Sashe 99
Gobe Na Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Da tunanin Abraham na shiga gida, rokon da yai min ya karya min zuciya, indai har mutum zai hada ka da Annabi ya roki abunda kasan zaka iya masa anya ya dace na tsallake? Ko da musulunci da yace zai yi? Ko dan ya tuba da gaske? Sai dai me? Har gobe bana son jin wani kalami daga bakinsa bana kaunar ganinsa kuma bana tunanin zan koyi soyayyarsa balle har na iya kamar yadda yake tunani.
To me zanyi? Na yafe masa be bar ni ba, na san idan ma na daina kulashi hakan ba zai wadatar domin kuwa ba kyaleni zai yi ba, to ko dai na kai kararsa a wani gurin ne na fallasa sirrinsa?
A hankali na sauke ajiyar zuciya ina ta tunanin mafita, hakika ina neman abokin shawara wata zuciyar na nace min na fadawa Mama ta wani bangaren kuma ina jin tsoron yadda hankalinta zai tashi, gashi daman ba lafiya ta isheta ba ga kuma rashin mijinta ina ganin kamar idan na labarta mata hakan zai iya janyo mata matsala, amman ai bani da abokiyar shawara sai ita bana da wanda ya fita, ko ba komai na san dole zata tambayi waye Abraham kamar yadda ta bukata dazun. Har na unkura zan tashi da zimmar shiga har uwar daka na labarta mata komai sai muk ji sallamar mata biyu tun kan na ga mahaifiyar Aminu na gane cewar ita ce saboda yanayin maganarta.
Bayan Inna ta amsa musu suka nufo falon Mama suna ta doka sallama, ni da Mama dake can cikin daki muka hada baki gurin amsa musu, komawa nai na zauna Mama kuma ta fito daga dakin sanye da Hijabinta. Kallo daya zaka yi ma Hajiya ka fahimce cewar tana cikin tashin hankali, daman can haka take Allah ya zuba mata son yaya musammn Aminu bata kaunar abunda ya same shi, yana daya daga cikin dalilin daya saka ko fada mukai ko na kai kararsa sai ni ta ba ni laifi.
Sama sama suka gaisa da Mama har take mata ya karin hakuri, amman idonta na kaina tana min wani kallo kamar na mamaki.
“Halima gurinki muka zo”
“To Hajiya Allah yasa ba laifi nai ba”
Na fada ina kallonta sai ta dan tabe baki tana murmushin da ni kaina na san be kai zuci ba.
“Akan maganar Aminu ne da kika sa aka kama, yanzu abunda kika yi kin yi daidai kenan? Ko ba komai ai uban yayanki ne komai Aminu ya lalace sai kin fi kowa jin ciwo, haka komai Aminu yai arziki sai kin fi kowa jindadi, saboda yayan da ke tsakani, yanzu daidai ne ki saka sojoji su kama shi bayan kin san ba za su masa da sauki ba?”
Da fari murmushi nai kamin mamaki ya biyo baya ya na jin kalamanta na rainon waya da take akai.
“Aminu ba ni yai fada ba, kuma ba ni na saka a kama shi ba”
“To bakinku dai daya kenan? Shi yace ba da shi yai fada ba da ke yai, ke ma kin ce haka, yanzu ina gaskiyar magana a nan...”
Mama ta tari numfashinta tana kallona.
“Ba haka zaki ce ba Halimatu, ki fada gaskiyar abunda ya faru, kuna hanya ne na ganku ya fara fada yana kiranta matarsa yana masifa da shi wanda suke taren, sai kuma gashi ya buga kanta da murfi mota a kokarinsa na ya jnyota daga jikin motar mutumen sandiyar haka ya fasa mata goshi dai kina gani a goshinsa, shi kuma wanda suke tare yaji haushi ya saka soja suka kama shi”
“Ah to ya isa ya raba tsakaninsu ne, tun da akwai yaya ai dole ne yai magana da ita, waya san gobe ban da Allah, aka san abunda gaba zata haifar? Ko aurenki yai ya isa ya yanke alakarku ne ai alaka Allah ya riga ya hada Wallahi”
Ba mama kadai ba ni kaina kallonta nake da mamaki, sai masifa take ta inda take shiga ba ta nan take fita ba sai fada take da Ahmad din da baya nan a zatonta so na yake, a raina na ce idan kin isa ki je a gansa ki yi. Matar da suke tare wacce ita mahaifiya ce a gurin Aminu ta dakatar da ita.
“Yanzu dai ba ta wannan muke ba Hajiya, shi bazarawarin naki yace sai kin amince sannan zai saki Aminu, dan haka yanzu ki tashi muje ki fada masa cewar kin yafe”
Kallonta nai wani irin dadi ya lullube ni ko ba komai Ahmad ya mutuntani kuma ya nuna musu cewar ina da muhimmanci ba kamar yadda danta yake wulakanta ni ba.
“Kuje ku fada masa na yafe”
“A a tare zamu tafi ki fada masa, tunda idan munje zai iya cewa sai ya ji ta bakinki ko kuma ki kira wayarsa a yanzu nan ki masa magana”
Hajiyar Aminu ta fada. Bana son na fada musu bana da number su kamar yadda bana son zuwa gidan domin kawai fada masa cewar na amince, ina kokarin yin magana Mama ta tari numfashina
“Halima tashi kuje ki fada masa da bakinki kim yafe”
“To Mama”
Na tashi na shiga ciki, Hijabin dake jikin na canza daga fari zuwa brown dogo har kasa mai gyale sannan na bisu muka fita, ashe har da namiji suke ya tsaya a waje, wanda kanen mahaifin Aminu ne. A motarsa muka shiga ya dauki hanyar gidansu Ahmad, tun da muka shiga motar babu wanda yace uffan har muka isa.
Harabar gidan tana nan da kyauta kamar kullum, ga haske ta ko'ina gwanin sha'awa, musamman bangaren da aka zagaye da fulawoyi an saka wasu kananan gulub sun haska su gwanin sha'awa.
Fita mukai daga motar muka nufi kofar shiga falon Hajiya ta fara knocked, ganin an dade ba a bude kofar ba ta sake yi, nan ma shiru har muka soma gajiya da tsayuwa. Hakan yasa na nufi kofar da zimmar na kwankwasa da karfi ta yadda za su ji wata kila bugawan da Hajiya take basa ji ne, tun da gidan masu kudi komai na su dabam ne. Ina kai hannuna Ahmad ya bude kofar fuska a hade alamar ransa a bacen yake kenan, sai dai muna hada ido sai ya saka min murmushi ko da wasa ba kalli mutanen da muke tare ba sai yai kamar be gansu ba idonsa na kaina ya kara wangale kofar falon.
“Shigo”
Ni na fara shiga sannan suma suka biyo baya, da kansa ya nuna min wata one seater ya ce na zauna, ba musu na zauna ina kallon kanwarsa wacce ke kallona tana dan murmushi.
“Sannunki”
“Yauwa Sannu Halima ko?”
Na gyada mata kai.
“Ya goshin naki?”
Ya tambaya yana kallona.
“Alhamdulillah”
“Siyama kawo mata lemu”
“No ba sai an kawo ba, daman mun zo ne akan maganar Aminu, mahaifiyarsa tace ka ce sai na amince za a sake shi”
“Yes sun miki cilas ne? ”
Mahaifiyar Aminu ta saki baki.
“Ikon Allah wane irin cilas kuma? Akwai fa yara a tsakaninsu yara hudu ai ko ba komai a hakura tun da ba a san abunda gaba zata haifar ba, yara hudu yau a ba wasa bane komai abu ya lalace dole akwai alaka akwai wannan son a tsakani, tun da idan babu shi ba zaki rike masa yaya a hannunki ba”
A iya tunanina mahaifiyar Aminu tana fadar hakan ne saboda Ahmad ya ji cewar ina da yara hudu idan ma be sani ba ya sani, saboda ya fasa aurena ko so na kamar yadda take tunanin so na yake, ta yi hakan ne kawai dan ta muzanta ni idan ma baya son yara sai ya fasa aurena tun da ta san ba duk namiji ke son yaran da ba na shi ba.
Kallon nai zan yi magana Ahmad ya girgiza kai alamar kar na ce komai.
“Kin amince?”
Sai naji kamar bace a a ko dan Hajiyar amman rahamar zuciyata ta hana ni.
“Eh na yafe”
Wayarsa ya dauka ya kira wnda nake kyautata zaton direbansa ne.
“Ga iyayen mutumen nan zasu fito yanzu, kuje tare kamfani ka dauko motarsa then ku wuce AP barack ku karbo shi gurin Faruk”
Yana sauke wayar ya kallesu yace.
“Za ku iya fita direba na jiranku”
A dolen dolen sukai masa godiya har da addu'ar Allah ya saka da alheri.
Suna mikewa tsaye nima na mike sai yai alamar na zauna da hannu, haka kuwa akai sai na zauna din su kuma suka fita.
“Siyama je ki kira Hajiya su gaisa”
“Ow... Owk... Owk.... ”
Ta tashi ta nufi upstairs tana wasa da wayar hannunta.
“Na gode”
Na fada ina kallonsa, sai ya juyo dubansa daga kallon Siyama izuwa gare ni. Kasa nai da kaina ina wasa da yan yatsun hannuna sosai nake son nai masa maganar Abraham domin ina kyautata zaton tsakanin shi da Abdallah ne suke bincike akansa, wanda nake ganin hakan kamar hatsari ne ga rayuwarsu. Ina zaune a gurin Siyama ta sauko tace wai na shigo dakin in ji Hajiya, kamar mai jira na tashi na nufi upstairs din Siyama na shiga dakin nima na shiga sai na zauna a saman kujerar dake gefen windows ina gaisawa da ita tana min sannu da ciwon da na ji, ta tambayi Mama sannan ta dora da ya karin hakuri.
Ban wani dade ba ganin dare na na yi mata sallama na taso na fito daga dakin, Ahmad na tsaye jikin stairs din yana kallon kafafuwana har na sauko.
“Muje na sauke ki”
“No zan hau Napep”
Tabe baki yai.
“Kin fi son Napap kenan da motata okay muje na taka miki”
Tare muka jeru da shi muna kusan isa gate Siyama ta kwala min kira, a gurin muka tsaya har ta iso, ta miko min ledar hannunta.
“Gashi in ji Hajiya”
“Wannan ba tarbiya bace ya zaki kwala mata kira kamar wacce tai sata?”
“To Yaya idan ban daga murya ba kuka fita ita Hajiya ai fada zata min tace ban ba wa Halima, yanzu kuma na bata ka fara min masifa wai ina murya da yawa”
“To ai sai ki kira wayata ko nata ki ce mu jiraki”
“Ina na ga Number ta?”
“Bata number ki”
Ya fada yana kallona sai ta miko min tsadaddiyar wayar.
“Sa min number ki”
To me zanyi? Na yafe masa be bar ni ba, na san idan ma na daina kulashi hakan ba zai wadatar domin kuwa ba kyaleni zai yi ba, to ko dai na kai kararsa a wani gurin ne na fallasa sirrinsa?
A hankali na sauke ajiyar zuciya ina ta tunanin mafita, hakika ina neman abokin shawara wata zuciyar na nace min na fadawa Mama ta wani bangaren kuma ina jin tsoron yadda hankalinta zai tashi, gashi daman ba lafiya ta isheta ba ga kuma rashin mijinta ina ganin kamar idan na labarta mata hakan zai iya janyo mata matsala, amman ai bani da abokiyar shawara sai ita bana da wanda ya fita, ko ba komai na san dole zata tambayi waye Abraham kamar yadda ta bukata dazun. Har na unkura zan tashi da zimmar shiga har uwar daka na labarta mata komai sai muk ji sallamar mata biyu tun kan na ga mahaifiyar Aminu na gane cewar ita ce saboda yanayin maganarta.
Bayan Inna ta amsa musu suka nufo falon Mama suna ta doka sallama, ni da Mama dake can cikin daki muka hada baki gurin amsa musu, komawa nai na zauna Mama kuma ta fito daga dakin sanye da Hijabinta. Kallo daya zaka yi ma Hajiya ka fahimce cewar tana cikin tashin hankali, daman can haka take Allah ya zuba mata son yaya musammn Aminu bata kaunar abunda ya same shi, yana daya daga cikin dalilin daya saka ko fada mukai ko na kai kararsa sai ni ta ba ni laifi.
Sama sama suka gaisa da Mama har take mata ya karin hakuri, amman idonta na kaina tana min wani kallo kamar na mamaki.
“Halima gurinki muka zo”
“To Hajiya Allah yasa ba laifi nai ba”
Na fada ina kallonta sai ta dan tabe baki tana murmushin da ni kaina na san be kai zuci ba.
“Akan maganar Aminu ne da kika sa aka kama, yanzu abunda kika yi kin yi daidai kenan? Ko ba komai ai uban yayanki ne komai Aminu ya lalace sai kin fi kowa jin ciwo, haka komai Aminu yai arziki sai kin fi kowa jindadi, saboda yayan da ke tsakani, yanzu daidai ne ki saka sojoji su kama shi bayan kin san ba za su masa da sauki ba?”
Da fari murmushi nai kamin mamaki ya biyo baya ya na jin kalamanta na rainon waya da take akai.
“Aminu ba ni yai fada ba, kuma ba ni na saka a kama shi ba”
“To bakinku dai daya kenan? Shi yace ba da shi yai fada ba da ke yai, ke ma kin ce haka, yanzu ina gaskiyar magana a nan...”
Mama ta tari numfashinta tana kallona.
“Ba haka zaki ce ba Halimatu, ki fada gaskiyar abunda ya faru, kuna hanya ne na ganku ya fara fada yana kiranta matarsa yana masifa da shi wanda suke taren, sai kuma gashi ya buga kanta da murfi mota a kokarinsa na ya jnyota daga jikin motar mutumen sandiyar haka ya fasa mata goshi dai kina gani a goshinsa, shi kuma wanda suke tare yaji haushi ya saka soja suka kama shi”
“Ah to ya isa ya raba tsakaninsu ne, tun da akwai yaya ai dole ne yai magana da ita, waya san gobe ban da Allah, aka san abunda gaba zata haifar? Ko aurenki yai ya isa ya yanke alakarku ne ai alaka Allah ya riga ya hada Wallahi”
Ba mama kadai ba ni kaina kallonta nake da mamaki, sai masifa take ta inda take shiga ba ta nan take fita ba sai fada take da Ahmad din da baya nan a zatonta so na yake, a raina na ce idan kin isa ki je a gansa ki yi. Matar da suke tare wacce ita mahaifiya ce a gurin Aminu ta dakatar da ita.
“Yanzu dai ba ta wannan muke ba Hajiya, shi bazarawarin naki yace sai kin amince sannan zai saki Aminu, dan haka yanzu ki tashi muje ki fada masa cewar kin yafe”
Kallonta nai wani irin dadi ya lullube ni ko ba komai Ahmad ya mutuntani kuma ya nuna musu cewar ina da muhimmanci ba kamar yadda danta yake wulakanta ni ba.
“Kuje ku fada masa na yafe”
“A a tare zamu tafi ki fada masa, tunda idan munje zai iya cewa sai ya ji ta bakinki ko kuma ki kira wayarsa a yanzu nan ki masa magana”
Hajiyar Aminu ta fada. Bana son na fada musu bana da number su kamar yadda bana son zuwa gidan domin kawai fada masa cewar na amince, ina kokarin yin magana Mama ta tari numfashina
“Halima tashi kuje ki fada masa da bakinki kim yafe”
“To Mama”
Na tashi na shiga ciki, Hijabin dake jikin na canza daga fari zuwa brown dogo har kasa mai gyale sannan na bisu muka fita, ashe har da namiji suke ya tsaya a waje, wanda kanen mahaifin Aminu ne. A motarsa muka shiga ya dauki hanyar gidansu Ahmad, tun da muka shiga motar babu wanda yace uffan har muka isa.
Harabar gidan tana nan da kyauta kamar kullum, ga haske ta ko'ina gwanin sha'awa, musamman bangaren da aka zagaye da fulawoyi an saka wasu kananan gulub sun haska su gwanin sha'awa.
Fita mukai daga motar muka nufi kofar shiga falon Hajiya ta fara knocked, ganin an dade ba a bude kofar ba ta sake yi, nan ma shiru har muka soma gajiya da tsayuwa. Hakan yasa na nufi kofar da zimmar na kwankwasa da karfi ta yadda za su ji wata kila bugawan da Hajiya take basa ji ne, tun da gidan masu kudi komai na su dabam ne. Ina kai hannuna Ahmad ya bude kofar fuska a hade alamar ransa a bacen yake kenan, sai dai muna hada ido sai ya saka min murmushi ko da wasa ba kalli mutanen da muke tare ba sai yai kamar be gansu ba idonsa na kaina ya kara wangale kofar falon.
“Shigo”
Ni na fara shiga sannan suma suka biyo baya, da kansa ya nuna min wata one seater ya ce na zauna, ba musu na zauna ina kallon kanwarsa wacce ke kallona tana dan murmushi.
“Sannunki”
“Yauwa Sannu Halima ko?”
Na gyada mata kai.
“Ya goshin naki?”
Ya tambaya yana kallona.
“Alhamdulillah”
“Siyama kawo mata lemu”
“No ba sai an kawo ba, daman mun zo ne akan maganar Aminu, mahaifiyarsa tace ka ce sai na amince za a sake shi”
“Yes sun miki cilas ne? ”
Mahaifiyar Aminu ta saki baki.
“Ikon Allah wane irin cilas kuma? Akwai fa yara a tsakaninsu yara hudu ai ko ba komai a hakura tun da ba a san abunda gaba zata haifar ba, yara hudu yau a ba wasa bane komai abu ya lalace dole akwai alaka akwai wannan son a tsakani, tun da idan babu shi ba zaki rike masa yaya a hannunki ba”
A iya tunanina mahaifiyar Aminu tana fadar hakan ne saboda Ahmad ya ji cewar ina da yara hudu idan ma be sani ba ya sani, saboda ya fasa aurena ko so na kamar yadda take tunanin so na yake, ta yi hakan ne kawai dan ta muzanta ni idan ma baya son yara sai ya fasa aurena tun da ta san ba duk namiji ke son yaran da ba na shi ba.
Kallon nai zan yi magana Ahmad ya girgiza kai alamar kar na ce komai.
“Kin amince?”
Sai naji kamar bace a a ko dan Hajiyar amman rahamar zuciyata ta hana ni.
“Eh na yafe”
Wayarsa ya dauka ya kira wnda nake kyautata zaton direbansa ne.
“Ga iyayen mutumen nan zasu fito yanzu, kuje tare kamfani ka dauko motarsa then ku wuce AP barack ku karbo shi gurin Faruk”
Yana sauke wayar ya kallesu yace.
“Za ku iya fita direba na jiranku”
A dolen dolen sukai masa godiya har da addu'ar Allah ya saka da alheri.
Suna mikewa tsaye nima na mike sai yai alamar na zauna da hannu, haka kuwa akai sai na zauna din su kuma suka fita.
“Siyama je ki kira Hajiya su gaisa”
“Ow... Owk... Owk.... ”
Ta tashi ta nufi upstairs tana wasa da wayar hannunta.
“Na gode”
Na fada ina kallonsa, sai ya juyo dubansa daga kallon Siyama izuwa gare ni. Kasa nai da kaina ina wasa da yan yatsun hannuna sosai nake son nai masa maganar Abraham domin ina kyautata zaton tsakanin shi da Abdallah ne suke bincike akansa, wanda nake ganin hakan kamar hatsari ne ga rayuwarsu. Ina zaune a gurin Siyama ta sauko tace wai na shigo dakin in ji Hajiya, kamar mai jira na tashi na nufi upstairs din Siyama na shiga dakin nima na shiga sai na zauna a saman kujerar dake gefen windows ina gaisawa da ita tana min sannu da ciwon da na ji, ta tambayi Mama sannan ta dora da ya karin hakuri.
Ban wani dade ba ganin dare na na yi mata sallama na taso na fito daga dakin, Ahmad na tsaye jikin stairs din yana kallon kafafuwana har na sauko.
“Muje na sauke ki”
“No zan hau Napep”
Tabe baki yai.
“Kin fi son Napap kenan da motata okay muje na taka miki”
Tare muka jeru da shi muna kusan isa gate Siyama ta kwala min kira, a gurin muka tsaya har ta iso, ta miko min ledar hannunta.
“Gashi in ji Hajiya”
“Wannan ba tarbiya bace ya zaki kwala mata kira kamar wacce tai sata?”
“To Yaya idan ban daga murya ba kuka fita ita Hajiya ai fada zata min tace ban ba wa Halima, yanzu kuma na bata ka fara min masifa wai ina murya da yawa”
“To ai sai ki kira wayata ko nata ki ce mu jiraki”
“Ina na ga Number ta?”
“Bata number ki”
Ya fada yana kallona sai ta miko min tsadaddiyar wayar.
“Sa min number ki”