Sashe 2
Kwantan Bauna Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
*☆☆☆*
Babban falo ne na isa da girma da kuma k'asaita da alfarma, kana kallon falon kasan na manyan mutane ne masu tak'ama da aji da kuma sarauta, domin kuwa kalar adon da akayi masa da kalar kujerun cikin sa kana kallon sa kasan bana talaka bane sai na mai arzuk'i arzuk'in ma irin na y'ay'an masarauta.
A zaune take ta d'ora k'afar ta akan pillow mata guda biyu suna matsa mata k'afafun ta a hankali hannun rik'e da waya tana dannawa hankalin ta a kwance.
Fara ce sosai mai kyau kana ganin ta kasan ta manyan ta amma kasancewar kud'i da hutu bai nuna ba in ka ganta baza ka d'auka tana da manyan yara ba, mulki,k'asaita, izza, ko in kula ya ratsa jikin ta sosai dan ko yanayin da take danna wayar da izza take yin ta.
Maza uku ne masu kama sak da juna samari matasa masu jini a jika suka shigo cikin falon nata da sallama. A k'alla zasu yi shekara ashirin da tara zuwa da talatin da haihuwa dogaye kyawawa masu kama da mahaifiyar su masu zagayayyen gashi bak'i a fuskar su. Farare ne dukkan su kana kallon su kaga y'an uku domin kamar da suke ta b'aci musamman guda biyu a cikin su babu abinda ya banbanta su sai adon gemu, dukkan su manyan kaya ne a jikin su irin na sarauta sun d'ora riga mai zanen sarauta a sama ko wanne da kalar tasa sunyi kyau sun amshi jikin su sosai duk da yanayin fuskar ko wannen su ya banbanta.
Zubewa bayin gaban ta suke suna kwasar gaisuwa amma babu wanda ya kula su a cikin su k'asa suka zauna kusa da k'afafun mahaifiyar su suka gaishe ta a tare ta amsa tana kallon su, Murmushi take tana kallon su alfahari yana sake mamaye zuciyar ta, ko a wannan b'angaren tasan ta yiwa abokan zaman ta fintinkau itace da gida, itace da katagum, ta kalli bayin nata sai jikin su ya fara k'yarma suka mik'e suka fita da sauri domin yanayin kallon da tayi musu sun fahimci me take nufi.
"Tun d'azu na aika kuzo dukkan ku sai yanzu kuka ga damar fitowa?." Wanda yake danna waya ne ya d'ago ya kalle ta yace, "Allah ya wuci zuciyar ki, Lokacin ina wanka ne." Hararar sa tayi jin abinda yace ta gane waye a cikin su tace, "kodai kana waya da y'an matan ka?." Baice komai ba ya d'auke kansa ya kalli k'asa.
Girgiza kai tayi kafin ta kalli na gefen ta tace, "Kai nasan daman indai kiran yazo wajan ka zaka iso kai bana jin ka Hydar" ta fad'a tana kallon sa.
Asad ta kalla wanda yake kallon k'asa yana wasa da gashin carpet d'in falon da farin hannun sa mai d'auke da azurfa kalar golden ta haska hannun sa sosai, shi kansa hannun nasa abin kallo ne. Tasan kome za'ayi bazai furta komai ba kallo ma bazai kalle su ba balle magana. "Asad!." D'ago idanu yayi ya kalle ta amma bai amsa ba, ta san bazai amsa hakan ya saka tace, "meyasa baka je zaman fada ba d'azu?."
Kansa ya mayar k'asa baice komai ba tace, "ba magana nake maka bane?, meyasa baka je fada ba matsayin ka na magajin wannan gida ko hukuncin mai martaba bai zo kunnen ka bane?."
"Allah yaja da ranki Mama ni banga dalilin da zai saka kina kiran sa magaji ba bayan nine babba a cikin mu, baki tab'a kira na magaji ba meyasa sai shi?" Aliyu ya fad'a yana kallon k'asa da alama ya gaji da jure yawan kiran sa da magaji da take yi.
Kallon sa tayi tace, "A hakan zaka zama magajin sarauta Aliyu? A hakan zaka mulki katagum?." Shiru yayi bai amsa ba ta dawo da kallon ta ga Asad tace, "Ko baza kayi magana ba nasan kana ji na Asad, duk wani abun da kake ji dashi a kanka ka ajjiye shi ka dinga zama kusa da mahaifin ka kana fahimtar yadda tsarin sarauta yake, kai kad'ai ne damar da nake da ita na zama mahaifiyar sarki kasan shine burina ya zamar maka dole ka cika min ita."
Rausayar da kansa yayi cikin muryar sa da bata fita sosai sabida taushin ta yace, "Allah yaja zamanin ki Mama, Bana so!."
"Dole kaso tunda ni ina so, kai kad'ai ne burina domin cikin y'an uwan ka gasu a zaune duk ka fisu quality, kai mahaifin ka ya zab'a har ya furta kai zai bawa kujerar sa sabida kullum k'arfin sa k'arewa yake dole kayi abinda nake so Asad koda kai baka so."
Runtse idanun sa yayi ya sake mayar da idanun sa k'asa Aliyu da yake ji kamar ya shak'e wuyan Asad sabida bak'in ciki yace, "Mama wai meye laifina ne ni da baza'a bani ragamar rik'e magajin masarautar katagum bane?, Asad baya so ni ina so meyasa baza'a bani ba ni?" Ya fad'a a tausahe duk da ransa a b'ace yake bai bari yayi mata magana da k'arfi ba sabida girman biyayya.
"Sabida baka dace ba Aliyu, baka da wadattacen ilimin addini, banzayen dabi'un ka na neman matan tsiya waye zai baka ragamar al'uma a hannun ka?. har bayin gidan nan baka bari ba badan na saka an binne zancen baiwar da ka lalata ba na saka a mayar da ita k'auye da yanzu mahaifin ka bai hukunta ka ba?." Shiru yayi bai amsa ba ta ja tsaki ta nuna shi da yatsa tace, "kar ina maganar sarautar gidan nan ka sake saka min baka, baka dace ba ba kuma zaka dace ba Aliyu. Asad shine magaji shine zai gaji mahaifin ku shine zai mulki masarautar katagum ba kai ba!."
Ran Aliyu ya kai k'ololuwa wajan b'aci ya cize bakin sa yace, "in kinyi min izini zan iya tafiya?." Mama ta bishi da kallo tace, "Tashi ka bani waje." Ba musu ya mik'e yace, "A huta lafiya" ya fad'a yana fita daga falon zuciyar sa a cushe.
Dawo da kallon ta tayi ga Asad tace, "kaji abinda nace maka ko?." D'aga kai yayi alamun eh tace, "tashi kaje anjima zan neme ka." Mik'ewa tsaye yayi baice komai ba ya fita aka bar Hydar a zaune kusa da ita.
Hydar ta kalla ta ga yana ta murmushi itama tayi murmushin tace, "Hydar Allah ya baka lafiya, bana son yawan ciwon nan naka ko kad'an" Murmushi yayi yace, "Amin Mama. Amma Allah yaja da ranki sai nake ganin da ki k'yale Deaf da batun sarautar nan baya so." D'aure fuska tayi tace, "ka daina kiran sa da kurma na fad'a maka rashin magana yake da ita amma shi ba kurma bane ba, sarauta kuma sai yayi da izinin Allah." Yace, "Allah ya wuci zuciyar ki, ina neman afuwa."
Numfashi ta sauke ta koma ta jingina da kujera tana kad'a k'afar ta, babban burin ta a rayuwar ta a yanzu shine Asad ya gaji sarautar masarautar katagum kamar yadda mahaifin sa yake son hakan, bata so sarautar ta fita daga gidan domin matuk'ar ta bar gidan zata cigaba da zaga dangin mahaifin sa ne maimakon y'ay'an ta da jikokin ta, "dole ma Asad ya karb'i mulkin nan koda baya so, tunda har mahaifinsa ya furta shi zai bawa mulkin nan komai zai tafi yadda na tsara."
Asad koda ya fita fadar cikin gida ya nufa domin amsa kiran mahaifin sa, tafiya yake a nutse kana kallon sa izza da k'asaita da tak'ama ta gama ratsa ko wanne b'angare na jikin sa, kasancewar sa mai nutsuwa sai akayi sa'a aka had'a nutsuwa da sarauta sai suka bada kalar izza ta musamman wacce kafin ka samu mai irin ta sai ka tona. Dak'yar yake taka k'afar sa sabida sarautar da ta gama ratsa jijiya da tsokar jikin sa, kamar yana tausayin k'asa haka yake tafiya bakin sa na motsawa a hankali yana furta kalmar da ta zame masa jiki a koda yaushe wato Astagafirullah.
Zubewa ake ana gaishe shi sai dai ya kad'a kai ko ya d'aga hannu amma magana koda motsa bakin sane baya yi sai lazimin da yake yi, Ba jimawa ya k'araso k'aramar fada yasan tabbas mahaifin sa yana ciki ya shiga da sallama cikin muryar sa da bata fita sosai.
Ga mamakin sa mahaifin nasa baya nan sai dogarai da alama bai jima da tashi ba, "barka da shigowa Yarima mai jiran gado, barka da zuwa magajin masarautar katagum, Allah ya tsare mana kai, ya kare ka daga dukkan makiyan ka, takawar ka lafiya......" D'aga masa musu hannu yayi hakan ya saka su jan bakin su sukayi shiru ya kalli kujerar mahaifin sa ya kalle su nan take suka gane mai yake nufi cikin girmamawa suka ce, "mai martaba ya shiga ciki" suka fad'a suna sunkuyar da kansu suna yi masa jinjina.
Baice komai ba ya juya yana ji suna kwara masa kirari ya yatsine fuska ya nufi babban falon sa na cikin gidan, da gajeriyar sallama ya shiga mahaifin sa na hango shi annunirin fuskar sa ta bayyana yana zaune su biyu kacal daga shi sai k'anin sa da suke ciki d'aya wanda ya kasance wambai katagum suna tattaunawa, k'arasowa yayi da girmamawa ya gaida mahaifin nasa ya amsa yana fad'in, "Asad zaki na, barka da zuwa."
Murmushi yayi wanda ya k'ara saka fuskar sa annuri da kyau ta fito da zallar k'uruciyar sa amma baice komai ba, wanda yake a zaune shima murmushin yake yace, "Asad ikon Allah." Mai martaba yana kallon sa yace, "ya akayi ne Asad? Akwai wani abun ne?."
Kai ya girgiza kai alamun babu komai yana murmushi amma baice komai ba, "in anjima kazo ina neman ka." Kai ya d'aga kafin yace, "to in sha Allah zan amsa kira."
Mahaifin nasa yace, "Zaka iya tafiya." Ya sake duk'ar da kansa yace, "Godiya nake. A tashi lafiya" Daga haka ya mik'e ya fita suka bishi da kallo kafin mai martaba yace, "Mubarak ya kake ganin ranar dana ajjiye sarautar nan Asad zai iya mulkin nan kuwa?."
Babban falo ne na isa da girma da kuma k'asaita da alfarma, kana kallon falon kasan na manyan mutane ne masu tak'ama da aji da kuma sarauta, domin kuwa kalar adon da akayi masa da kalar kujerun cikin sa kana kallon sa kasan bana talaka bane sai na mai arzuk'i arzuk'in ma irin na y'ay'an masarauta.
A zaune take ta d'ora k'afar ta akan pillow mata guda biyu suna matsa mata k'afafun ta a hankali hannun rik'e da waya tana dannawa hankalin ta a kwance.
Fara ce sosai mai kyau kana ganin ta kasan ta manyan ta amma kasancewar kud'i da hutu bai nuna ba in ka ganta baza ka d'auka tana da manyan yara ba, mulki,k'asaita, izza, ko in kula ya ratsa jikin ta sosai dan ko yanayin da take danna wayar da izza take yin ta.
Maza uku ne masu kama sak da juna samari matasa masu jini a jika suka shigo cikin falon nata da sallama. A k'alla zasu yi shekara ashirin da tara zuwa da talatin da haihuwa dogaye kyawawa masu kama da mahaifiyar su masu zagayayyen gashi bak'i a fuskar su. Farare ne dukkan su kana kallon su kaga y'an uku domin kamar da suke ta b'aci musamman guda biyu a cikin su babu abinda ya banbanta su sai adon gemu, dukkan su manyan kaya ne a jikin su irin na sarauta sun d'ora riga mai zanen sarauta a sama ko wanne da kalar tasa sunyi kyau sun amshi jikin su sosai duk da yanayin fuskar ko wannen su ya banbanta.
Zubewa bayin gaban ta suke suna kwasar gaisuwa amma babu wanda ya kula su a cikin su k'asa suka zauna kusa da k'afafun mahaifiyar su suka gaishe ta a tare ta amsa tana kallon su, Murmushi take tana kallon su alfahari yana sake mamaye zuciyar ta, ko a wannan b'angaren tasan ta yiwa abokan zaman ta fintinkau itace da gida, itace da katagum, ta kalli bayin nata sai jikin su ya fara k'yarma suka mik'e suka fita da sauri domin yanayin kallon da tayi musu sun fahimci me take nufi.
"Tun d'azu na aika kuzo dukkan ku sai yanzu kuka ga damar fitowa?." Wanda yake danna waya ne ya d'ago ya kalle ta yace, "Allah ya wuci zuciyar ki, Lokacin ina wanka ne." Hararar sa tayi jin abinda yace ta gane waye a cikin su tace, "kodai kana waya da y'an matan ka?." Baice komai ba ya d'auke kansa ya kalli k'asa.
Girgiza kai tayi kafin ta kalli na gefen ta tace, "Kai nasan daman indai kiran yazo wajan ka zaka iso kai bana jin ka Hydar" ta fad'a tana kallon sa.
Asad ta kalla wanda yake kallon k'asa yana wasa da gashin carpet d'in falon da farin hannun sa mai d'auke da azurfa kalar golden ta haska hannun sa sosai, shi kansa hannun nasa abin kallo ne. Tasan kome za'ayi bazai furta komai ba kallo ma bazai kalle su ba balle magana. "Asad!." D'ago idanu yayi ya kalle ta amma bai amsa ba, ta san bazai amsa hakan ya saka tace, "meyasa baka je zaman fada ba d'azu?."
Kansa ya mayar k'asa baice komai ba tace, "ba magana nake maka bane?, meyasa baka je fada ba matsayin ka na magajin wannan gida ko hukuncin mai martaba bai zo kunnen ka bane?."
"Allah yaja da ranki Mama ni banga dalilin da zai saka kina kiran sa magaji ba bayan nine babba a cikin mu, baki tab'a kira na magaji ba meyasa sai shi?" Aliyu ya fad'a yana kallon k'asa da alama ya gaji da jure yawan kiran sa da magaji da take yi.
Kallon sa tayi tace, "A hakan zaka zama magajin sarauta Aliyu? A hakan zaka mulki katagum?." Shiru yayi bai amsa ba ta dawo da kallon ta ga Asad tace, "Ko baza kayi magana ba nasan kana ji na Asad, duk wani abun da kake ji dashi a kanka ka ajjiye shi ka dinga zama kusa da mahaifin ka kana fahimtar yadda tsarin sarauta yake, kai kad'ai ne damar da nake da ita na zama mahaifiyar sarki kasan shine burina ya zamar maka dole ka cika min ita."
Rausayar da kansa yayi cikin muryar sa da bata fita sosai sabida taushin ta yace, "Allah yaja zamanin ki Mama, Bana so!."
"Dole kaso tunda ni ina so, kai kad'ai ne burina domin cikin y'an uwan ka gasu a zaune duk ka fisu quality, kai mahaifin ka ya zab'a har ya furta kai zai bawa kujerar sa sabida kullum k'arfin sa k'arewa yake dole kayi abinda nake so Asad koda kai baka so."
Runtse idanun sa yayi ya sake mayar da idanun sa k'asa Aliyu da yake ji kamar ya shak'e wuyan Asad sabida bak'in ciki yace, "Mama wai meye laifina ne ni da baza'a bani ragamar rik'e magajin masarautar katagum bane?, Asad baya so ni ina so meyasa baza'a bani ba ni?" Ya fad'a a tausahe duk da ransa a b'ace yake bai bari yayi mata magana da k'arfi ba sabida girman biyayya.
"Sabida baka dace ba Aliyu, baka da wadattacen ilimin addini, banzayen dabi'un ka na neman matan tsiya waye zai baka ragamar al'uma a hannun ka?. har bayin gidan nan baka bari ba badan na saka an binne zancen baiwar da ka lalata ba na saka a mayar da ita k'auye da yanzu mahaifin ka bai hukunta ka ba?." Shiru yayi bai amsa ba ta ja tsaki ta nuna shi da yatsa tace, "kar ina maganar sarautar gidan nan ka sake saka min baka, baka dace ba ba kuma zaka dace ba Aliyu. Asad shine magaji shine zai gaji mahaifin ku shine zai mulki masarautar katagum ba kai ba!."
Ran Aliyu ya kai k'ololuwa wajan b'aci ya cize bakin sa yace, "in kinyi min izini zan iya tafiya?." Mama ta bishi da kallo tace, "Tashi ka bani waje." Ba musu ya mik'e yace, "A huta lafiya" ya fad'a yana fita daga falon zuciyar sa a cushe.
Dawo da kallon ta tayi ga Asad tace, "kaji abinda nace maka ko?." D'aga kai yayi alamun eh tace, "tashi kaje anjima zan neme ka." Mik'ewa tsaye yayi baice komai ba ya fita aka bar Hydar a zaune kusa da ita.
Hydar ta kalla ta ga yana ta murmushi itama tayi murmushin tace, "Hydar Allah ya baka lafiya, bana son yawan ciwon nan naka ko kad'an" Murmushi yayi yace, "Amin Mama. Amma Allah yaja da ranki sai nake ganin da ki k'yale Deaf da batun sarautar nan baya so." D'aure fuska tayi tace, "ka daina kiran sa da kurma na fad'a maka rashin magana yake da ita amma shi ba kurma bane ba, sarauta kuma sai yayi da izinin Allah." Yace, "Allah ya wuci zuciyar ki, ina neman afuwa."
Numfashi ta sauke ta koma ta jingina da kujera tana kad'a k'afar ta, babban burin ta a rayuwar ta a yanzu shine Asad ya gaji sarautar masarautar katagum kamar yadda mahaifin sa yake son hakan, bata so sarautar ta fita daga gidan domin matuk'ar ta bar gidan zata cigaba da zaga dangin mahaifin sa ne maimakon y'ay'an ta da jikokin ta, "dole ma Asad ya karb'i mulkin nan koda baya so, tunda har mahaifinsa ya furta shi zai bawa mulkin nan komai zai tafi yadda na tsara."
Asad koda ya fita fadar cikin gida ya nufa domin amsa kiran mahaifin sa, tafiya yake a nutse kana kallon sa izza da k'asaita da tak'ama ta gama ratsa ko wanne b'angare na jikin sa, kasancewar sa mai nutsuwa sai akayi sa'a aka had'a nutsuwa da sarauta sai suka bada kalar izza ta musamman wacce kafin ka samu mai irin ta sai ka tona. Dak'yar yake taka k'afar sa sabida sarautar da ta gama ratsa jijiya da tsokar jikin sa, kamar yana tausayin k'asa haka yake tafiya bakin sa na motsawa a hankali yana furta kalmar da ta zame masa jiki a koda yaushe wato Astagafirullah.
Zubewa ake ana gaishe shi sai dai ya kad'a kai ko ya d'aga hannu amma magana koda motsa bakin sane baya yi sai lazimin da yake yi, Ba jimawa ya k'araso k'aramar fada yasan tabbas mahaifin sa yana ciki ya shiga da sallama cikin muryar sa da bata fita sosai.
Ga mamakin sa mahaifin nasa baya nan sai dogarai da alama bai jima da tashi ba, "barka da shigowa Yarima mai jiran gado, barka da zuwa magajin masarautar katagum, Allah ya tsare mana kai, ya kare ka daga dukkan makiyan ka, takawar ka lafiya......" D'aga masa musu hannu yayi hakan ya saka su jan bakin su sukayi shiru ya kalli kujerar mahaifin sa ya kalle su nan take suka gane mai yake nufi cikin girmamawa suka ce, "mai martaba ya shiga ciki" suka fad'a suna sunkuyar da kansu suna yi masa jinjina.
Baice komai ba ya juya yana ji suna kwara masa kirari ya yatsine fuska ya nufi babban falon sa na cikin gidan, da gajeriyar sallama ya shiga mahaifin sa na hango shi annunirin fuskar sa ta bayyana yana zaune su biyu kacal daga shi sai k'anin sa da suke ciki d'aya wanda ya kasance wambai katagum suna tattaunawa, k'arasowa yayi da girmamawa ya gaida mahaifin nasa ya amsa yana fad'in, "Asad zaki na, barka da zuwa."
Murmushi yayi wanda ya k'ara saka fuskar sa annuri da kyau ta fito da zallar k'uruciyar sa amma baice komai ba, wanda yake a zaune shima murmushin yake yace, "Asad ikon Allah." Mai martaba yana kallon sa yace, "ya akayi ne Asad? Akwai wani abun ne?."
Kai ya girgiza kai alamun babu komai yana murmushi amma baice komai ba, "in anjima kazo ina neman ka." Kai ya d'aga kafin yace, "to in sha Allah zan amsa kira."
Mahaifin nasa yace, "Zaka iya tafiya." Ya sake duk'ar da kansa yace, "Godiya nake. A tashi lafiya" Daga haka ya mik'e ya fita suka bishi da kallo kafin mai martaba yace, "Mubarak ya kake ganin ranar dana ajjiye sarautar nan Asad zai iya mulkin nan kuwa?."