Sashe 4
Kwantan Bauna Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Da kallo yake binta har ta kai k'arshe yace, "to uwar iyayi ita y'ar uwar ki bata yi magana ba sai ke?, yaran nan dai nine na tsuguna na haifi kayana ba wani ya haifar min ba, kema da kike tutuyar y'ar kice nine nayi miki cikin ta ko? To ki saka min matsaya a lamarina da y'ay'ana na amince da tarbiyayyar dana yi musu, in ma bak'in ciki kike dan ina samun arzuki da talla sai dai ki mutu." Shiru tayi Rauda ta sunkuya ta d'auki kular da yake mai marik'i ce kuma bata da girma can ta kalli mahaifiyar ta ta da mahaifin ta tace, "Sai na dawo."
"Allah ya kiyaye" Umma ta furta a sanyaye tana kallon ta ta fita daga gidan jikinta a sanyaye.........
*KWANTAN ƁAUNA*
FitattuBiyar 2023.
©️ *Nana Haleema.*
*002.*
Bayan fitar Rauda Umma ta kalli Baba ta girgiza kai tace, "Dan Allah Malam ka daina d'orawa y'ay'an ka talla ka bar mu mu matan ka mu dinga siyar maka kome kake so a gida, tura yaran nan tallah babu abinda zai haifar sai d'a mara ido."
"Kedai kiyi masa amma ni kam gwara a d'ora musu tallan, yadda za'ayi rububin siya a wajan su mu baza'a yi a wajan mu ba. sune y'an mata wani saurayin ko dan su kula shi ma ya siya a wajan su" wacce take fitowa daga d'aya d'akin ta fad'a tana kallon Umma.
Baba yace, "bar ta Asabe ita ai baza ta tab'a ganewa ba shiyasa, indai akace an tab'a mata Rauda shikenan babu zaman lafiya, ko da yake tun lokacin yayyen Raudan ake fama da ita y'ar bak'in ciki ce bata so taga nayi arzuk'i." Murmushi Umma tayi ta kalle su cikin takaici tace, "Amma bakwa gudun wani abun ya faru dasu ta silar tallan da ake basu?, kun manta y'ay'a mata ne dukkan su sun kai munzalin aure?."
Baba ya nuna ta da yatsa yace, "Kinga Binta bana son mugun fata a kan yarana, ina yi musu addu'a ba dare babu rana Allah zai kare min su duk inda suke, kar na sake jin kin furta wata magana mara dad'i a kan su in ba so kike ranki ha b'aci ba." Umma bata kuma cewa komai ba ta koma d'akin ta.
Tana jiyo shi yana fad'in, "kuma wallahi kika cigaba da hure mata kunne akan yaron nan Anas da yake son ta take k'in sauraron sa ki kiyayi hukuncin da zan miki, ban tab'a ganin uwa y'ar bak'in ciki kamar ki ba. Ace y'ar ki ta samu mai kud'i amma ki dinga bari tana wulaƙanta shi....? ita ba y'ar kowa ba ba kuma jikar kowa ba, gata ita ba kyau ba balle ace shi ya gano ya nace amma ki dinga hure mata kunne."
Tana jin sa tayi shiru ta zauna a kan ledar da take shinfid'e a d'akin tana girgiza kai. Lamarin sa kullum sake gaba yake duk da girman da yake cimma masa, indai akan kud'i ne ba sani ba sabo, ko meye zaiyi indai akace kud'i zance ya k'are, tun lokacin baya haka yake gashi shekaru har sunyi nisa halayyar sa tana nan.
Malam Adam haifaffan garin azare ne mazaunin unguwar Katsalle, y'an uwan sa da kowa nasan y'an Azare ne a nan aka haife su a nan kuma suka tashi suke kuma zaune. Yana da mata guda biyu Asabe da Binta y'ay'a kuma yana da goma takwas mata biyu maza, Asabe tana da guda shida biyar mata namiji d'aya, Umma kuma uku mata d'aya namiji shine auta a gidan gabad'aya. Suna zaman lafiya babu laifi wata ran ka gansu kamar y'an uwa wata rana kuma da kaga yanayin su kasan kishiyoyin juna ne. An aurar da mata biyar uku suka rage a gidan, Rauda wacce ta kasance itace babba wanda suka rage a d'akin su sai k'anwar ta Ummulkhairi sai k'anin ta Khalil. D'aya d'akin kuma sa'ar Rauda mai suna Rahma sai k'anin ta Garzali.
Talakawa ne gidan wani lokacin abincin da zasu ci gagarar su yake sai dai kowa ya san abinda zai ci shida y'ay'an sa, mai gidan Allah ya d'ora masa san abin duniya baya jin kunyar rok'o haka baya jin kunyar cewa a bashi, koda sirikan sa ne mazajen y'ay'an sa indai Allah ya had'a su koda a hanya ne da wahala su rabu bai tambayi wani abun ba duk da suma ba masu kud'i bane ba. Tun y'ay'an nasa mata suna nuna rashin jin dad'in hakan da yake yiwa mazajen su har suka gaji domin ba zai daina ba.
Tunda su Rauda suka kammala secondary school suka sauke a islmaiyya ya ajjiye batun karatu daman dak'yar aka k'arasa shi, dak'yar da sid'in goshi da ya hana su cigaba da karatu yace bashi hali suka koma islmaiyya suna hadda shima dan kyauta ce wani d'an siyaya ya d'auki nayi. Shekarar farko aka kori Rahma ita kuma Rauda ta cigaba da yin haddar ta tana sake sanin littafan addini dan Allah ya bata kaifin basira.
Bayan ta kammala hadda a cikin shekara d'aya ta dawo gida sosai ta samu ilimi ta k'aru ta kuma san abubuwa da yawa a fanin addini, burin ta ta zama y'ar jarida amma kuma Baba ya daqile wannan burin nata domin yace bashi da halin da zai kaita jami'a dole ta jinginar da burin ta badan taso ba. Daga nan ya fara dafa musu abinci yana d'ora musu talla su shiga kasuwa su siyar su kawo masa kud'in ya d'aga pillow ya ajjiye dan babu wanda zai ci kud'in koda abinci ne babu a gidan sai dai a hak'ura.
Dangin sa babu wanda bai masa fad'a akan basu tallan nan da yake yi ba amma ya shafawa idanun sa toka yace shifa ya haife su baiga wanda zai dakatar dashi da neman kud'in sa ba dole aka hak'ura aka k'yale shi. Babban yayan Umma babban malami ne a garin kowa ya sanshi har shi sai da ya yiwa Baba magana a kai amma ya nuna shifa y'ay'an sane yana da iko dasu dole aka zuba masa idanu.
Masifar son kud'in sa ya amince ya ajjiye kud'in kar ya ci kar iyalan sa su ci amma zai ajjiye yayi ta kallon kud'in yana jin dad'i a fad'ar sa yace kallon kud'in ma rahama ne, da kansa yake girka musu abinci suna shiga kasuwa suna siyarwa gudun ma kar matan nasa su b'ata masa rai akan hakan shiyasa yake zagewa ya hura wuta ya dafa.
Rauda yarinya ce y'ar shekara ashirin da hud'u bata da wadaccen kyau haka baza'a ce mata mummuna ba ba laifi dai zata shiga kadaran kadahan, tana da farin jinin samari sabida ilimin addinin ta kowa abinda yake kwad'ayi kenan a tare da ita amma bata sauraron su burin ta karatun jarida ne amma mahaifin ta ya hana shiyasa bata kula su musamman masu kud'i Umman ta takan ce mata kar ta d'ora buri a zuciyar ta domin duniyar ta koma kwarya tabi kwarya.
Rauda wayayyiya ce in suna hira da Umma baza kace babar ta bace hira suke sosai suyi shawara kamar yaya da k'anwar ta. Sam Rauda bata da duhun kai in taga abu bata sani ba zata tambayi wanda ya sani ya fad'a mata sabida gaba hakan ya saka take a waye in taci kwalliya ka ganta baza kace yar Malam Adamu bace ba. Tana da kirki da girmama na gaba amma fa bata da kunya in aka tab'a ta, bata bari ko waye yayi mata sai ta mayar musamman a tab'a mata iyaye bata jure wannan.
Duk girman mutum in ya latsa ta bazata bar masa ba sai ta mayar a cewar in babba bai ja girman sa ba dan k'arami yabi ta kan girman nasa ba wani abun bane, Allah bai halicce ta da tsoro ba ko Baba ne yayi wani abun ba daidai ba zata same shi ta fad'a masa sai dai yayi mata fad'an ya gama tunda ta fad'a shinkenan, halitta d'aya take tsoro a duniya shine doki.
Anas ya jima yana bibiyar Rauda amma bata sauraron sa bai gaji ba duk sati sai yazo k'ofar gidan su koda bai ganta ba zai gama zaman sa ya tafi sabida Allah ya d'ora masa k'aunar ta, nutsuwar ta da ilimin ta yana daga cikin abinda yake sake jawo hankalin sa zuwa gare ta, kowa yana kaf unguwar itace mai haddar alkur'ani sau da dama y'an matan unguwar wajan ta suke zuwa tayi musu k'ari abinda yake sake burge Anas kenan da ita. In Baba yana nan ne yake tilasta mata zuwa wajan sa kawai dai ya bata wani abun ya kwace ya ajjiye gobe ma in ya dawo ya sake turata shine burin sa kawai.
*☆☆☆*
Aliyu tunda ya bar cikin gidan sarauta ya nufi wani plat house mai kyau da ya tsaru da falayoyi da fitala masu kyaun gaske, yana zaune a falon yayi shiru yana aikin jan tsaki ba komai ne yake k'ona masa rai ba sai zancen mahaifiyar sa akan Asad, pillow da yake ajjiye a kan kujara ya d'auka ya cillar cikin fushi yana jan numfashi zuciyar sa na mugun tafasa sabida bala'in b'acin rai da bak'in ciki.
Cize lips d'in sa yayi ya koma ya jingina da kujera yana jin d'aci yana tasowa daga cikin zuciyar sa har kan harshen sa yana jin sa. "meyasa komai sai Asad?, meyasa ni ba'a maganar zan yi sarauta sai shi?!" Ya fad'a da k'arfi yana d'aukar remote yayi jifa dashi ya daki bango ya tarwatse a wajan.
"Ya dai prince lafiya?" Wani matashi wanda bazai wuce sa'an sa ba ya fad'a yana shigowa falon yana bin sa da kallo, bai magana ba sai sake runtse idanun sa da yayi matashin ya zauna a kujerar da take kallon sa ganin yanayin da yake ciki ya saka yace, "Prince yane?." Nan ma bai masa magana ba bai kuma d'ago ba ganin hakan sai ya ja bakin sa ya tsuke baice komai ba sai da ya ga dama sannan ya d'ago ya sauke numfashi yana kallon sa shima yana kallon sa.
"Allah ya kiyaye" Umma ta furta a sanyaye tana kallon ta ta fita daga gidan jikinta a sanyaye.........
*KWANTAN ƁAUNA*
FitattuBiyar 2023.
©️ *Nana Haleema.*
*002.*
Bayan fitar Rauda Umma ta kalli Baba ta girgiza kai tace, "Dan Allah Malam ka daina d'orawa y'ay'an ka talla ka bar mu mu matan ka mu dinga siyar maka kome kake so a gida, tura yaran nan tallah babu abinda zai haifar sai d'a mara ido."
"Kedai kiyi masa amma ni kam gwara a d'ora musu tallan, yadda za'ayi rububin siya a wajan su mu baza'a yi a wajan mu ba. sune y'an mata wani saurayin ko dan su kula shi ma ya siya a wajan su" wacce take fitowa daga d'aya d'akin ta fad'a tana kallon Umma.
Baba yace, "bar ta Asabe ita ai baza ta tab'a ganewa ba shiyasa, indai akace an tab'a mata Rauda shikenan babu zaman lafiya, ko da yake tun lokacin yayyen Raudan ake fama da ita y'ar bak'in ciki ce bata so taga nayi arzuk'i." Murmushi Umma tayi ta kalle su cikin takaici tace, "Amma bakwa gudun wani abun ya faru dasu ta silar tallan da ake basu?, kun manta y'ay'a mata ne dukkan su sun kai munzalin aure?."
Baba ya nuna ta da yatsa yace, "Kinga Binta bana son mugun fata a kan yarana, ina yi musu addu'a ba dare babu rana Allah zai kare min su duk inda suke, kar na sake jin kin furta wata magana mara dad'i a kan su in ba so kike ranki ha b'aci ba." Umma bata kuma cewa komai ba ta koma d'akin ta.
Tana jiyo shi yana fad'in, "kuma wallahi kika cigaba da hure mata kunne akan yaron nan Anas da yake son ta take k'in sauraron sa ki kiyayi hukuncin da zan miki, ban tab'a ganin uwa y'ar bak'in ciki kamar ki ba. Ace y'ar ki ta samu mai kud'i amma ki dinga bari tana wulaƙanta shi....? ita ba y'ar kowa ba ba kuma jikar kowa ba, gata ita ba kyau ba balle ace shi ya gano ya nace amma ki dinga hure mata kunne."
Tana jin sa tayi shiru ta zauna a kan ledar da take shinfid'e a d'akin tana girgiza kai. Lamarin sa kullum sake gaba yake duk da girman da yake cimma masa, indai akan kud'i ne ba sani ba sabo, ko meye zaiyi indai akace kud'i zance ya k'are, tun lokacin baya haka yake gashi shekaru har sunyi nisa halayyar sa tana nan.
Malam Adam haifaffan garin azare ne mazaunin unguwar Katsalle, y'an uwan sa da kowa nasan y'an Azare ne a nan aka haife su a nan kuma suka tashi suke kuma zaune. Yana da mata guda biyu Asabe da Binta y'ay'a kuma yana da goma takwas mata biyu maza, Asabe tana da guda shida biyar mata namiji d'aya, Umma kuma uku mata d'aya namiji shine auta a gidan gabad'aya. Suna zaman lafiya babu laifi wata ran ka gansu kamar y'an uwa wata rana kuma da kaga yanayin su kasan kishiyoyin juna ne. An aurar da mata biyar uku suka rage a gidan, Rauda wacce ta kasance itace babba wanda suka rage a d'akin su sai k'anwar ta Ummulkhairi sai k'anin ta Khalil. D'aya d'akin kuma sa'ar Rauda mai suna Rahma sai k'anin ta Garzali.
Talakawa ne gidan wani lokacin abincin da zasu ci gagarar su yake sai dai kowa ya san abinda zai ci shida y'ay'an sa, mai gidan Allah ya d'ora masa san abin duniya baya jin kunyar rok'o haka baya jin kunyar cewa a bashi, koda sirikan sa ne mazajen y'ay'an sa indai Allah ya had'a su koda a hanya ne da wahala su rabu bai tambayi wani abun ba duk da suma ba masu kud'i bane ba. Tun y'ay'an nasa mata suna nuna rashin jin dad'in hakan da yake yiwa mazajen su har suka gaji domin ba zai daina ba.
Tunda su Rauda suka kammala secondary school suka sauke a islmaiyya ya ajjiye batun karatu daman dak'yar aka k'arasa shi, dak'yar da sid'in goshi da ya hana su cigaba da karatu yace bashi hali suka koma islmaiyya suna hadda shima dan kyauta ce wani d'an siyaya ya d'auki nayi. Shekarar farko aka kori Rahma ita kuma Rauda ta cigaba da yin haddar ta tana sake sanin littafan addini dan Allah ya bata kaifin basira.
Bayan ta kammala hadda a cikin shekara d'aya ta dawo gida sosai ta samu ilimi ta k'aru ta kuma san abubuwa da yawa a fanin addini, burin ta ta zama y'ar jarida amma kuma Baba ya daqile wannan burin nata domin yace bashi da halin da zai kaita jami'a dole ta jinginar da burin ta badan taso ba. Daga nan ya fara dafa musu abinci yana d'ora musu talla su shiga kasuwa su siyar su kawo masa kud'in ya d'aga pillow ya ajjiye dan babu wanda zai ci kud'in koda abinci ne babu a gidan sai dai a hak'ura.
Dangin sa babu wanda bai masa fad'a akan basu tallan nan da yake yi ba amma ya shafawa idanun sa toka yace shifa ya haife su baiga wanda zai dakatar dashi da neman kud'in sa ba dole aka hak'ura aka k'yale shi. Babban yayan Umma babban malami ne a garin kowa ya sanshi har shi sai da ya yiwa Baba magana a kai amma ya nuna shifa y'ay'an sane yana da iko dasu dole aka zuba masa idanu.
Masifar son kud'in sa ya amince ya ajjiye kud'in kar ya ci kar iyalan sa su ci amma zai ajjiye yayi ta kallon kud'in yana jin dad'i a fad'ar sa yace kallon kud'in ma rahama ne, da kansa yake girka musu abinci suna shiga kasuwa suna siyarwa gudun ma kar matan nasa su b'ata masa rai akan hakan shiyasa yake zagewa ya hura wuta ya dafa.
Rauda yarinya ce y'ar shekara ashirin da hud'u bata da wadaccen kyau haka baza'a ce mata mummuna ba ba laifi dai zata shiga kadaran kadahan, tana da farin jinin samari sabida ilimin addinin ta kowa abinda yake kwad'ayi kenan a tare da ita amma bata sauraron su burin ta karatun jarida ne amma mahaifin ta ya hana shiyasa bata kula su musamman masu kud'i Umman ta takan ce mata kar ta d'ora buri a zuciyar ta domin duniyar ta koma kwarya tabi kwarya.
Rauda wayayyiya ce in suna hira da Umma baza kace babar ta bace hira suke sosai suyi shawara kamar yaya da k'anwar ta. Sam Rauda bata da duhun kai in taga abu bata sani ba zata tambayi wanda ya sani ya fad'a mata sabida gaba hakan ya saka take a waye in taci kwalliya ka ganta baza kace yar Malam Adamu bace ba. Tana da kirki da girmama na gaba amma fa bata da kunya in aka tab'a ta, bata bari ko waye yayi mata sai ta mayar musamman a tab'a mata iyaye bata jure wannan.
Duk girman mutum in ya latsa ta bazata bar masa ba sai ta mayar a cewar in babba bai ja girman sa ba dan k'arami yabi ta kan girman nasa ba wani abun bane, Allah bai halicce ta da tsoro ba ko Baba ne yayi wani abun ba daidai ba zata same shi ta fad'a masa sai dai yayi mata fad'an ya gama tunda ta fad'a shinkenan, halitta d'aya take tsoro a duniya shine doki.
Anas ya jima yana bibiyar Rauda amma bata sauraron sa bai gaji ba duk sati sai yazo k'ofar gidan su koda bai ganta ba zai gama zaman sa ya tafi sabida Allah ya d'ora masa k'aunar ta, nutsuwar ta da ilimin ta yana daga cikin abinda yake sake jawo hankalin sa zuwa gare ta, kowa yana kaf unguwar itace mai haddar alkur'ani sau da dama y'an matan unguwar wajan ta suke zuwa tayi musu k'ari abinda yake sake burge Anas kenan da ita. In Baba yana nan ne yake tilasta mata zuwa wajan sa kawai dai ya bata wani abun ya kwace ya ajjiye gobe ma in ya dawo ya sake turata shine burin sa kawai.
*☆☆☆*
Aliyu tunda ya bar cikin gidan sarauta ya nufi wani plat house mai kyau da ya tsaru da falayoyi da fitala masu kyaun gaske, yana zaune a falon yayi shiru yana aikin jan tsaki ba komai ne yake k'ona masa rai ba sai zancen mahaifiyar sa akan Asad, pillow da yake ajjiye a kan kujara ya d'auka ya cillar cikin fushi yana jan numfashi zuciyar sa na mugun tafasa sabida bala'in b'acin rai da bak'in ciki.
Cize lips d'in sa yayi ya koma ya jingina da kujera yana jin d'aci yana tasowa daga cikin zuciyar sa har kan harshen sa yana jin sa. "meyasa komai sai Asad?, meyasa ni ba'a maganar zan yi sarauta sai shi?!" Ya fad'a da k'arfi yana d'aukar remote yayi jifa dashi ya daki bango ya tarwatse a wajan.
"Ya dai prince lafiya?" Wani matashi wanda bazai wuce sa'an sa ba ya fad'a yana shigowa falon yana bin sa da kallo, bai magana ba sai sake runtse idanun sa da yayi matashin ya zauna a kujerar da take kallon sa ganin yanayin da yake ciki ya saka yace, "Prince yane?." Nan ma bai masa magana ba bai kuma d'ago ba ganin hakan sai ya ja bakin sa ya tsuke baice komai ba sai da ya ga dama sannan ya d'ago ya sauke numfashi yana kallon sa shima yana kallon sa.