Sashe 61
Gobe Na Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
“Dan Allah ka taimaka ka kaini gida i don't think zan iya driving”
Har zuwa lokacin da ya fadawa Doc Nura haka, be ji komai a ransa game da mutuwar yarsa ba, ya yarda ta mutu amman be ji zafi ko jin kewa ko tausayi a ransa ba, be kuma san da dalilin hakan ba. Wani yanayi yake jin kansa ba damuwa ba bakinciki.
A motar asibiti aka saka baby Namra, shi kuma ya shiga Motar Doc Nura Hajiya da darebanta kuma suka shiga nasu motar, aka baro motar Ahmad asibiti har sai da direban ya dawo ya dauka. Hajiya ce da kanwarsa suka kira familynsu suka sanar musu mutuwar Baby Namra. Hajiya na aikin hawaye yarta na rusa kuka wato kanwar Ahmad wacce ta shaku da Baby kamar wata kawarta,
Ahmad kam part dinsa ya shiga ya kwanta saman gadonsa rairaim ya lumshe idonsa yana maida numfashi a hankali. Wayoyinsa na ta ringing amman ya kasa ko da motsawa balle ya dauka....
AMINU POV.
Zaune yake Sa'adatu na kwance saman jikinsa hannunsa a cikin rigarta yana ta wasa da kirjinta, sam baya jin komai ba ya jin cewar abunda yake aikata akwai zunubi duk kuwa da kasancewar yasan sakamakon mu'amala da matan banza balle mace mai aure kuma kawar matarsa.
Haka yake a bangarenta bata jin cewar cin amanar mijinta take, ta dauki alhakin Allah da na mijinta ga kuma na yayanta hakan be taba damunta ba, taba taba jin ko ras a ranta zuciyarta tana nishadantuwa da alfasha kamar yadda shi ma yake ji.
“Wallahi na rasa kwarin guiwar da zan fada mata cewar zan dauko yayana”
“Wai kai wani irin tsoro kake mata ne? Tana matarka amman ko magana zaka mata sai ka rikice”
“Wallahi nima ban sani mugun tsoronta nake kamar mutuwa”
Ta tabe baki sannan ta tashi zaune.
“Ni dai dan Allah ka yi duk yadda za ka yi ka dawo da Halimatu, ta zauna cikin yayanta, daman can ban jidadin rabuwarku ba domin bana son naga ana raba mace da yayanta, dan tsabani kadan daga tambaya fita unguwa sai ka saketa”
Iskar bakinsa ya bursar domin yasan shi ya fada mata haka cewar ya saketa saboda ta fita unguwa ba da izininsa ba. Amman yanzu yana son ya dawo da ita ko dan arzikinsa ba yana jin kamar yafo samun natsuwa yayi yadda yake so a lokacin da yake auren Halimatu ba kamar yanzu ba, uwa uba kuma ga arzikinsa ance yana tare da ita. Wayarsa ya dauka ya soma lasawa yana fadin.
“Zan dawo da ita dole ma ne na dawo da ita, amman yaran zan fara karbewa tukuna yadda take da shegen son yara dole ta biyo su”
Bayan ya fadi haka ya kara wayar a kunne.
“Babyna ya kike”
“Lafiya kalau Baby kana ina?”
“Ina gurin aiki amman yanzu zan iso gida”
“Sai ka iso love you”
“Love you too”
Ya aje wayar yana tuna lokacin da yake auren Halimatu, at any time zai iya shiga gidansa kuma sai a time din da ya so dawowa zai dawo ba kamar yanzu ba, da wannan ta saka masa ka'idar indai zai dawo gida ya rika kiranta yana sanar mata, and be isa ya dawo pass 9 ba, a yanzu gida yake sallah isha'i wani lokacin har da magariba ma, be isa ya shirya tafiyar karya ba, balle har ya dauki wata macw su je tare, shi yake batawa Halimatu rai amman tai ta bashi hakuri, ba kamar wannan ba da ita zata bata masa ran kuma ya bata hakuri wani lokacin har da kukansa, gaba daya rayuwa ta masa juyin masa jindadi yai masa upside down. Shi kansa yanzu ya kasa gane kansa ga tsoronta ya cika masa zuciya ko magana zai mata fargaba yake.
Mikewa yai tsaye yana sauke ajiyar zuciya.
“Ya kamata na je gida yanzu, idan kin gama ki rufe dakin ki basu makullinsu”
“Okay”
Ta fada yana gyara rigarta.
****
Murja na aje wayar ta kalli Sadi tai saurin sauka ka gado.
“Gashi nan dawowa”
Shi ma zabura yai ya sauka daga kan gadon ya dauki rigar shaddarsa ya saka.
“Abunda muke fa nake tunanin wata rana asirinmu zai tonu, shiyasa na ce miki mu rika haduwa wani gurin kar wata be kira ba ya riske mu”
“Ni fa ba zan iya yawo boye boye ba sai a fara cewa ana ganina ina yawo, amman kai idan ka zo wa ya san abunda ya kawo ka gidan yayanka? Kai dai ko ka gaji da ni ne?”
Bakinsa ya kai yai mata kiss
“Ina zan gaji da ke Murja, tun kina waje ban gaji da ke ba balle yanzu da kike gidan yayana”
“To ka tafi dai kar ya tararda kai sai mun yi waya”
Ta fada tana turashi, ba musu ya dauki keys dinsa da wayarsa da ya saka a silent ya fice da sauri ita kuma ya nufi wardrobe ta dauko zane ta daura sannan ta bude karamar jakarta ta dauko kullin wani abu ta nufo kitchen da shi, kular miyar taushe ta bude ta kwance abun ta zuba kadan sannan ta saka spoon ta garwaye miyar ta fito da sauri ta maida maganin a muhallinsa ta shiga bandaki.
HALIMATU POV.
Me yake faruwa da ni? Da gaske hauka na ke a yanzu? Tsantsar damuwa ce ko kuma shaye-shaye da na fara ne ko kuma gamu nai? Har na shigo cikin gidan mu bana raba dayan biyu ba. Dare ne a lokacin amman a gidanky kamar rana, domin kowa yana farkewa cikin da har da yayana. Sannu kowa ke min suna ta min kallon tausayi, ni kuma na amsa na zauna q tabarmar da aka shimfida tsakar gidan.
“Momy...”
Muryar Namra ce da na kalleta sai ta kara boya bayan Aisha tana hawaye, can kuma ta leko.
“Momy dan Allah ki yi hakuri karki da ke ni, Wallahi ba ni na jefata rijiya ba, ita ce ta hau taba dirowa tana hawa shine murfin ya balle ta fada ciki Wallahi ba ni ba ce”
Ta fada cikin kuka kamin Inna ta karba mata.
“Dan Allah karki mata komai Halimatu, tun dazun take dakonki, ta kasa zaune ta kasa tsaye ta ce idan kika dawo yanka ta za ki yi, ki dauki abun nan a matsayin kaddara”
Idona ya cika da hawaye tausayin yata ya kama ni, sai na mika mata hannu alamar ta zo.
“Ba za ki min komai ba”
Na gyada mata kai sai ta tako ta zo gurin ta kama hannuna nawa ni kuma na jata jikina na rumgume, ni da ita muka fashe da kuka a tare. Ashe ba mu kadai ba, har sauran kanena da Inna sai da sukai hawaye ban lura sai da na tashi zan je dakin Mama.
Wani abum hamdallah a lokacin da na shiga dakin Mama sai na tararda ita a kwance magani a gafenta da ruwan zafi, daman can na san tana da hawan jini sai dai ba kasafai yake tashi ba sai idan wani abun ya faru ko ranta ya bace sosai, wannan karon na san tashin hawan jinin nata baya rasa nasaba da abunda ya faru. A gafen gadonta na na zauna kasa na dora kaina a saman gadon ina bachi ina kuka, Adnan ya shigo ya dora kansa saman cinyata sai kai hannu na dafa kansa.
“Bana da sa'ar komai a rayuwata, ko a lokacin da na haife ku mahaifinku ce min yai na tara masa yaya, zan tsofar da shi....”
Tuna ba ni kadai na ke ba yasa na yi saurin yin shiru sai dai hakan be hana Adnan fahimtar yarena ba.
“Kamar yaya Momy”
Hannu na kai na rufe bakina na hade yawu. Sai ya dago ya kalleni.
“Momy dan Allah ki daina kuka”
Ya fada yana kokarin fashewa da kukan. Hannu na kai na kama fuskarsa na rike.
“Adnan kai na fara haihuwa Allah ya raya min kai, ya inganta rayuwarka yai maka albarka ba baka ikon kula da kanenka ko bana raye”
“Ameen”
Mama ta amsa daga kwance da take tana kallona. Saurin share hasayena nai.
“Ashe kin farka ya jiki?”
“Ya na ki jikin?”
Shiru nai na wani lokacin ina kallonta kamin na amsa.
“Na ji sauki”
Sai ta tashi zaune cikin rashin kwarin jiki ta shiga bandakin da ke cikin dakin.a zaune nai bachi duk yadda Mama ta so na kwanta sai na kasa ko na kwanta ma bachi baya daukata hakan yasa na tashi nai alwala na raya daren da nafila. Misalin hudu da rabi nai sallamar karshe a lokacin da na daga hannuna na yi kirari ga Ubangijina nai salati ga annabi na sai na rasa mi zan fara roko, lafiyata ko ta Baby Namra ko farinciki ko gushewar damuwa?
“Allah ka min mafita ka tsaya min, ka isar min a komai da komai ka zama gatana, ka yafe min laifukana, ka sadani da rahamarka”
Bayan na gama na sake rufewa da salatin Annabi, ban tashi daga gurin ba har aka kira sallah asuba, bayan na gama sallah na dauko qur'ane na soma karantawa har bakwai da yan mintuna sannan na tashi, ina jin kaina na juya kafafuwana kuma sun yi nauyi kamar yadda idanuwa sukai.
“Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un Baby Namra ta rasu gashi ana sanarwa a Zamfara redio”
Shine abunda ya dira a kunne na da muryar Salma. Sai ni ma na karba mata a Hankali daga cikin dakin da nake tsaye.
“Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un”
Sai nai bayabaya har na kai jikin ginin dakin na jingina, hawaye suka ce min salamu alaiki......
7/21/21, 10:45 PM - Buhainat: *GOBE NA...*
By Khadeeja Candy
3️⃣2️⃣
Barka da Sallah Allah ya maimaita mana 🙏❤
Hannu na kai na rufe bakina, wannan karon ba kuka ido da baki kawai nake ba har da zuciya da kwakwalwa da jikina amsa amo yake. Kuka nake ta ko'ina irin kukan da ban taba yi ba, irin kukan da ban taba sani yana tare da ni ba karkawar nake kamar wacce ta shekara a cikin kankara hakorana na hadewa da juna suna wata kara, wani kalar hayaki nake ji a cikin kaina.
“Ashe har yanzun kukan be kare ba Halimatu”
Har zuwa lokacin da ya fadawa Doc Nura haka, be ji komai a ransa game da mutuwar yarsa ba, ya yarda ta mutu amman be ji zafi ko jin kewa ko tausayi a ransa ba, be kuma san da dalilin hakan ba. Wani yanayi yake jin kansa ba damuwa ba bakinciki.
A motar asibiti aka saka baby Namra, shi kuma ya shiga Motar Doc Nura Hajiya da darebanta kuma suka shiga nasu motar, aka baro motar Ahmad asibiti har sai da direban ya dawo ya dauka. Hajiya ce da kanwarsa suka kira familynsu suka sanar musu mutuwar Baby Namra. Hajiya na aikin hawaye yarta na rusa kuka wato kanwar Ahmad wacce ta shaku da Baby kamar wata kawarta,
Ahmad kam part dinsa ya shiga ya kwanta saman gadonsa rairaim ya lumshe idonsa yana maida numfashi a hankali. Wayoyinsa na ta ringing amman ya kasa ko da motsawa balle ya dauka....
AMINU POV.
Zaune yake Sa'adatu na kwance saman jikinsa hannunsa a cikin rigarta yana ta wasa da kirjinta, sam baya jin komai ba ya jin cewar abunda yake aikata akwai zunubi duk kuwa da kasancewar yasan sakamakon mu'amala da matan banza balle mace mai aure kuma kawar matarsa.
Haka yake a bangarenta bata jin cewar cin amanar mijinta take, ta dauki alhakin Allah da na mijinta ga kuma na yayanta hakan be taba damunta ba, taba taba jin ko ras a ranta zuciyarta tana nishadantuwa da alfasha kamar yadda shi ma yake ji.
“Wallahi na rasa kwarin guiwar da zan fada mata cewar zan dauko yayana”
“Wai kai wani irin tsoro kake mata ne? Tana matarka amman ko magana zaka mata sai ka rikice”
“Wallahi nima ban sani mugun tsoronta nake kamar mutuwa”
Ta tabe baki sannan ta tashi zaune.
“Ni dai dan Allah ka yi duk yadda za ka yi ka dawo da Halimatu, ta zauna cikin yayanta, daman can ban jidadin rabuwarku ba domin bana son naga ana raba mace da yayanta, dan tsabani kadan daga tambaya fita unguwa sai ka saketa”
Iskar bakinsa ya bursar domin yasan shi ya fada mata haka cewar ya saketa saboda ta fita unguwa ba da izininsa ba. Amman yanzu yana son ya dawo da ita ko dan arzikinsa ba yana jin kamar yafo samun natsuwa yayi yadda yake so a lokacin da yake auren Halimatu ba kamar yanzu ba, uwa uba kuma ga arzikinsa ance yana tare da ita. Wayarsa ya dauka ya soma lasawa yana fadin.
“Zan dawo da ita dole ma ne na dawo da ita, amman yaran zan fara karbewa tukuna yadda take da shegen son yara dole ta biyo su”
Bayan ya fadi haka ya kara wayar a kunne.
“Babyna ya kike”
“Lafiya kalau Baby kana ina?”
“Ina gurin aiki amman yanzu zan iso gida”
“Sai ka iso love you”
“Love you too”
Ya aje wayar yana tuna lokacin da yake auren Halimatu, at any time zai iya shiga gidansa kuma sai a time din da ya so dawowa zai dawo ba kamar yanzu ba, da wannan ta saka masa ka'idar indai zai dawo gida ya rika kiranta yana sanar mata, and be isa ya dawo pass 9 ba, a yanzu gida yake sallah isha'i wani lokacin har da magariba ma, be isa ya shirya tafiyar karya ba, balle har ya dauki wata macw su je tare, shi yake batawa Halimatu rai amman tai ta bashi hakuri, ba kamar wannan ba da ita zata bata masa ran kuma ya bata hakuri wani lokacin har da kukansa, gaba daya rayuwa ta masa juyin masa jindadi yai masa upside down. Shi kansa yanzu ya kasa gane kansa ga tsoronta ya cika masa zuciya ko magana zai mata fargaba yake.
Mikewa yai tsaye yana sauke ajiyar zuciya.
“Ya kamata na je gida yanzu, idan kin gama ki rufe dakin ki basu makullinsu”
“Okay”
Ta fada yana gyara rigarta.
****
Murja na aje wayar ta kalli Sadi tai saurin sauka ka gado.
“Gashi nan dawowa”
Shi ma zabura yai ya sauka daga kan gadon ya dauki rigar shaddarsa ya saka.
“Abunda muke fa nake tunanin wata rana asirinmu zai tonu, shiyasa na ce miki mu rika haduwa wani gurin kar wata be kira ba ya riske mu”
“Ni fa ba zan iya yawo boye boye ba sai a fara cewa ana ganina ina yawo, amman kai idan ka zo wa ya san abunda ya kawo ka gidan yayanka? Kai dai ko ka gaji da ni ne?”
Bakinsa ya kai yai mata kiss
“Ina zan gaji da ke Murja, tun kina waje ban gaji da ke ba balle yanzu da kike gidan yayana”
“To ka tafi dai kar ya tararda kai sai mun yi waya”
Ta fada tana turashi, ba musu ya dauki keys dinsa da wayarsa da ya saka a silent ya fice da sauri ita kuma ya nufi wardrobe ta dauko zane ta daura sannan ta bude karamar jakarta ta dauko kullin wani abu ta nufo kitchen da shi, kular miyar taushe ta bude ta kwance abun ta zuba kadan sannan ta saka spoon ta garwaye miyar ta fito da sauri ta maida maganin a muhallinsa ta shiga bandaki.
HALIMATU POV.
Me yake faruwa da ni? Da gaske hauka na ke a yanzu? Tsantsar damuwa ce ko kuma shaye-shaye da na fara ne ko kuma gamu nai? Har na shigo cikin gidan mu bana raba dayan biyu ba. Dare ne a lokacin amman a gidanky kamar rana, domin kowa yana farkewa cikin da har da yayana. Sannu kowa ke min suna ta min kallon tausayi, ni kuma na amsa na zauna q tabarmar da aka shimfida tsakar gidan.
“Momy...”
Muryar Namra ce da na kalleta sai ta kara boya bayan Aisha tana hawaye, can kuma ta leko.
“Momy dan Allah ki yi hakuri karki da ke ni, Wallahi ba ni na jefata rijiya ba, ita ce ta hau taba dirowa tana hawa shine murfin ya balle ta fada ciki Wallahi ba ni ba ce”
Ta fada cikin kuka kamin Inna ta karba mata.
“Dan Allah karki mata komai Halimatu, tun dazun take dakonki, ta kasa zaune ta kasa tsaye ta ce idan kika dawo yanka ta za ki yi, ki dauki abun nan a matsayin kaddara”
Idona ya cika da hawaye tausayin yata ya kama ni, sai na mika mata hannu alamar ta zo.
“Ba za ki min komai ba”
Na gyada mata kai sai ta tako ta zo gurin ta kama hannuna nawa ni kuma na jata jikina na rumgume, ni da ita muka fashe da kuka a tare. Ashe ba mu kadai ba, har sauran kanena da Inna sai da sukai hawaye ban lura sai da na tashi zan je dakin Mama.
Wani abum hamdallah a lokacin da na shiga dakin Mama sai na tararda ita a kwance magani a gafenta da ruwan zafi, daman can na san tana da hawan jini sai dai ba kasafai yake tashi ba sai idan wani abun ya faru ko ranta ya bace sosai, wannan karon na san tashin hawan jinin nata baya rasa nasaba da abunda ya faru. A gafen gadonta na na zauna kasa na dora kaina a saman gadon ina bachi ina kuka, Adnan ya shigo ya dora kansa saman cinyata sai kai hannu na dafa kansa.
“Bana da sa'ar komai a rayuwata, ko a lokacin da na haife ku mahaifinku ce min yai na tara masa yaya, zan tsofar da shi....”
Tuna ba ni kadai na ke ba yasa na yi saurin yin shiru sai dai hakan be hana Adnan fahimtar yarena ba.
“Kamar yaya Momy”
Hannu na kai na rufe bakina na hade yawu. Sai ya dago ya kalleni.
“Momy dan Allah ki daina kuka”
Ya fada yana kokarin fashewa da kukan. Hannu na kai na kama fuskarsa na rike.
“Adnan kai na fara haihuwa Allah ya raya min kai, ya inganta rayuwarka yai maka albarka ba baka ikon kula da kanenka ko bana raye”
“Ameen”
Mama ta amsa daga kwance da take tana kallona. Saurin share hasayena nai.
“Ashe kin farka ya jiki?”
“Ya na ki jikin?”
Shiru nai na wani lokacin ina kallonta kamin na amsa.
“Na ji sauki”
Sai ta tashi zaune cikin rashin kwarin jiki ta shiga bandakin da ke cikin dakin.a zaune nai bachi duk yadda Mama ta so na kwanta sai na kasa ko na kwanta ma bachi baya daukata hakan yasa na tashi nai alwala na raya daren da nafila. Misalin hudu da rabi nai sallamar karshe a lokacin da na daga hannuna na yi kirari ga Ubangijina nai salati ga annabi na sai na rasa mi zan fara roko, lafiyata ko ta Baby Namra ko farinciki ko gushewar damuwa?
“Allah ka min mafita ka tsaya min, ka isar min a komai da komai ka zama gatana, ka yafe min laifukana, ka sadani da rahamarka”
Bayan na gama na sake rufewa da salatin Annabi, ban tashi daga gurin ba har aka kira sallah asuba, bayan na gama sallah na dauko qur'ane na soma karantawa har bakwai da yan mintuna sannan na tashi, ina jin kaina na juya kafafuwana kuma sun yi nauyi kamar yadda idanuwa sukai.
“Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un Baby Namra ta rasu gashi ana sanarwa a Zamfara redio”
Shine abunda ya dira a kunne na da muryar Salma. Sai ni ma na karba mata a Hankali daga cikin dakin da nake tsaye.
“Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un”
Sai nai bayabaya har na kai jikin ginin dakin na jingina, hawaye suka ce min salamu alaiki......
7/21/21, 10:45 PM - Buhainat: *GOBE NA...*
By Khadeeja Candy
3️⃣2️⃣
Barka da Sallah Allah ya maimaita mana 🙏❤
Hannu na kai na rufe bakina, wannan karon ba kuka ido da baki kawai nake ba har da zuciya da kwakwalwa da jikina amsa amo yake. Kuka nake ta ko'ina irin kukan da ban taba yi ba, irin kukan da ban taba sani yana tare da ni ba karkawar nake kamar wacce ta shekara a cikin kankara hakorana na hadewa da juna suna wata kara, wani kalar hayaki nake ji a cikin kaina.
“Ashe har yanzun kukan be kare ba Halimatu”