na fiki, in iskanci ne shima na fiki, duk abinda kike ji dashi a tafin hannuna kike na dame ki na shanye. Na rantse da Allah kika sake dukar min uwa ko kika sake tab'a min uba sai na sake marin ki sai naga abinda zaki min. Banza babbar banza mara hankali mai tunanin jakuna" ta fad'a tana hararar ta cikin b'acin ran da ya bayyana k'arara a ka fuskar ta.
Mum da take kallon ta hannun ta dafe da kuncin ta kasa cewa komai tayi sai jikinta da yake rawa sosai alamun b'acin rai tsanar ta na shiga ko wanne sak'o da lungu na jikinta, tunda take ba'a tab'a tozarta ta kamar yadda akayi mata yau, yarinya k'arama ta fad'a mata wannan magana mai zafi har ta mare ta..?. Hannu ta saka da k'arfi ta tankad'e Rauda ta janye duka sandinan ta kalli matan tace, "Me kuka jira ne ku fara aiwatar da abinda ya kawo mu ku nuna musu mu ba sa'anin su bace" ta fad'a tana marin Rauda da k'arfin gaske. Nan da nan suka shiga dukan Umma da Rauda kamar Allah ya aiko su Inna da ta shigo lokacin ita da Rahma suka zo ceto aka had'a dasu ana duka Baba yana hannu an rik'e shi ya kasa komai.
Mama ta kalle ta tace, "Shiyasa na kira ki domin inaso ko meye a aiwatar dashi yau bana son b'ata lokaci." Mum tayi jim tana tunani kafin tace, "Mu saka a d'auko ta a sace ta mu bata wahala sosai a sake b'alla k'afar ta ta kinga in aka mata haka zata shiga hankalin ta." Mama ta girgiza kai tace, "Shawara ce mai kyau wannan amma bazata yu ba, in labarin ya bayyana daga baya sunan mai martaba zai b'aci a garin nan za'a dinga yawo dashi ace nice na aikata hakan. Canja wata."
Mum tace, "Haka ne. Mu tura mutane su je gidan ayi mata dukan tsiya ita da iyayen ta inda dama a b'alla ta a b'alla iyayen ta a kuma yi musu kyakykyawan warning wanda zai shiga jikin su, kin ga zasu ji tsoro dukkan su bama ita kad'ai ba har da iyayen ta."
Mama tayi murmushi cikin jin dad'in maganar tace, "Wannan shawarar tayi d'ari bisa dari da kuma ita zamuyi amfani; amma fa bana son aje da wani dogari daga gidan nan dan tonuwar wannan maganar ma b'ata suna ne a idanun mutanen gidan nan balle mutanen gari, k'askanci ne a wajena ace yaron dana fi so cikin y'ay'ana yana bibiyar wata y'ar talakawa. Inaso aje dake domin kiyi musu kyakykyawan warning wanda zasu shiga hankalin su." Mum tace, "Wannan ki d'auka an gama ranki ya dad'e, zan samu mutane a waje muje muyi duk abinda kika ce ai abu ne mai sauk'i."
Mama ta girgiza kai tace, "kuje a fara aiwatar da komai yanzu bana son b'ata lokaci Sadiya ke kin sani." Ba musu Mum ta mik'e tace, "An gama ranki ya dad'e" tana gama fad'ar hakan ta fita daga gidan da sauri.
Mum na fita gida ta koma Jidda bata nan gidan babu kowa jikin ta har rawa yake dan tama fi Mama son d'aukar mataki a kan Rauda ta d'auki abinda zata d'auka ta fita daga gidan da sauri. Mata da maza ta had'a duka ta biya su aka tafi gidan su Rauda lokacin rana ta bud'e sosai.
Rauda na zaune akan kujerar da ta saba zama ita da Umma da Inna bata nan sauran sun tafi makaranta, Baba ne ya fito daga d'aki bai fita da wuri ba Umma tace, "Malam kaji ashe duk abinda aka kawo gidan nan ba Anas ne ya bayar ba?." Baba ya kalle su yace, "kamar yaya kenan?."
"Jiya take yiwa Anas mganar magani yake cewa shi duk abinda aka kawo bashi ya bayar ba, hankalina duk ya tashi ban san abin wanda muke ci ba wallahi, da alhairi yake neman mu ko akasin sa duk bamu sani ba." Baba yace, "Bashi bane ba? Kuma Rauda ba wasa yake miki ba kuwa?."
Rauda tace, "Ya rantse min da Allah akan bashi bane ba." Baba cikin mamaki yace, "To amma dashi muka yi maganar ta kawai, da shi muka yi maganar keke napep d'in nan ya akayi wani daban yasan da ita?." Umma tace, "abinda ya d'aure min kai nima kenan." Shiru Baba yayi sai shiru can kuma yace, "Koma dai waye tunda ba sata nayi ba ai shikenan, ban kuma rok'i mutum ba Allah ne ya kawo min tsuntsu daga sama a gashe akan me zan ki ci ni kuwa?."
Umma tace, "Amma malam ya kamata a bincika." Baba yace, "Na bincika ina? Nida ke da kowa bamu sanshi ba ina zanje na bincika nace ga wanda nake nema nida ban sanshi ba?; kar ki d'aga min hankali ina zaune lafiya dan Allah."
"Assalamu Alaikum!" Aka fad'a daga soron gidan aka wuce Baba suka shigo cikin gidan mata uku maza biyu sai Mum ta hud'u. Baba da yake kallon ikon Allah ganin maza garada sun shige shi sun shiga tsakar gidan sa kai tsaye babu izinin sa ya k'araso yana kallon su yace, "Malamai lafiya kuka shigo min gida kai tsaye haka?."
Mum ta k'are masa kallo ta kalle gidan tace, "Au wai wannan gida ne?, ni na d'auka wani kango wanda y'an zaman banza suke zama suna shaye-shaye da yiwa yara fyad'e muka shigo, wai ashe gida" ta fad'a tana kallon wanda suka shigo sai suka fashe da dariya har da tafawa. Rauda ta kalle su tace, "Malamai lafiya zaku shigowa mutane gida kai tsaye?." Jin yadda tayi maganar cikin tsiwa ya saka Mum kallon ta tace, "Oh kece gurguwar kenan, astagafirullah" ta fad'a tana dariya kafin tace, "Yadda aka kwatanta min munin ki ma ashe kin wuce wajan, wannan sai kace ragowar y'an wuta; wanne bak'in zunubi kuka aikata kuka haifo wannan?" Mum ta fad'a tana kallon Baba tana nuna Rauda.
Rahma ta mik'e tace, "Dallah malamai me ya kawo ku gidan mu har kuke fad'a mana maganar banza?." Mum tace, "Koma gefe keda uwar ki y'an kallo ne. wajan ita da uwarta da uban ta muka zo ba ku ba, so ki tsaya kiyi kallo in kina da waya ki d'auko ki fara d'aukar video."
"Wacece ke da zaki zo kina fad'a mana maganar banza da wofi?" Umma ta fad'a tana mik'ewa tsaye. Baba yace, "Malama lafiya me ya kawo ku gidan nan?." Ta juya ta kalli Baba tace, "Jan kunne nazo nayi muku gabad'ayan ku akan gangancin da kuke neman aikatawa, ina so ku jawa y'ar ku kunne ta fita hanyar wanda take cikin hanyar sa, babu shi babu ita domin shi d'in ba sa'an ta bane tazarar su kamar tazarar sama da k'asa ne. Yafi k'arfin ta ya kuma fi k'arfin dangin ku gabad'aya."
Baba da gaban sa ya fad'i nan take Anas yazo ransa amma baice komai ba sai yace, "Akan wa kuke magana?." Mum ta gyara tsayuwa ta tofar da yawu tace, "Wannan gidan ai sai ka d'auki ciwo, bari kuga" ta fad'a tana d'auko facemask a jaka ta saka sannan tace, "Ina magana ne akan ASAD! Wanda kuka kamowa kurwa kuka asirice shi baya ganin kowa sai waccan bak'ar annobar, kaja mata kunne zata d'auko ruwan dafa kanta matuk'ar bata fita hanyar sa ba zatayi dana sanin da bata tab'a yin irin sa ba har abada."
Rauda dake zaune cikin fusata tace, "Waye Asad? Meye shi suna ne ko gari?, mutum ne ko aljani?" Ta fad'a cikin masifa tana kallon Mum da ba ita take kallo ba. Mum ta juyo ta kalle ta tace, "kin sanshi ai basai na fad'a miki ba, tunda har kuka iya bin bokaye kuke so ku kamo zuciyar sa ai kinfi kowa sanin sa. ke banda tsaurin ido ma da kwad'ayi irin na jikar talakawa ina ke ina Asad?, kalle ki fa kamar wacce aka d'auko daga cikin bak'in gawayi, tsabar bak'in da yake fuskar ki sai a d'auka jikar shaid'an ce ke, kalli k'afar ki abinda ya rage miki hawa kan titi ki fara bara amma ki fara tunanin Asad dan talauci ya toshe miki kwakwalwar ki."
"Kece dak'ik'iya mara hankali wacce bata san darajar d'an adam ba babu girma sai na jiki, shi wanda kike magana a kai bansan da zaman sa bama balle na d'aga idanuna na kalle shi, dan haka kija bak'ak'en k'afafun ki a fitar mana daga gida" ta fad'a cikin rashin kunya tana mata ihu. Mum ta girgiza kai tace, "lallai yarinya zan nuna miki ni ba sa'ar yin ki bace, ga sa'a ta nan" ta fad'a tana tsinkawa Umma dake tsaye mari ba zato babu tsammani. Baba ya yunk'uro zai zo wajan mazan suka rike shi gam ta juya yana kallon sa ransa a b'ace yace, "Ke wacce irin mahaukaciya ce shashasha? Ya zaki shigo har cikin gidana ki saka hannu ki daki matata?."
"Dan na nunawa y'ar ka itace abokiyar yina ba ita ba, kuma....." saukar marin da taji a tata fuskar ya hana ta k'arasawa ta juyo a razane taga Rauda a tsaye da sandinan ta tana wuci cikin b'acin rai Mum na juyowa a fusace Rauda ta sake bata wani sabon marin da batayi tsammani ba. Cikin fusata da rashin kunya da yatsa ta nuna ta tace, "A kaf duniya babu wanda ya isa ya tab'a min iyayena k'yale shi ciki kuwa har dake, in zafin kai kike ji dashi na fiki, in rashin kunya ce itama na fiki, in iskanci ne shima na fiki, duk abinda kike ji dashi a tafin hannuna kike na dame ki na shanye. Na rantse da Allah kika sake dukar min uwa ko kika sake tab'a min uba sai na sake marin ki sai naga abinda zaki min. Banza babbar banza mara hankali mai tunanin jakuna" ta fad'a tana hararar ta cikin b'acin ran da ya bayyana k'arara a ka fuskar ta.
Mum da take kallon ta hannun ta dafe da kuncin ta kasa cewa komai tayi sai jikinta da yake rawa sosai alamun b'acin rai tsanar ta na shiga ko wanne sak'o da lungu na jikinta, tunda take ba'a tab'a tozarta ta kamar yadda akayi mata yau, yarinya k'arama ta fad'a mata wannan magana mai zafi har ta mare ta..?. Hannu ta saka da k'arfi ta tankad'e Rauda ta janye duka sandinan ta kalli matan tace, "Me kuka jira ne ku fara aiwatar da abinda ya kawo mu ku nuna musu mu ba sa'anin su bace" ta fad'a tana marin Rauda da k'arfin gaske. Nan da nan suka shiga dukan Umma da Rauda kamar Allah ya aiko su Inna da ta shigo lokacin ita da Rahma suka zo ceto aka had'a dasu ana duka Baba yana hannu an rik'e shi ya kasa komai.