Sashe 47
Kwantan Bauna Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Hydar ya kalli Asad da ya zuba mata idanu kawai yana kallon ta ya girgiza kai yana cize bakin sa cikin zallan b'acin ran da yake ji a zuciyar sa, in badan Asad ba ta isa ta dinga fad'a masa wannan kalmai marasa dad'in jin ya tsaya yana kallon ta bai hukunta ta ba?. Ya daure yace, "Ni da kaina nace kuyi hak'uri muje a fara yi muku magani kafin komai." Kafin Baba yayi magana ta kuma cewa, "Bama so ku rik'e kayan ku talakawan da ake rainawa sun yiwa kansu magani kuma zasu karb'arwa kansu hakkin kansu."
"Wai ke meye haka ne? Ina baki hak'uri kina sake d'aga min murya kina fad'ar duk abinda yazo bakin ki?, wani dalili kawai ya saka nake tsaye a gaban ki ina baki hak'uri amma badan shi ba bazan zo inda kuke bama balle ki samu bakin fad'a min abinda kike so. Na fad'a miki kuyi hak'uri zaku ji abinda ya jawo hakan wanda ban sani ba shima wanda akayi dukan dan shi bai sani ba, meyasa kike haka ne?" Ya fad'a cikin fad'a yana kallon ta ransa a b'ace. Zata kuma magana Baba yace, "Muna so muji dalilin dan gaskiya sai maganar nan taje kunnen mahaifin ku sai naji dalilin dukan da aka yiwa iyalai na har cikin gida."
"Firstly ku fara ganin likita a duba lafiyar ku, please Baba kuzo muje" Hydar ya sake fad'a yana kallon Baba. Rauda ta kalli Asad da idanun sa yake yawo a kanta amma in baka fahimta ba baza kace ita yake kallo ba taja dogon tsaki tace, "Wanda akayi dan shi d'in yana tsaye k'ikam shi bazai bada hak'uri ba sabida bamu kai ya bamu hak'uri ba an dake mu an daki banza kenan, to wallahi sai na d'auki mataki ina k'yale komai banda a tab'a min iyayena." D'auke kai yayi daga kanta Baba ya kalle ta yace, "Ya isa haka Rauda bana son sake jin bakin ki, ke Rahma tashi mu taimaka mata ta tashi aje asibitin."
Tare da Baba suka fita Rahma da Inna suka fito da Umma da Rauda suka shiga bayan mota Baba ma ya shiga Hydar ya shiga mazaunin driver dan yasan Asad bazai iya tuk'i ba ya ja motar suka tafi asibiti. Babu wanda yake magana a cikin su har suka je asibitin ya saka aka duba su aka sake gyara ciwon hannu Umma aka sake wanke ciwukan fuskar su duk da ba masu yawa bane ba. A d'akin da suke suna hutawa bayan an gama Umma taji dad'in jikin ta su Hydar sunje sun dawo Asad ya kalli Umma yace, "kiyi hak'uri Mama."
Umma tace, "To ya zanyi in ba hak'urin ba?, babu komai." Hydar yace, "Baba zaku koma wani gidan daman kafin a gama gyara wancan zan kai ku yanzu suma wad'ancan zan koma na kai su gidan, in kawai abinda kuke da buk'ata sai a d'auko muku." Baba yace, "to sai muje tare in yaso akwai k'anwar Rauda nasan zuwa yanzu ta dawo daga makaranta sai ta d'auko musu abinda zata d'auko." Rauda Hydar ya kalla da take kallon wani wajan daban ya kalli Asad da yake a tsaye baice komai ba shima ya d'auke kansa.
"Baba muje" Asad ya fad'a yana kallon su suka tashi suka fito zuwa inda motar take suka shiga suka tafi. Kusa da unguwar su suka tsaya jikin wani gida babba flat mai maroon d'in gate da maroon d'in fenti yayi kyau sosai kamar sabo dan kana gani kasa ba'a zama a cikin sa kawai yana ajjiye ne. Asad ya fito Hydar ma ya fito suka cewa Baba shima ya fito.
Gidan suka shiga Jim kad'an suka fito Baba yace, "Kuzo muje ciki." Umma ce ta fita Rauda kam k'in fitowa tayi Baba yace, "baza ki fito bane ba?." Ta kalli Baba zuciyar ta kamar ana tafasa ta sabida b'acin rai tace, "Zan fito daga baya." Shi da Umma suka shiga gidan ta bisu da kallo tana kiyasta adadin matakin da zata d'auka a zuciyar ta.
Hydar ne ya shiga gaban motar ya zauna bai kalle ta bayace, "ki ajjiye abinda kike ji dashi a kanki ki fahimci abinda zan fad'a miki yanzu. Ina so ki fahimci abun dakyau kiyi tunanin kalaman da suka fad'a miki akan Asad ki gano me hakan yake nufi." Shiru tayi dan har lokacin a fusace take kafin ta girgiza kai tace, "A yanayin maganar su yayi kama da b'atan kai sukayi suna so suje wajan wacce take sonsa ko dai abinda yayi kama da haka." Hydar yace, "good girl. Ba b'atan kai sukayi ba Rauda tabbas kece."
"Nice me?."
"Kece wacce Allah ya d'orawa Asad k'aunar ta a zuciyar sa!."
Gaban Rauda ya fad'i har ta dafe k'irji bata san tayi ba ta kalle shi cikij tsananin bugawar zuciya a firgice tace, "Me kake nufi?."
Hydar ya juyo ya kalle ta yace, "Ina nufin Asad yana sonki yana kuma fatan auren ki dalilin da ya saka wanda basa goyan baya suka fara d'aukar mataki a kanki, dan farawa akayi in maganar ta cigaba tabbas akwai wasu abubuwa a gaba wanda zan iya cewa sunfi wannan. Na zab'i na fad'a miki ne ba tare da ya sani ba dan kisan dalilin da ya saka akayi miki haka." Shiru Rauda tayi ta kasa magana sai zuciyar ta da take bugawa da sauri-sauri tana sake maimaita kalmar yana sonta a zuciyar ta cikin mamaki da tsoro da ya bayyana a gare ta.
"Sona fa kace? Ta yaya zan amince da hakan bayan matsayin sa da nawa akwai banbanci?, har yaushe mukayi had'uwar da zai fara sona?, har yaushe ya sanni? Yaushe ya ganni da zai soni?. Wad'an nan kalaman naka sun sake bani tsoro sun tabbatar min da akwai wani abun da kuke nema dani shiyasa tun yanzu kuka fata bayyanar da nufin ku a gare ni. Shin me nayi muku?." Murmushi Hydar yayi yace, "Inda akwai abinda muke nema dake da tuni mun aiwatar dashi babu wanda ya sani basai anzo yanzu ba. ki tuna abinda Aliyu yayi miki wanda babu wanda ya sani har kawo gobe kinga da munyi niya zamu iya aikata abinda yafi haka babu wanda yasan mune muka aikata, in munso har ranki zamu iya d'auka babu wanda sai san mune to a kan me dan muna da wata manufa a kanki sai biyo ta wannan hanyar?. In muna da manufa a kan ki bazan tankare ki da wannan maganar ba domin furta tama ba ga ko wacce mace ya dace ba sai wacce ta isa, ke kin san su waye mu basai an fad'a miki ba." Kalaman sa sun shige ta sosai bakin ta ya mutu murus ta kasa furta komai domin ta tabbatar da abinda yace gaskiya da akwai manufar da suke da ita baza su tunkare ta ba, kallon window tayi zuciyar ta na zillo a lokacin Asad yazo wajan shida Baba.
Baba ya bud'e mata yace, "fito ki huta zamu jemu tawo da sauran." Jikinta ya mutu Baba ya rik'o ta suka shiga cikin gidan da ta kasa kallon sa sabida tunanin abinda aka fad'a mata ya tsaya mata a zuciya kamar an soka mata mashi a zuciyar ta haka take ji. Gida ne babba sosai mai babban ma'ajiyar mota sai babban tsakar gida sai kuma k'ofa guda uku a tsakar gidan. Guda d'aya suka shiga sai gasu a falo babba mai kyau wanda babu abinda babu a cikin sa har da a.c da duk wani abun buk'ata akwai shi a falon ya zaunar da ita ya koma.
Basu jima ba suka dawo dasu Inna bayan sun d'auko kayan sawa da abin buk'ata suka shiga ciki Baba ya tsaya yace ya kalle su, "To mun gode muku Allah ya saka da alkhairi, kunyi bakin k'okarin ku akan mu badan ku ba da bamu san inda zamu je mu zauna ba. amma duk da haka inaso maganar nan tazo gaban mai martaba." Hydar yace, "Kar ka damu Baba mu da kanmu zamu sanar masa baza a bar maganar ba in sha Allah. Za'a kawo abinci yanzu." Baba ya amsa ya shiga ciki suma suka shiga motar Hydar ya fincike ta zuwa gida.
A can gida kuwa Mum tana wajan Mama ranta a b'ace take zayyanawa Mama abinda ya faru tana had'awa da k'arya akan abinda Rauda tayi mata, "Wai ni yarinyar nan zata d'aga hannu ta mara? Har tana fad'a min wai me zatayi da Asad a fad'a masa shi da ya nace mata ya daina zuwa inda take?. Ranki ya dad'e meyasa Asad zai mana haka dan Allah? Kinga yarinyar kuwa?; ai duk yadda kike musalta munin ta ya wuce haka wallahi. kaf unguwar gidan su yafi na kowa lalacewa, gaskiya Asad bai kyauta mana ba wannan cin mutunci ne a gare mu gabad'aya."
Ran Mama ya sake b'aci ta girgiza kai tace, "Ta mare ki!, lallai yarinyar nan tana buk'atar babban mataki ba k'arami ba. Zan yi maganin abun da gaggawa bazan d'auki wannan cin kashin ba, k'aryar Asad wallahi babu shi babu ita dole ya rabu da ita matuk'ar yana son zaman lafiya. Ina shi ina wannan yarinyar?" Ta fad'a tana dafe kai cikin zallar takaici.
"Ai kuwa ranki ya dad'e bazai rabu da ita ba, Gwara ma mahaifiyata ta dajna tunanin hakan dan bazai yau ba" Aliyu ya fad'a yana shigowa ciki yana kallon su.
Mum ta kalle shi tace, "Haba Aliyu! meyasa zaka ce haka?." Yace, "To abinda yake zahiri na fad'a ai Mum, kuna nan kuna tunanin kun d'auki mataki kunyi maganin ta shi kuma yana can yaje gidan su ya d'auke su da kansa ya kaisu asibiti an musu maganin ciwon da suka ji ya mayar dasu d'aya daga cikin guest house d'in sa, yanzu maganar da nake suna cikin gida mai a.c da TV kamar gidan ki." A fusace Mama ta tace, "da gaske kake ko da wasa Aliyu?."
"Ni na isa nayi wasa da mahaifiyata? Abinda na fad'a gaskiya ne bazan yiwa Mamana k'arya ba."
"Wai ke meye haka ne? Ina baki hak'uri kina sake d'aga min murya kina fad'ar duk abinda yazo bakin ki?, wani dalili kawai ya saka nake tsaye a gaban ki ina baki hak'uri amma badan shi ba bazan zo inda kuke bama balle ki samu bakin fad'a min abinda kike so. Na fad'a miki kuyi hak'uri zaku ji abinda ya jawo hakan wanda ban sani ba shima wanda akayi dukan dan shi bai sani ba, meyasa kike haka ne?" Ya fad'a cikin fad'a yana kallon ta ransa a b'ace. Zata kuma magana Baba yace, "Muna so muji dalilin dan gaskiya sai maganar nan taje kunnen mahaifin ku sai naji dalilin dukan da aka yiwa iyalai na har cikin gida."
"Firstly ku fara ganin likita a duba lafiyar ku, please Baba kuzo muje" Hydar ya sake fad'a yana kallon Baba. Rauda ta kalli Asad da idanun sa yake yawo a kanta amma in baka fahimta ba baza kace ita yake kallo ba taja dogon tsaki tace, "Wanda akayi dan shi d'in yana tsaye k'ikam shi bazai bada hak'uri ba sabida bamu kai ya bamu hak'uri ba an dake mu an daki banza kenan, to wallahi sai na d'auki mataki ina k'yale komai banda a tab'a min iyayena." D'auke kai yayi daga kanta Baba ya kalle ta yace, "Ya isa haka Rauda bana son sake jin bakin ki, ke Rahma tashi mu taimaka mata ta tashi aje asibitin."
Tare da Baba suka fita Rahma da Inna suka fito da Umma da Rauda suka shiga bayan mota Baba ma ya shiga Hydar ya shiga mazaunin driver dan yasan Asad bazai iya tuk'i ba ya ja motar suka tafi asibiti. Babu wanda yake magana a cikin su har suka je asibitin ya saka aka duba su aka sake gyara ciwon hannu Umma aka sake wanke ciwukan fuskar su duk da ba masu yawa bane ba. A d'akin da suke suna hutawa bayan an gama Umma taji dad'in jikin ta su Hydar sunje sun dawo Asad ya kalli Umma yace, "kiyi hak'uri Mama."
Umma tace, "To ya zanyi in ba hak'urin ba?, babu komai." Hydar yace, "Baba zaku koma wani gidan daman kafin a gama gyara wancan zan kai ku yanzu suma wad'ancan zan koma na kai su gidan, in kawai abinda kuke da buk'ata sai a d'auko muku." Baba yace, "to sai muje tare in yaso akwai k'anwar Rauda nasan zuwa yanzu ta dawo daga makaranta sai ta d'auko musu abinda zata d'auko." Rauda Hydar ya kalla da take kallon wani wajan daban ya kalli Asad da yake a tsaye baice komai ba shima ya d'auke kansa.
"Baba muje" Asad ya fad'a yana kallon su suka tashi suka fito zuwa inda motar take suka shiga suka tafi. Kusa da unguwar su suka tsaya jikin wani gida babba flat mai maroon d'in gate da maroon d'in fenti yayi kyau sosai kamar sabo dan kana gani kasa ba'a zama a cikin sa kawai yana ajjiye ne. Asad ya fito Hydar ma ya fito suka cewa Baba shima ya fito.
Gidan suka shiga Jim kad'an suka fito Baba yace, "Kuzo muje ciki." Umma ce ta fita Rauda kam k'in fitowa tayi Baba yace, "baza ki fito bane ba?." Ta kalli Baba zuciyar ta kamar ana tafasa ta sabida b'acin rai tace, "Zan fito daga baya." Shi da Umma suka shiga gidan ta bisu da kallo tana kiyasta adadin matakin da zata d'auka a zuciyar ta.
Hydar ne ya shiga gaban motar ya zauna bai kalle ta bayace, "ki ajjiye abinda kike ji dashi a kanki ki fahimci abinda zan fad'a miki yanzu. Ina so ki fahimci abun dakyau kiyi tunanin kalaman da suka fad'a miki akan Asad ki gano me hakan yake nufi." Shiru tayi dan har lokacin a fusace take kafin ta girgiza kai tace, "A yanayin maganar su yayi kama da b'atan kai sukayi suna so suje wajan wacce take sonsa ko dai abinda yayi kama da haka." Hydar yace, "good girl. Ba b'atan kai sukayi ba Rauda tabbas kece."
"Nice me?."
"Kece wacce Allah ya d'orawa Asad k'aunar ta a zuciyar sa!."
Gaban Rauda ya fad'i har ta dafe k'irji bata san tayi ba ta kalle shi cikij tsananin bugawar zuciya a firgice tace, "Me kake nufi?."
Hydar ya juyo ya kalle ta yace, "Ina nufin Asad yana sonki yana kuma fatan auren ki dalilin da ya saka wanda basa goyan baya suka fara d'aukar mataki a kanki, dan farawa akayi in maganar ta cigaba tabbas akwai wasu abubuwa a gaba wanda zan iya cewa sunfi wannan. Na zab'i na fad'a miki ne ba tare da ya sani ba dan kisan dalilin da ya saka akayi miki haka." Shiru Rauda tayi ta kasa magana sai zuciyar ta da take bugawa da sauri-sauri tana sake maimaita kalmar yana sonta a zuciyar ta cikin mamaki da tsoro da ya bayyana a gare ta.
"Sona fa kace? Ta yaya zan amince da hakan bayan matsayin sa da nawa akwai banbanci?, har yaushe mukayi had'uwar da zai fara sona?, har yaushe ya sanni? Yaushe ya ganni da zai soni?. Wad'an nan kalaman naka sun sake bani tsoro sun tabbatar min da akwai wani abun da kuke nema dani shiyasa tun yanzu kuka fata bayyanar da nufin ku a gare ni. Shin me nayi muku?." Murmushi Hydar yayi yace, "Inda akwai abinda muke nema dake da tuni mun aiwatar dashi babu wanda ya sani basai anzo yanzu ba. ki tuna abinda Aliyu yayi miki wanda babu wanda ya sani har kawo gobe kinga da munyi niya zamu iya aikata abinda yafi haka babu wanda yasan mune muka aikata, in munso har ranki zamu iya d'auka babu wanda sai san mune to a kan me dan muna da wata manufa a kanki sai biyo ta wannan hanyar?. In muna da manufa a kan ki bazan tankare ki da wannan maganar ba domin furta tama ba ga ko wacce mace ya dace ba sai wacce ta isa, ke kin san su waye mu basai an fad'a miki ba." Kalaman sa sun shige ta sosai bakin ta ya mutu murus ta kasa furta komai domin ta tabbatar da abinda yace gaskiya da akwai manufar da suke da ita baza su tunkare ta ba, kallon window tayi zuciyar ta na zillo a lokacin Asad yazo wajan shida Baba.
Baba ya bud'e mata yace, "fito ki huta zamu jemu tawo da sauran." Jikinta ya mutu Baba ya rik'o ta suka shiga cikin gidan da ta kasa kallon sa sabida tunanin abinda aka fad'a mata ya tsaya mata a zuciya kamar an soka mata mashi a zuciyar ta haka take ji. Gida ne babba sosai mai babban ma'ajiyar mota sai babban tsakar gida sai kuma k'ofa guda uku a tsakar gidan. Guda d'aya suka shiga sai gasu a falo babba mai kyau wanda babu abinda babu a cikin sa har da a.c da duk wani abun buk'ata akwai shi a falon ya zaunar da ita ya koma.
Basu jima ba suka dawo dasu Inna bayan sun d'auko kayan sawa da abin buk'ata suka shiga ciki Baba ya tsaya yace ya kalle su, "To mun gode muku Allah ya saka da alkhairi, kunyi bakin k'okarin ku akan mu badan ku ba da bamu san inda zamu je mu zauna ba. amma duk da haka inaso maganar nan tazo gaban mai martaba." Hydar yace, "Kar ka damu Baba mu da kanmu zamu sanar masa baza a bar maganar ba in sha Allah. Za'a kawo abinci yanzu." Baba ya amsa ya shiga ciki suma suka shiga motar Hydar ya fincike ta zuwa gida.
A can gida kuwa Mum tana wajan Mama ranta a b'ace take zayyanawa Mama abinda ya faru tana had'awa da k'arya akan abinda Rauda tayi mata, "Wai ni yarinyar nan zata d'aga hannu ta mara? Har tana fad'a min wai me zatayi da Asad a fad'a masa shi da ya nace mata ya daina zuwa inda take?. Ranki ya dad'e meyasa Asad zai mana haka dan Allah? Kinga yarinyar kuwa?; ai duk yadda kike musalta munin ta ya wuce haka wallahi. kaf unguwar gidan su yafi na kowa lalacewa, gaskiya Asad bai kyauta mana ba wannan cin mutunci ne a gare mu gabad'aya."
Ran Mama ya sake b'aci ta girgiza kai tace, "Ta mare ki!, lallai yarinyar nan tana buk'atar babban mataki ba k'arami ba. Zan yi maganin abun da gaggawa bazan d'auki wannan cin kashin ba, k'aryar Asad wallahi babu shi babu ita dole ya rabu da ita matuk'ar yana son zaman lafiya. Ina shi ina wannan yarinyar?" Ta fad'a tana dafe kai cikin zallar takaici.
"Ai kuwa ranki ya dad'e bazai rabu da ita ba, Gwara ma mahaifiyata ta dajna tunanin hakan dan bazai yau ba" Aliyu ya fad'a yana shigowa ciki yana kallon su.
Mum ta kalle shi tace, "Haba Aliyu! meyasa zaka ce haka?." Yace, "To abinda yake zahiri na fad'a ai Mum, kuna nan kuna tunanin kun d'auki mataki kunyi maganin ta shi kuma yana can yaje gidan su ya d'auke su da kansa ya kaisu asibiti an musu maganin ciwon da suka ji ya mayar dasu d'aya daga cikin guest house d'in sa, yanzu maganar da nake suna cikin gida mai a.c da TV kamar gidan ki." A fusace Mama ta tace, "da gaske kake ko da wasa Aliyu?."
"Ni na isa nayi wasa da mahaifiyata? Abinda na fad'a gaskiya ne bazan yiwa Mamana k'arya ba."