Sashe 43
Kwantan Bauna Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Mai zai hana, bara na sanar dasu shigowar ku" ya fad'a yana komawa ciki da sauri Asad baice komai ba har Baba ya dawo yace su shigo. Yana gaba suna binsa a baya Hydar na k'arewa gidan kallo har suka shiga ciki. suna zaune dukkan su a kan tabarma a tsakar gidan suka shigo da sallama cikin takun nutsuwa da k'asaita, dukkan su manyan kaya suka saka sun karb'i jikin su sosai tunda suka shigo khamshi ya mamaye gidan. S tare suka amsa Rauda da take zaune a akan kujera ta d'ago ido suka had'a ido da Asad nan take gaban ta ya fad'i tayi saurin janye idanun ta.
"Bismillah ku k'araso mana" Baba ya fad'a yana nuna musu wajan zama. Basu musa ba suka zauna suka gaisa da Umma kafin Hydar yace, "Mama ayi hak'uri nayi fama da rashin lafiya ne shiyasa ban kuma waiwayon ta ba, amma in sha Allah komai zai wuce yanzu." Umma tace, "Babu komai lafiya ai tafi gaban wasa, Allah ya k'ara lafiya." Hydar ya amsa da amin kafin ya kalle ta yace, "Ya jikin ki?."
Sai da ta saukar da kanta k'asa kafin tace, "Da sauk'i." Bai kuma cewa komai ba Asad daman tunda aka gaisa bai sake magana ba. Khalil ne ya shigo yana fad'in, "Baba ga Yaya Anas yazo." Baba yace, "To ina zuwa." Hydar yana so ya basu kud'i amma bai fito da komai ba duk sai yaji kunya tana baibaye shi ganin hakan Asad ya d'auko kud'i a aljihun sa ya ajjiye kusa da Umma sannan yace, "ku fara shiri tafiyar ku baza ta wuce nan da sati ba" yana fad'ar hakan ya mik'e sai Hydar ne yayi musu sallama dan yasan Asad ya gama magana suka fita tare da Baba.
A tsaye jikin mota suka ga Anas Baba ya k'arasa gare shi suna tare dasu Asad, har k'asa Anas ya gaida Baba kafin Baba yace, "Ranka ya dad'e wannan shine Anas mai neman auren Rauda, yana ta d'awainiya damu hatta maganin ta shine yake siya duk da lalurar da ta same ta bai saka ya guje ta ba" ya fad'a yana kallon Asad yana fad'a masa fuskar sa a washe da a nutsuwar magana da kamar Asad.
Abinda Asad yake ji a zuciyar sa sabida abinda Baba yace bai tab'a jin irin sa ba tunda Allah ya kawo shi duniya, k'irjin sa har d'agawa yake sabida bala'in tashi hankalin da bai san zai same shi ba a lokacin, bai tab'a jin k'una da rad'ad'in da yake ji ba tunda yazo duniya. Suka yake ji a zuciyar sa in ya tuna kalaman Baba da yake cewa 'mai neman auren Rauda' nan take sai yaji kamar jiri zai d'auke shi ya fad'i k'asa.
Kai kawai ya d'aga sukayi gaba Baba ya biyo bayan su yana godiya Asad ya bashi kud'i bai iya cewa komai ba suka shiga mota suka bar wajan.
Gudu sosai Asad yake yi hakan ya saka Hydar kallon sa dan yasan shi ba ma'abocin gudu bane in kaga yans gudu ransa a b'ace yake ko kuma wani abun na damun sa,shiru Hydar yayi ya fara tariyo abinda ya faru tun daga farkon zuwan su har yazo inda yaga yanayin sa ya canja inda suke magana da Anas kenan dan shidai yasan har suka fito daga gidan su Rauda yanayin sa bai canja ba. Kallon Asad ya kuma yi yana nazarin sa kafin ya girgiza kai baice komai ba shima.
Anas bai ga Rauda ba sai da akayi magriba aka kunna hasken soron sannan ta fito suka gaisa cikin soyayya yake kallon ta kana yace, "Naga wanda suka buge ki Baba yace min y'ay'an Sarkin garin nan, amma sun kyauta gaskiya abubuwan da sukayi ba ko wanne d'an mai mulkin ne zai shi ba; a ganin wasu da banbanci tsakanin su damu." Rauda ta d'aga kai tace, "Sosai ma kuwa sunyi k'ok'ari."
"Yanzu yaushe ce tafiyar taku Egypt d'in?."
"Ban sani ba gaskiya; ya dai ce bazai wuce sati ba."
"Allah ya nuna mana, nima da ni za'ayi tafiyar in sha Allah."
Murmushi kawai tayi kafin yace, "Rauda magana nake so zamuyi dake." Ta kalle shi tace, "Ina jin ka."
"Tsakanin da Allah kina sona ko a'a?." Gabanta yayi mugun fad'uwa ta runtse idanun ta domin bata san me zatace masa ba komai ta fad'a tasan k'arya take, in tace tana son sa tayi k'arya in tace bata son sa nan ma tayi k'arya.
"Kin yi shiru Rauda, ki bani amsa koda zata cutar dani gaskiya kawai nake son ji." Nan ma shiru bata bashi amsa ba yayi murmushi yace, "Na riga da na fahimci amsa ta Rauda, har yanzu baki bani wani matsayi a zuciyar ki ba, bazan sare ba zan cigaba da nemawa kaina gurbi har na samu ko za'a kai shekara goma nan gaba zan jure."
Tausayin sa taji ya kamata ta kalli kanta ta ganta da k'afa guda d'aya gata ita ba kyau ne da ita ba amma namiji mai kyau da kud'i kamar Anas yana sonta duk da abinda ya same ta bai guje ta ba ya nuna shi dai ita yake so sai taji wani iri a zuciyar ta ta sunkuyar da kai a hankali tace, "Nifa ban ce ba." Murmushi yayi yace, "Nima ban ce kin ce ba ai Rauda, na fahimta ne kuma fahimta ta itace gaskiya."
Zatayi magana Ummulkhairi ta fito zata wuce Rauda tace, "Ina zaki je da magariba?."
"Zan je wajan Bala na karb'o miki magani Umma tace ya k'are."
"Koma anjima sai muje tare."
Ba musu ta koma ya kalle ta yace, "Ina ne wajan mai maganin na karb'o miki?." Rauda ta kalle shi tace, "babu nisa bakin titi ne, wajan wanda ka tura aka bawa kud'in maganin nawa fa." Anas yayi jim kana yace, "wanda na tura aka bawa kud'in magani? Yaushe kenan?." Rauda da mamaki ta kalle shi tace, "Wanda ka biya bashin maganin da yake kaina sannan ka siya kace na dinga karb'a har kud'in su k'are....? a ranar ka turo mana da kayan abinci da yawa da kud'i har da alqawarin Baba na keke napep, ka manta kenan?." Anas ya girgiza kai cikin mamaki ya rik'e bakin sa yace, "Rauda bani bane, duk abinda kika lissafa ban san anyi ba gaskiya sai yanzu da kika fad'a. Maganar keke napep d'azu muka magana da wanda zai kawowa Baba amma ban kawo ba tukunna."
Rauda cike da al'ajabi tace, "Wai da gaske kake?." Ya d'aga mata kai yace, "Da gaske nake ban san anyi ba sai yanzu da kike fad'a min, abinda na sani na turo da da kud'i a baki kafin na dawo." Rauda ta sauke numfashi tana girgiza kai cikin tsoro da mamaki tace, "to waye ya aiko da wad'annan abubuwan haka?, duk a tunanin mu kaine shiyasa bamuyi tunanin kowa ba kaine kawai kazo ranmu a lokacin." Anas ya girgiza kai yana tab'e yace, "Damn it! Lallai akwai wani a gefe wanda yake neman shigowa cikin gwamnati na a shirye, tabbas ko waye ya aiko da abinda kika fad'a masoyin ki ne."
Rauda kamar zata zubar da hawaye tace, "to waye?."
"Allah ne ya sanshi Rauda" ya furta a sanyaye yana kallon ta jikin sa ya kuma yin sanyi jin abinda rauni a zuciyar sa. Shiru tayi shima haka tunanin ta waye wannan wanda yasan abinda yake faruwa da ita har yayi mata abinda yayi....? Koma waye tabbas yana bibiyar ta tunda har yasan da abinda Baba yake so yasan yanayin gidan su na rashin abinci yasan kuma da bashi a kanta wajan Bala mai magani, tabbas ya santa ko ya nemi sani a kanta. shi kuma tunanin waye wannan yake k'okarin shigowa rayuwar Raudan sa a b'oye...? Waye wanda yake k'okarin yin kutse a gwamnatin da yake so ya Gina...?, a ina yake? Waye shi?. Babu wanda zai basu amsa haka dukkan su suka rabu jikin kowa babu k'wari kowa da tunanin da yake zuciyar sa.
Asad yana tsaye a jikin window d'akin sa yana kallon mutanen da suke shige da fice a gidan iska na kad'a shi kad'an kasancewar yanayin garin babu iska, ya rasa abinda yake masa dad'i gabad'aya hakan ya saka shi kallon waje ko zai ji dad'i, motsin da yaji a bayan sa hakan ya saka shi ya juyo yaga Hydar ne ya shigo ya k'araso kusa dashi ya tsaya yace, "Deaf akwai abinda yake damun ka tun lokacin da muka baro gidan su yarinyar nan na lura akwai wani abu, meye shi...?."
Numfashi ya sauke baice komai ba ya cigaba da kallon window d'in kafin Hydar ya kuma cewa, "Ka sanar dani abinda yake damun ka ko zan iya maka maganin sa." Asad ya bar jikin Window d'in ya saka hannu a aljihu yace, "Ban san meyasa nake ganin ta ko haushe ba Hydar, even in my dreams I saw her lokaci zuwa lokaci." Jin yadda yayi maganar da rauni ya saka Hydar fuskantar sa yace, "Who is she?." Kallon idanun Hydar yayi kafin ya bar wajan yace, "Forget it."
"Tell me please, bana so na ganka cikin damuwa ka sanar dani."
Asad ya zuba masa ido na wani lokacin kafin ya tsaya jikin mudubi yana kallon kansa yace, "Hydar...." Sai kuma yayi shiru jin hakan ya saka Hydar yace, "Please in baka fad'a min ba wa zaka fad'awa?."
"Ina ganin ta a mafarki Hydar tana taimako na ko yaushe tana bani kariya, after that na ganta a zahiri na tabbatar itace ta cikin mafarkina" sai kuma ya dafe kansa ya sauke numfashi yace, "ban san me nake ji ba but ina jin wani iri." ya fad'a yana dafe kansa ya jingina da bango yana lumshe idanun sa.
"Wacece?." Shiru Asad yayi masa bai amsa ba Hydar ya sake maimaitawa sai daga baya yace, "Rauda!." Hydar gaban sa yayi mugun fad'uwar ya zaro manyan idanun sa waje yace, "What? Rauda!, I think yarinyar da muka je gidan su itace Rauda ba...?, yeah itace, oh my god!" ya fad'a yana dafe kansa yana kallon d'an uwan nasa da mamaki.
"Bismillah ku k'araso mana" Baba ya fad'a yana nuna musu wajan zama. Basu musa ba suka zauna suka gaisa da Umma kafin Hydar yace, "Mama ayi hak'uri nayi fama da rashin lafiya ne shiyasa ban kuma waiwayon ta ba, amma in sha Allah komai zai wuce yanzu." Umma tace, "Babu komai lafiya ai tafi gaban wasa, Allah ya k'ara lafiya." Hydar ya amsa da amin kafin ya kalle ta yace, "Ya jikin ki?."
Sai da ta saukar da kanta k'asa kafin tace, "Da sauk'i." Bai kuma cewa komai ba Asad daman tunda aka gaisa bai sake magana ba. Khalil ne ya shigo yana fad'in, "Baba ga Yaya Anas yazo." Baba yace, "To ina zuwa." Hydar yana so ya basu kud'i amma bai fito da komai ba duk sai yaji kunya tana baibaye shi ganin hakan Asad ya d'auko kud'i a aljihun sa ya ajjiye kusa da Umma sannan yace, "ku fara shiri tafiyar ku baza ta wuce nan da sati ba" yana fad'ar hakan ya mik'e sai Hydar ne yayi musu sallama dan yasan Asad ya gama magana suka fita tare da Baba.
A tsaye jikin mota suka ga Anas Baba ya k'arasa gare shi suna tare dasu Asad, har k'asa Anas ya gaida Baba kafin Baba yace, "Ranka ya dad'e wannan shine Anas mai neman auren Rauda, yana ta d'awainiya damu hatta maganin ta shine yake siya duk da lalurar da ta same ta bai saka ya guje ta ba" ya fad'a yana kallon Asad yana fad'a masa fuskar sa a washe da a nutsuwar magana da kamar Asad.
Abinda Asad yake ji a zuciyar sa sabida abinda Baba yace bai tab'a jin irin sa ba tunda Allah ya kawo shi duniya, k'irjin sa har d'agawa yake sabida bala'in tashi hankalin da bai san zai same shi ba a lokacin, bai tab'a jin k'una da rad'ad'in da yake ji ba tunda yazo duniya. Suka yake ji a zuciyar sa in ya tuna kalaman Baba da yake cewa 'mai neman auren Rauda' nan take sai yaji kamar jiri zai d'auke shi ya fad'i k'asa.
Kai kawai ya d'aga sukayi gaba Baba ya biyo bayan su yana godiya Asad ya bashi kud'i bai iya cewa komai ba suka shiga mota suka bar wajan.
Gudu sosai Asad yake yi hakan ya saka Hydar kallon sa dan yasan shi ba ma'abocin gudu bane in kaga yans gudu ransa a b'ace yake ko kuma wani abun na damun sa,shiru Hydar yayi ya fara tariyo abinda ya faru tun daga farkon zuwan su har yazo inda yaga yanayin sa ya canja inda suke magana da Anas kenan dan shidai yasan har suka fito daga gidan su Rauda yanayin sa bai canja ba. Kallon Asad ya kuma yi yana nazarin sa kafin ya girgiza kai baice komai ba shima.
Anas bai ga Rauda ba sai da akayi magriba aka kunna hasken soron sannan ta fito suka gaisa cikin soyayya yake kallon ta kana yace, "Naga wanda suka buge ki Baba yace min y'ay'an Sarkin garin nan, amma sun kyauta gaskiya abubuwan da sukayi ba ko wanne d'an mai mulkin ne zai shi ba; a ganin wasu da banbanci tsakanin su damu." Rauda ta d'aga kai tace, "Sosai ma kuwa sunyi k'ok'ari."
"Yanzu yaushe ce tafiyar taku Egypt d'in?."
"Ban sani ba gaskiya; ya dai ce bazai wuce sati ba."
"Allah ya nuna mana, nima da ni za'ayi tafiyar in sha Allah."
Murmushi kawai tayi kafin yace, "Rauda magana nake so zamuyi dake." Ta kalle shi tace, "Ina jin ka."
"Tsakanin da Allah kina sona ko a'a?." Gabanta yayi mugun fad'uwa ta runtse idanun ta domin bata san me zatace masa ba komai ta fad'a tasan k'arya take, in tace tana son sa tayi k'arya in tace bata son sa nan ma tayi k'arya.
"Kin yi shiru Rauda, ki bani amsa koda zata cutar dani gaskiya kawai nake son ji." Nan ma shiru bata bashi amsa ba yayi murmushi yace, "Na riga da na fahimci amsa ta Rauda, har yanzu baki bani wani matsayi a zuciyar ki ba, bazan sare ba zan cigaba da nemawa kaina gurbi har na samu ko za'a kai shekara goma nan gaba zan jure."
Tausayin sa taji ya kamata ta kalli kanta ta ganta da k'afa guda d'aya gata ita ba kyau ne da ita ba amma namiji mai kyau da kud'i kamar Anas yana sonta duk da abinda ya same ta bai guje ta ba ya nuna shi dai ita yake so sai taji wani iri a zuciyar ta ta sunkuyar da kai a hankali tace, "Nifa ban ce ba." Murmushi yayi yace, "Nima ban ce kin ce ba ai Rauda, na fahimta ne kuma fahimta ta itace gaskiya."
Zatayi magana Ummulkhairi ta fito zata wuce Rauda tace, "Ina zaki je da magariba?."
"Zan je wajan Bala na karb'o miki magani Umma tace ya k'are."
"Koma anjima sai muje tare."
Ba musu ta koma ya kalle ta yace, "Ina ne wajan mai maganin na karb'o miki?." Rauda ta kalle shi tace, "babu nisa bakin titi ne, wajan wanda ka tura aka bawa kud'in maganin nawa fa." Anas yayi jim kana yace, "wanda na tura aka bawa kud'in magani? Yaushe kenan?." Rauda da mamaki ta kalle shi tace, "Wanda ka biya bashin maganin da yake kaina sannan ka siya kace na dinga karb'a har kud'in su k'are....? a ranar ka turo mana da kayan abinci da yawa da kud'i har da alqawarin Baba na keke napep, ka manta kenan?." Anas ya girgiza kai cikin mamaki ya rik'e bakin sa yace, "Rauda bani bane, duk abinda kika lissafa ban san anyi ba gaskiya sai yanzu da kika fad'a. Maganar keke napep d'azu muka magana da wanda zai kawowa Baba amma ban kawo ba tukunna."
Rauda cike da al'ajabi tace, "Wai da gaske kake?." Ya d'aga mata kai yace, "Da gaske nake ban san anyi ba sai yanzu da kike fad'a min, abinda na sani na turo da da kud'i a baki kafin na dawo." Rauda ta sauke numfashi tana girgiza kai cikin tsoro da mamaki tace, "to waye ya aiko da wad'annan abubuwan haka?, duk a tunanin mu kaine shiyasa bamuyi tunanin kowa ba kaine kawai kazo ranmu a lokacin." Anas ya girgiza kai yana tab'e yace, "Damn it! Lallai akwai wani a gefe wanda yake neman shigowa cikin gwamnati na a shirye, tabbas ko waye ya aiko da abinda kika fad'a masoyin ki ne."
Rauda kamar zata zubar da hawaye tace, "to waye?."
"Allah ne ya sanshi Rauda" ya furta a sanyaye yana kallon ta jikin sa ya kuma yin sanyi jin abinda rauni a zuciyar sa. Shiru tayi shima haka tunanin ta waye wannan wanda yasan abinda yake faruwa da ita har yayi mata abinda yayi....? Koma waye tabbas yana bibiyar ta tunda har yasan da abinda Baba yake so yasan yanayin gidan su na rashin abinci yasan kuma da bashi a kanta wajan Bala mai magani, tabbas ya santa ko ya nemi sani a kanta. shi kuma tunanin waye wannan yake k'okarin shigowa rayuwar Raudan sa a b'oye...? Waye wanda yake k'okarin yin kutse a gwamnatin da yake so ya Gina...?, a ina yake? Waye shi?. Babu wanda zai basu amsa haka dukkan su suka rabu jikin kowa babu k'wari kowa da tunanin da yake zuciyar sa.
Asad yana tsaye a jikin window d'akin sa yana kallon mutanen da suke shige da fice a gidan iska na kad'a shi kad'an kasancewar yanayin garin babu iska, ya rasa abinda yake masa dad'i gabad'aya hakan ya saka shi kallon waje ko zai ji dad'i, motsin da yaji a bayan sa hakan ya saka shi ya juyo yaga Hydar ne ya shigo ya k'araso kusa dashi ya tsaya yace, "Deaf akwai abinda yake damun ka tun lokacin da muka baro gidan su yarinyar nan na lura akwai wani abu, meye shi...?."
Numfashi ya sauke baice komai ba ya cigaba da kallon window d'in kafin Hydar ya kuma cewa, "Ka sanar dani abinda yake damun ka ko zan iya maka maganin sa." Asad ya bar jikin Window d'in ya saka hannu a aljihu yace, "Ban san meyasa nake ganin ta ko haushe ba Hydar, even in my dreams I saw her lokaci zuwa lokaci." Jin yadda yayi maganar da rauni ya saka Hydar fuskantar sa yace, "Who is she?." Kallon idanun Hydar yayi kafin ya bar wajan yace, "Forget it."
"Tell me please, bana so na ganka cikin damuwa ka sanar dani."
Asad ya zuba masa ido na wani lokacin kafin ya tsaya jikin mudubi yana kallon kansa yace, "Hydar...." Sai kuma yayi shiru jin hakan ya saka Hydar yace, "Please in baka fad'a min ba wa zaka fad'awa?."
"Ina ganin ta a mafarki Hydar tana taimako na ko yaushe tana bani kariya, after that na ganta a zahiri na tabbatar itace ta cikin mafarkina" sai kuma ya dafe kansa ya sauke numfashi yace, "ban san me nake ji ba but ina jin wani iri." ya fad'a yana dafe kansa ya jingina da bango yana lumshe idanun sa.
"Wacece?." Shiru Asad yayi masa bai amsa ba Hydar ya sake maimaitawa sai daga baya yace, "Rauda!." Hydar gaban sa yayi mugun fad'uwar ya zaro manyan idanun sa waje yace, "What? Rauda!, I think yarinyar da muka je gidan su itace Rauda ba...?, yeah itace, oh my god!" ya fad'a yana dafe kansa yana kallon d'an uwan nasa da mamaki.