Sashe 14
Kwantan Bauna Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Hajiya tace, "wacece ita?, a ina take?, meye alaqar mu da ita...?."
Waziri yayi murmushi yace, "kamar yadda na fad'a miki zaki santa in lokacin yazo amma banda yanzu, ki cigaba da zuba idanu tabbas a kwanakin nan za'a wayi gari ace azo a fitar da gawar Asad, ki rubuta ki ajjiye na tabbatar da wannan" yana gama fad'ar hakan ya yanke wayar ba tare da ya jira yaji me zata ce ba tabi wayar da kallo zuciyar ta na hasaso mata Master planer amma ta kasa gane wacece.................
*KWANTAN ƁAUNA*
FitattuBiyar 2023.
©️ *Nana Haleema.*
*Book 1*
*007.*
Bayan sallar juma'a aka samu kiran gaggawa daga mai martaba duka iyalan gidan hatta matan da suke gidan mazajen su sai da aka kira su aka taru a fadar cikin gida duk wani da ya kasan jini a gidan sai da aka kira shi. Dukkan su suna zaune ana sauraren abinda mai martaba zaice kowa yayi mamakin kiran.
A kamalance da k'asaita da zallar nutsuwa da hikima ya fara fad'in, "kamar yarda na saka a kira ku nasan da yawan ku kuna tunanin lafiya akayi kiran gaggawa haka kasancewar bai tab'a faruwa ba. Ba wani abun bane an kira ku ne akan murabus da nace zanyi a d'ora Asad." Kallon kallo aka shiga yi dukka mutanen wajan gaban su na fad'uwa matuk'a burin kowa yaji k'arshen maganar.
"Babu batun ta a yanzu mu janye, amma nan da wasu kwanaki maganar zata dawo matuk'ar ina raye kuma abinda nace baza'a canja shi ba, in kunga abinda na fad'a bai faru ba ku tabbatar k'asa ta rufe fuska ta." Shiru fadar take ko masu kirari babu kasancewar magana ce ta cikin gida su kad'ai babu damar magana kuma sai ya bada dama. Fuskokin mutanen dake wajan zaka kalla zaka hango zallan farin ciki akan abinda yace, fuskar Mama ce kawai a d'aure cikin akasin farin ciki amma bata ce komai ba.
"Bana son na sake jin wata magana akan wannan na yiwa tufkar hanci, in lokaci yayi komai zai bayyana amma banda yanzu." Nan ma shiru suka kuma yi kafin yace, "Akwai wanda yake da magana a cikin kuz?." Shiru akayi babu wanda yace komai sai daga baya babar y'a kaf gidan mai Maimuna wacce taci sunan mahaifiyar mai martaba ake kiran ta da Mummy tace, "Allah yaja da zamanin mahaifin mu, Allah ya kare mahaifin mu a duk inda yake. Hukuncin mai martaba shine hukunci a ko wanne lokaci, babu mai magana a cikin mu."
Kai ya girgiza kafin yace, "Kowa zai iya tafiya." Kai k'asa sukayi da kansu a tare dukkan su suka furta, "A tashi lafiya." Dukkan su suka fita kowa ya nufi b'angaren sa zuciyar kowa fari kar sab'anin Mama da take cikin mayuwacin hali.
Tunda ta shiga b'angaren ta take zagaye hankalin ta a tashe ta matuk'a ta kasa zama sai kai kawo take, ta d'auki waya hannu na rawa ta kira Sadiya tana d'auka tace, "Sadiya akwai matsala babba."
Daga can b'angaren tace, "Ranki ya dad'e me ya faru?."
"Mai martaba ya janye batun murabus d'in sa haka kawai babu wani dalili."
"Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un, Ranki ya dad'e munyi sake gaskiya, duk yadda akayi wani abun aka yiwa mai martaba kuma ya shiga jikin sa. In fulani zata tuna akwai wanda zasu shiga su fita wajan ganin an tarwatsa mana abinda muka saka a gaba."
"Shiyasa nace miki ina buk'atar zuwa Kano, dole ne na shiga garin Kano a kwanakin nan, babu wanda ya isa ya shiga tsakanina da mulkin Asad, babu shi ko waye" tana fad'a ta yanke wayar hannun ta na rawa ta kira Asad.
Yana zaune yaga kiran ta daman yasan sai Mama ta neme shi ya d'auki wayar baiyi magana ba ya sauke daga kunnen sa ya tashi ya tafi b'angaren nata, can ciki ya shiga inda ya kasance babu mai shiga sai su yana shiga kafin ma yayi magana tace, "a tafiyar da kuka yi dashi me kuka tattauna har ya canja shawara lokaci guda?." Ya d'ago ido kamar zaiyi magana sai ya fasa ganin hakan sai ranta ya sake ya b'aci tace, "bazan lamunci wannan shirun naka ba Asad! Ka fad'a min kaine kace masa baka ra'ayi?."
Kai ya girgiza alamun a'a kafin yace, "wallahil azim Mama bamuyi magana irin wannan dashi ba, ki amince dani bazan yi k'arya dan na kare kaina ba" ya fad'a a sanyaye yana kallon k'asa. remote ta d'auka tayi jifa dashi ya tarwatse a wajan tana wuci tace, "koma dai meye Asad baka isa kak'i karb'ar mulkin nan ba indai ina da rai, Asad kaine zaka mulki garin nan babu wanda ya isa ya shiga tsakanin ku da mulkin nan, dole ka cika min burin." tana fad'in hakan ta wuce zuwa d'akin ta tana fad'in, "A shirya min tafiya gobe zan wuce Kano." Kai ya girgiza sai da ta shiga ciki sannan ya juya ya fita zuciyar sa gabad'aya babu dad'i ko kad'an.
A falon Hajiya iyalan ta zagaye suke da ita maza da mata y'ay'an ta kowa ka kalla zaka hango zallar farin ciki a tare dashi barin ma ita da take ta murmushi ita kad'ai alamun hak'ar ta ta cimma ruwa. Wayar ta da taji tana k'ara ya sakata ta mik'e ta shiga d'aki ta barsu a wajan ta amsa wayar tace, "Abu kamar wasa yana ta zama gaske, sai ga mai martaba da kansa ya janye batun nan."
Waziri yace, "Na sha fad'a miki ki kwantar da hankalin ki komai fa a hannun mu yake amma duk sai ki bi damu kan ki."
Murmushi tayi mai sauti tace, "yanzu meye abu na gaba?."
"Master planer tace mu had'u dake waje d'aya zamu tattauna."
"Yaushe zaka shigo to?."
"Zan shigo zuwa dare." Murmushi tayi tace, "Allah ya kai mu" tana fad'ar hakan ta yanke wayar zuciyar ta cike da farin ciki a bayyane.
*◇*
Amaryar Sarki Hajiya Rukayya wacce ake kira da Ammi a gidan itama tana zaune da nata iyalan babban d'an ta namiji mai suna Nazif a shekaru bazai wuce shekara sha hud'u ba ya kalle ta yace, "Ammi ni na rasa ganewa kamar kina goyan bayan sarautar Asad?." Murmushi tayi ta kalle su dukkan su tace, "To meye nawa da zanki goyan baya Nazif? Kai dai a musulunce baka kai minzalin jan ragamar al'umma ba to meye abin tayar da jijiyoyin wuya akan hakan?."
Babbar y'ar ta mace mai suna Zainab wacce ake kira Yaya Zainab tace, "kin huta Ammi, koma waye zai mulki garin nan mudai burin mu ya kasance alkahiri a gare mu da kuma garin." Wacce take bin ta tace, "Shine kawai fatan mu amma ni banga abin tayar da hankali a lamarin nan ba. Asad kuma kaf gidan nan babu mai kirkin sa kawai shi rashin maganar sa ce illa amma kowa yasan halin sa ga san y'an uwan sa baya lakari da yanayin gidan namu kowa na sa ne. Duk da Mama bata son yana sauraren mu amma shi ko a jikin sa, ga ilimi da kud'i a hannun sa."
Ammi tace, "Allah ya kyauta" duk suka amsa da amin suka cigaba da hirar su gabad'aya maganar mulkin katagum bata gaban su su kam.
Hydar da Aliyu da kuma Asad ne a zaune a b'angaren su babu wanda yake yiwa d'an uwan sa magana dukkan su waya ce a hannun su suna dannawa hankalin su a kwance, waya Hydar ya d'auka ya kira Dr ya sake tambayar sa jikin Rauda ya tabbatar masa da komai daidai. Asad ya dafe kansa da yake mugun ciwo yana yatsine fuskar sa. Hydar ya kalle shi yace, "Deaf ya dai?." Yatsine fuska yayi yace, "nothing" yana fad'a kawai ya tashi ya shiga d'akin sa ya kulle k'ofar ya zaga baya ya bud'e varanda yana kallon harabar gidan ana ta hidima da shige da fice.
Allah ya sani baya k'aunar mulkin da ake son k'ak'aba masa ga jifa da yake sha tun daga fara maganar sarautar nan yake ganin mutane da yawa wanda baiyi tunani ba a mafarkin sa ina ga an bashi sarautar?. Burin sa kasancewa a madina ba'a Nigeria ba a can yake burin yin aiki kuma burin sa ya cika amma Mama ta hana.
Lumshe idanun sa yayi mafarkin da yayi a jiya ya dawo masa kansa ya wara idanun sa yana k'ok'arin tuno fuskar yarinyar da ya gani ta taimake sa a mafarkin amma ya kasa, furzar da iska yake yi jikin sa na kyarma hankalin sa ya tashi ji yake gidan gabad'aya yana juya masa sam baya son zama a cikin sa, duk yadda yaso daurewa kasawa yayi ya fito ya d'auki makullin mota ya fita har lokacin Hydar da Ali suna zaune.
Hydar ma fita yayi aka bar Aliyu a zaune yana ganin fitar su ya mik'e ya shiga d'akin Asad yana k'arewa d'akin kallo kamar yana neman wani abun a ciki. Babba ne d'akin sosai komai fari ne a d'akin hatta tiles d'in d'akin fari ne labulaye carpet komai fari ne a d'akin, fari kuma tass babu alamun daud'a a tare da ko ina sai khamshi da yake yi. tab'e baki yake yana girgiza kai yana hasahen abinda ya kamata yayi a d'akin kafin ya fita daga d'akin.
Hydar yana fita asibitin ya koma a lokacin Umma ce kawai a ciki ya shiga da sallama ta amsa tana kallon sa yace, "Sannu Mama, ya mai jikin?."
"Da sauk'i gata bata farka ba har yanzu." Kallon ta yake yi ya runtse idanu ya rasa dalilin da ya saka gaban sa yake fad'uwa in ya kalli fuskar ta sai yaji wani abun yana shigar sa ya rasa meye.
"Allah zai bata lafiya."
"In sha Allah, ban san sunan ka ba."
Murmushi yayi kad'an yace, "Aliyu suna na" ya fad'a yana ajjiye kud'i a gefen gadon ta ya fita bai kuma cewa komai ba. Kallon kud'in take yi ganin su da yawa a zahiri bata tab'a ganin mai yawan su ba balle kuma ta rik'e ta yunk'ura zata d'auka kenan Baba ya shigo.
Idanun sa akan kud'in suka fad'a ya k'araso yana fad'in, "Ikon Allah wannan abin arzukin fa" ya fad'a yana k'arasowa wajan ya d'auki kud'in yana kallo.
Waziri yayi murmushi yace, "kamar yadda na fad'a miki zaki santa in lokacin yazo amma banda yanzu, ki cigaba da zuba idanu tabbas a kwanakin nan za'a wayi gari ace azo a fitar da gawar Asad, ki rubuta ki ajjiye na tabbatar da wannan" yana gama fad'ar hakan ya yanke wayar ba tare da ya jira yaji me zata ce ba tabi wayar da kallo zuciyar ta na hasaso mata Master planer amma ta kasa gane wacece.................
*KWANTAN ƁAUNA*
FitattuBiyar 2023.
©️ *Nana Haleema.*
*Book 1*
*007.*
Bayan sallar juma'a aka samu kiran gaggawa daga mai martaba duka iyalan gidan hatta matan da suke gidan mazajen su sai da aka kira su aka taru a fadar cikin gida duk wani da ya kasan jini a gidan sai da aka kira shi. Dukkan su suna zaune ana sauraren abinda mai martaba zaice kowa yayi mamakin kiran.
A kamalance da k'asaita da zallar nutsuwa da hikima ya fara fad'in, "kamar yarda na saka a kira ku nasan da yawan ku kuna tunanin lafiya akayi kiran gaggawa haka kasancewar bai tab'a faruwa ba. Ba wani abun bane an kira ku ne akan murabus da nace zanyi a d'ora Asad." Kallon kallo aka shiga yi dukka mutanen wajan gaban su na fad'uwa matuk'a burin kowa yaji k'arshen maganar.
"Babu batun ta a yanzu mu janye, amma nan da wasu kwanaki maganar zata dawo matuk'ar ina raye kuma abinda nace baza'a canja shi ba, in kunga abinda na fad'a bai faru ba ku tabbatar k'asa ta rufe fuska ta." Shiru fadar take ko masu kirari babu kasancewar magana ce ta cikin gida su kad'ai babu damar magana kuma sai ya bada dama. Fuskokin mutanen dake wajan zaka kalla zaka hango zallan farin ciki akan abinda yace, fuskar Mama ce kawai a d'aure cikin akasin farin ciki amma bata ce komai ba.
"Bana son na sake jin wata magana akan wannan na yiwa tufkar hanci, in lokaci yayi komai zai bayyana amma banda yanzu." Nan ma shiru suka kuma yi kafin yace, "Akwai wanda yake da magana a cikin kuz?." Shiru akayi babu wanda yace komai sai daga baya babar y'a kaf gidan mai Maimuna wacce taci sunan mahaifiyar mai martaba ake kiran ta da Mummy tace, "Allah yaja da zamanin mahaifin mu, Allah ya kare mahaifin mu a duk inda yake. Hukuncin mai martaba shine hukunci a ko wanne lokaci, babu mai magana a cikin mu."
Kai ya girgiza kafin yace, "Kowa zai iya tafiya." Kai k'asa sukayi da kansu a tare dukkan su suka furta, "A tashi lafiya." Dukkan su suka fita kowa ya nufi b'angaren sa zuciyar kowa fari kar sab'anin Mama da take cikin mayuwacin hali.
Tunda ta shiga b'angaren ta take zagaye hankalin ta a tashe ta matuk'a ta kasa zama sai kai kawo take, ta d'auki waya hannu na rawa ta kira Sadiya tana d'auka tace, "Sadiya akwai matsala babba."
Daga can b'angaren tace, "Ranki ya dad'e me ya faru?."
"Mai martaba ya janye batun murabus d'in sa haka kawai babu wani dalili."
"Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un, Ranki ya dad'e munyi sake gaskiya, duk yadda akayi wani abun aka yiwa mai martaba kuma ya shiga jikin sa. In fulani zata tuna akwai wanda zasu shiga su fita wajan ganin an tarwatsa mana abinda muka saka a gaba."
"Shiyasa nace miki ina buk'atar zuwa Kano, dole ne na shiga garin Kano a kwanakin nan, babu wanda ya isa ya shiga tsakanina da mulkin Asad, babu shi ko waye" tana fad'a ta yanke wayar hannun ta na rawa ta kira Asad.
Yana zaune yaga kiran ta daman yasan sai Mama ta neme shi ya d'auki wayar baiyi magana ba ya sauke daga kunnen sa ya tashi ya tafi b'angaren nata, can ciki ya shiga inda ya kasance babu mai shiga sai su yana shiga kafin ma yayi magana tace, "a tafiyar da kuka yi dashi me kuka tattauna har ya canja shawara lokaci guda?." Ya d'ago ido kamar zaiyi magana sai ya fasa ganin hakan sai ranta ya sake ya b'aci tace, "bazan lamunci wannan shirun naka ba Asad! Ka fad'a min kaine kace masa baka ra'ayi?."
Kai ya girgiza alamun a'a kafin yace, "wallahil azim Mama bamuyi magana irin wannan dashi ba, ki amince dani bazan yi k'arya dan na kare kaina ba" ya fad'a a sanyaye yana kallon k'asa. remote ta d'auka tayi jifa dashi ya tarwatse a wajan tana wuci tace, "koma dai meye Asad baka isa kak'i karb'ar mulkin nan ba indai ina da rai, Asad kaine zaka mulki garin nan babu wanda ya isa ya shiga tsakanin ku da mulkin nan, dole ka cika min burin." tana fad'in hakan ta wuce zuwa d'akin ta tana fad'in, "A shirya min tafiya gobe zan wuce Kano." Kai ya girgiza sai da ta shiga ciki sannan ya juya ya fita zuciyar sa gabad'aya babu dad'i ko kad'an.
A falon Hajiya iyalan ta zagaye suke da ita maza da mata y'ay'an ta kowa ka kalla zaka hango zallar farin ciki a tare dashi barin ma ita da take ta murmushi ita kad'ai alamun hak'ar ta ta cimma ruwa. Wayar ta da taji tana k'ara ya sakata ta mik'e ta shiga d'aki ta barsu a wajan ta amsa wayar tace, "Abu kamar wasa yana ta zama gaske, sai ga mai martaba da kansa ya janye batun nan."
Waziri yace, "Na sha fad'a miki ki kwantar da hankalin ki komai fa a hannun mu yake amma duk sai ki bi damu kan ki."
Murmushi tayi mai sauti tace, "yanzu meye abu na gaba?."
"Master planer tace mu had'u dake waje d'aya zamu tattauna."
"Yaushe zaka shigo to?."
"Zan shigo zuwa dare." Murmushi tayi tace, "Allah ya kai mu" tana fad'ar hakan ta yanke wayar zuciyar ta cike da farin ciki a bayyane.
*◇*
Amaryar Sarki Hajiya Rukayya wacce ake kira da Ammi a gidan itama tana zaune da nata iyalan babban d'an ta namiji mai suna Nazif a shekaru bazai wuce shekara sha hud'u ba ya kalle ta yace, "Ammi ni na rasa ganewa kamar kina goyan bayan sarautar Asad?." Murmushi tayi ta kalle su dukkan su tace, "To meye nawa da zanki goyan baya Nazif? Kai dai a musulunce baka kai minzalin jan ragamar al'umma ba to meye abin tayar da jijiyoyin wuya akan hakan?."
Babbar y'ar ta mace mai suna Zainab wacce ake kira Yaya Zainab tace, "kin huta Ammi, koma waye zai mulki garin nan mudai burin mu ya kasance alkahiri a gare mu da kuma garin." Wacce take bin ta tace, "Shine kawai fatan mu amma ni banga abin tayar da hankali a lamarin nan ba. Asad kuma kaf gidan nan babu mai kirkin sa kawai shi rashin maganar sa ce illa amma kowa yasan halin sa ga san y'an uwan sa baya lakari da yanayin gidan namu kowa na sa ne. Duk da Mama bata son yana sauraren mu amma shi ko a jikin sa, ga ilimi da kud'i a hannun sa."
Ammi tace, "Allah ya kyauta" duk suka amsa da amin suka cigaba da hirar su gabad'aya maganar mulkin katagum bata gaban su su kam.
Hydar da Aliyu da kuma Asad ne a zaune a b'angaren su babu wanda yake yiwa d'an uwan sa magana dukkan su waya ce a hannun su suna dannawa hankalin su a kwance, waya Hydar ya d'auka ya kira Dr ya sake tambayar sa jikin Rauda ya tabbatar masa da komai daidai. Asad ya dafe kansa da yake mugun ciwo yana yatsine fuskar sa. Hydar ya kalle shi yace, "Deaf ya dai?." Yatsine fuska yayi yace, "nothing" yana fad'a kawai ya tashi ya shiga d'akin sa ya kulle k'ofar ya zaga baya ya bud'e varanda yana kallon harabar gidan ana ta hidima da shige da fice.
Allah ya sani baya k'aunar mulkin da ake son k'ak'aba masa ga jifa da yake sha tun daga fara maganar sarautar nan yake ganin mutane da yawa wanda baiyi tunani ba a mafarkin sa ina ga an bashi sarautar?. Burin sa kasancewa a madina ba'a Nigeria ba a can yake burin yin aiki kuma burin sa ya cika amma Mama ta hana.
Lumshe idanun sa yayi mafarkin da yayi a jiya ya dawo masa kansa ya wara idanun sa yana k'ok'arin tuno fuskar yarinyar da ya gani ta taimake sa a mafarkin amma ya kasa, furzar da iska yake yi jikin sa na kyarma hankalin sa ya tashi ji yake gidan gabad'aya yana juya masa sam baya son zama a cikin sa, duk yadda yaso daurewa kasawa yayi ya fito ya d'auki makullin mota ya fita har lokacin Hydar da Ali suna zaune.
Hydar ma fita yayi aka bar Aliyu a zaune yana ganin fitar su ya mik'e ya shiga d'akin Asad yana k'arewa d'akin kallo kamar yana neman wani abun a ciki. Babba ne d'akin sosai komai fari ne a d'akin hatta tiles d'in d'akin fari ne labulaye carpet komai fari ne a d'akin, fari kuma tass babu alamun daud'a a tare da ko ina sai khamshi da yake yi. tab'e baki yake yana girgiza kai yana hasahen abinda ya kamata yayi a d'akin kafin ya fita daga d'akin.
Hydar yana fita asibitin ya koma a lokacin Umma ce kawai a ciki ya shiga da sallama ta amsa tana kallon sa yace, "Sannu Mama, ya mai jikin?."
"Da sauk'i gata bata farka ba har yanzu." Kallon ta yake yi ya runtse idanu ya rasa dalilin da ya saka gaban sa yake fad'uwa in ya kalli fuskar ta sai yaji wani abun yana shigar sa ya rasa meye.
"Allah zai bata lafiya."
"In sha Allah, ban san sunan ka ba."
Murmushi yayi kad'an yace, "Aliyu suna na" ya fad'a yana ajjiye kud'i a gefen gadon ta ya fita bai kuma cewa komai ba. Kallon kud'in take yi ganin su da yawa a zahiri bata tab'a ganin mai yawan su ba balle kuma ta rik'e ta yunk'ura zata d'auka kenan Baba ya shigo.
Idanun sa akan kud'in suka fad'a ya k'araso yana fad'in, "Ikon Allah wannan abin arzukin fa" ya fad'a yana k'arasowa wajan ya d'auki kud'in yana kallo.