Sashe 18
Gobe Na Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Wani dimmmm na ji kamar an dora min abu akao na kunya da nauyin kalamanta, hakika ni ma mace ce ba zan zo mijina ya kula wata mace ba kuma ba zan jidadi ba, sai a iya zamana da Kabir ban taba daukar hoto daga ni sai shi ba ko kuma ni kadai na tura masa to a ina ya samu hotona wata kila a media ko kuma a gurin wani wata kila kuma ya dauke ni ne a lokacin da nake aiki.
“Shin baki taba sanin Kabir yana aure da yaya ba?”
Ta jefo min tambayar da ban san ta ina zan tattara amsar da mika mata ba har ta gamsar da ita.
“Ya kamata ace na damu da lafiyar mijina a yanzu ko dan saboda yayan mu, amman saboda ke idan na tuno sai na ce masa Allah ya kara, ke ya kamata ace kin fi ni damuwa da shi, ko ba komai kin fini samun lokacinsa kin fi ni samun soyayarsa da kularwarsa, kin fini muhimmanci a gurinsa”
Tana fadar hakan ta fara takawa zata bar ni a gurin da dafin furucinta, cikin kuzari da hanzari na mika sautin muryarta dan isar da mata da abunda bata sani ba.
“Babu wata alaka tsakanina da mijin, abokin aikina ne kawai kuma ni ma matar aure ce har da yaya be kamata ki zarge ni ba”
Juyowa tai ta tsaya tana kallona kamar mai mamakin abunda ya fito daga bakina, a zatona zata yarda da kalamaina ne ko kuma ta dora su a ma'aunin tunani.
“Matar aure? Kina nufin irin auren nan da be hana mai yinsa aikata komai ko? Kina nufin irin ijiyar auren da wasu kan take su aikata alfasha da wasu mazan ko?”
Wani irin abu na ji ya taso min ina iya jure komai a cikin har da kazafin sata ko maita amman ba zan juri a kira mi karuwaba, domin na san illa da kazantar zina ban aikata ba dan haka ba zan yarda wasu su bata min suna ba.
“Ke malama ban san ki ba bana da wata alaka da ke, ko ki iya halsheki ba zan jure irin wadannan kalaman daga bakin kowa ba...!”
“Baki san ni ba ba ki da alaka da ni amman kina da ita da mijina ko? Banza marar sanin ciwon wawuya wacce igiyar aure bata hana ta aikata komai ba....”
Cikin daga muryar take fada min haka, ban san lokacin da na karasa kusa da ita na wanke mata fuska da mari ba, abunda ya janyo hankalin wasu mutanen izuwa gare mu kenan daman tun da ta fara maganar aka fara tsayawa yana kallon mu...
___________
Tofaaaaaaaaa.
Al-hamdulillah yanzu kan Al-hamdulillah na gama komai hankali ya dawo gurin typing.....✍️
7/20/21, 8:30 AM - Buhainat: *GOBE NA...*
_My Tomorrow_
By Khadeeja Candy
1️⃣1️⃣
“Ko yar iska ce ni na fi karfin iskanci da Kabir, mutumen da ke daukar the same salary da na ke dauka, mi ya samu mi ya bani na fi karfin abunda kike tunani na fi karfin aikata alfasha da aurena da yayana”
Na fada mata cikin zafin nama bayan na wanke mata fuska da mari, wata matar da ce da ban wayance wacece ita ba ta zo da sauri ta rike matar Kabir din tana kiranta da sunanta.
“Haba Maryam wannan abun da kike ba mutunci ba ne, ai ko da gaske mijinki yana aikata alfahari be kamata ki tsare mace a hanya kina mata wannan maganar ba, ballanta baki da tabbaci akan hakan kamata yai ki fara damuwa da damuwar mijinki a yanzu Kabir yana a halin tausayin a yanzu abunda likito suke fada jinin ya kai har cikin kansa zai rayu ba zai rayu ba haukacewa zai yi ko ya manta komai duk be dame ki ba sai wani abun da ba zaki iya canjawa ba! Haba Maryam”
“Wallahi Anty karuwarsa ce kuma saboda ita wannan hadrin ya same shi, yanzu kuma dan rashin kunya har ta sako kafarta ta zo ganinsa? Haba Anty da wanne zan ji da ciwonsa ko da ganinta”
Ta fada cikin kuka ni kan tuni jikina yai sanyi jin abunda ya same Kabir jinin ya taba kwakwalwarsa, abun ya tsorani sosai kuma ya jefani a cikin wata duniyar tunanin da fargabar yadda gobensa zata kasance. Takawa na fara yi ina tafiya na nufo gate din fita daga asibitin gaba daya ba tare da na sake cewa komai ba, kallo daya za ka min ka fahimci akwai damuwa a tare da kamar yadda tunani ya kawo min ziyara a yanzu. Kar dai ace saboda ya rabe ni hakan ya same shi? Kaddararta ta fara wuce iya ni kawai har ta fara taba yayana da mutanen da suke kusa da ni? Tambayar da na yi ma kaina kenan tambayar da ban san wanda zai amsa min ita ba. Guri na samu kusa da gate din na zauna a saman wani guntun dakali idona cike da kwalla, ban samu kaina a cikin tausayin wani mutum wanda ba jinina kamar yadda tausayin Kabir ya dirar min a zuciya yai min kawaya a ruhi, ya nemi jijiyoyin jinina da jiki ya rike.
“Halimatu”
Muryar Abdallah ce ta hankalto ni har na dago kaina na kalleshi hawaye na min zuba.
“Zama kikai a guri kamar wannan har kina kuka a public? Mutane fa suna ta kallonki”
Cikin wani irin sanyin muryar da natsuwa yai min maganar da sautin da ni kadai zan iya ji da kuma fahimtar kalmomin da yake furta min. Sauke kaina nai daga kallonsa zuwa kallon titi ina ta yawo da ido.
“Abdallah ina tunanin Gobena ne, ya zata kasance? Miyasa abubuwan nan za su faru ta dalilina? Na farko yata? Na biyu kuma abokin aikina? Abunda ya faru da Namra kamar jiya ne, ban sammaci wani abun da zai taba zuciyata kamar haka zai sake faruwa ba, idan wani abun nai nauyi ya sake faruwa da ni ina jin kamar ba zan iya jure ba”
Risinowa yai gabana yana kallon fuskata.
“Share hawayenki zo muje a mota ki min bayani maybe zan sama miki mafita”
Sai na sake dago kai na kalleshi a karo na biyu, a yau Abdallah yai magana ta hankali da nuna kulawarsa a kaina, ko da yake a can baya ma ai yana nunawa sai dai wacan karon ina ganin rashin dacewar hakan saboda akwai igiyar aure a kaina, kuma a baya duk wata magana da zai min ta Aminu ce da abunda ya shafe shi.
“Abdallah zan iya rikon ka kamar dan'uwan? Abokin shawara? Wanda zan labartawa damuwata ya nema min mafita? Dan Allah?”
Sai ya kasa ce min komai, ba dan komai ba dan sai dan ya san inda manufata ta dosa, daga lokacin da zai rike ni a matsayin yar'uwa to babu zancen soyayya ko aure a tsakaninmu, ni kuwa abunda na fi so kenan, domin ban tana yi ma Abdallah kallon so ko kauna ba balle har ta ga kai ga aure! Mikewa yai tsaye ya nufi inda motarsa take, sai a lokacin na lura da inda ya faka ta, tashi nai na bi bayansa ba tare da na share hawayena ba. Na bude front seat ma shiga shi kuma ya tashi motar ya koma da ni cikin asibitin, a daya daga cikin guraren da aka tanada domin likitoci su faka motocinsu ya faka motarsa sannan ya juyo ya kalleni.
“Idan har hakan zai faranta miki rai Halima zan yi, amman ki sani zan cutu domin ba abunda nake so kenan ba, sai dai zan jira har lokacin da zaki fahimci da gaske na ke, fada min minene damuwarki?”
“Abokin aikina yayi hadari saboda ni, kuma yanzu na ji cewar akwai yiyuwar jimin ya tana kansa wata kila ya haukace ko ya manta komai ko ya mutu”
Na fada kai tsaye ina share hawayena. Sosai ya nuna min damuwarsa.
“Subhanallahi miya same shi haka?”
A take na labarta masa komai har zuwa fadan da mukai da matarsa. Na yi zaton ko zai tausaya masa ne sai na ga murmushi a fuskarsa.
“Kin kasa yarda cewar kina da kyau da kan iya jan hankali wasu mazan izuwa gareki saboda Aminu yana yawan fada miki cewar baki da kyau ko? Kina da kyau Halima seriously kina da jikin da ko wane namiji zai so ki kasance a tare da shi, ina tunanin abunda ya ja hankali abokin aikinki kenan har ya kai ga mallakar hotunanki da sakawa sunanki spacial saboda ke din ta musamman ce”
Na yi kasa da kaina ina tuna lokacin da Aminu yake fada min cewar kibar jikina ta masa yawa shi yar siririyar mace yake so wacce ke kamar zata kare, mace da zai nuna mata soyayya ta nuna masa yai zaman jindadi da ita ba zaman tara masa yaya ba.
“Bana son ki saboda kawai wadannan abubuwan da na lissafa miki, no ina fada miki hakan ne saboda ki yarda cewar ke din kyakkyawa ce kuma Allah be rage ki da komai ba”
Maganar da yai ce ta dawo da ni daga duniyar tunanin da na fara zuwa, hakan yasa nai kokarin kawarta maganar.
“Taya zan fahimtar da matarsa cewar ni ba karuwarsa ba ce”
Sai da ya danna horn din motarsa kamar wani ne a gaban mu alhalin babu komai a gabanmu sai fulawoyi.
“Ki sakawa ranki sallama for now Halimatu, ki cire zancen cewar saboda ke wannan abun ya samu abokin aikinki, kuma ki manta da zancen fahimtar da matarsa, ki daga musu kafa na wani lokacin idan ya samu lafiya kamin lokacin sai ki je ki ganshi kuma ki fada masa ya fahimtar matarsa sannan kuma ki gargade shi daya cire kansa akan duk wani abun daya shafe ki, Halima kin san abunda nake so da ke?”
Na girgiza masa kai alamar ban sani ba.
“So na ke ki manta da komai da kowa a gabanki ki maida hankalinki gurin aikinki kuma ki kula da yaranki sai kuma zancen Namra shi ma ki jajirce wajen ganin kin kwato mata hakkinta barin wannan maganar zai bawa kanen mahaifinta damar yi ma wata yar ne”
“Amman Mama tace na bar maganar saboda kar na jawa Namra abun kunya idan ta girma”
“Shin baki taba sanin Kabir yana aure da yaya ba?”
Ta jefo min tambayar da ban san ta ina zan tattara amsar da mika mata ba har ta gamsar da ita.
“Ya kamata ace na damu da lafiyar mijina a yanzu ko dan saboda yayan mu, amman saboda ke idan na tuno sai na ce masa Allah ya kara, ke ya kamata ace kin fi ni damuwa da shi, ko ba komai kin fini samun lokacinsa kin fi ni samun soyayarsa da kularwarsa, kin fini muhimmanci a gurinsa”
Tana fadar hakan ta fara takawa zata bar ni a gurin da dafin furucinta, cikin kuzari da hanzari na mika sautin muryarta dan isar da mata da abunda bata sani ba.
“Babu wata alaka tsakanina da mijin, abokin aikina ne kawai kuma ni ma matar aure ce har da yaya be kamata ki zarge ni ba”
Juyowa tai ta tsaya tana kallona kamar mai mamakin abunda ya fito daga bakina, a zatona zata yarda da kalamaina ne ko kuma ta dora su a ma'aunin tunani.
“Matar aure? Kina nufin irin auren nan da be hana mai yinsa aikata komai ko? Kina nufin irin ijiyar auren da wasu kan take su aikata alfasha da wasu mazan ko?”
Wani irin abu na ji ya taso min ina iya jure komai a cikin har da kazafin sata ko maita amman ba zan juri a kira mi karuwaba, domin na san illa da kazantar zina ban aikata ba dan haka ba zan yarda wasu su bata min suna ba.
“Ke malama ban san ki ba bana da wata alaka da ke, ko ki iya halsheki ba zan jure irin wadannan kalaman daga bakin kowa ba...!”
“Baki san ni ba ba ki da alaka da ni amman kina da ita da mijina ko? Banza marar sanin ciwon wawuya wacce igiyar aure bata hana ta aikata komai ba....”
Cikin daga muryar take fada min haka, ban san lokacin da na karasa kusa da ita na wanke mata fuska da mari ba, abunda ya janyo hankalin wasu mutanen izuwa gare mu kenan daman tun da ta fara maganar aka fara tsayawa yana kallon mu...
___________
Tofaaaaaaaaa.
Al-hamdulillah yanzu kan Al-hamdulillah na gama komai hankali ya dawo gurin typing.....✍️
7/20/21, 8:30 AM - Buhainat: *GOBE NA...*
_My Tomorrow_
By Khadeeja Candy
1️⃣1️⃣
“Ko yar iska ce ni na fi karfin iskanci da Kabir, mutumen da ke daukar the same salary da na ke dauka, mi ya samu mi ya bani na fi karfin abunda kike tunani na fi karfin aikata alfasha da aurena da yayana”
Na fada mata cikin zafin nama bayan na wanke mata fuska da mari, wata matar da ce da ban wayance wacece ita ba ta zo da sauri ta rike matar Kabir din tana kiranta da sunanta.
“Haba Maryam wannan abun da kike ba mutunci ba ne, ai ko da gaske mijinki yana aikata alfahari be kamata ki tsare mace a hanya kina mata wannan maganar ba, ballanta baki da tabbaci akan hakan kamata yai ki fara damuwa da damuwar mijinki a yanzu Kabir yana a halin tausayin a yanzu abunda likito suke fada jinin ya kai har cikin kansa zai rayu ba zai rayu ba haukacewa zai yi ko ya manta komai duk be dame ki ba sai wani abun da ba zaki iya canjawa ba! Haba Maryam”
“Wallahi Anty karuwarsa ce kuma saboda ita wannan hadrin ya same shi, yanzu kuma dan rashin kunya har ta sako kafarta ta zo ganinsa? Haba Anty da wanne zan ji da ciwonsa ko da ganinta”
Ta fada cikin kuka ni kan tuni jikina yai sanyi jin abunda ya same Kabir jinin ya taba kwakwalwarsa, abun ya tsorani sosai kuma ya jefani a cikin wata duniyar tunanin da fargabar yadda gobensa zata kasance. Takawa na fara yi ina tafiya na nufo gate din fita daga asibitin gaba daya ba tare da na sake cewa komai ba, kallo daya za ka min ka fahimci akwai damuwa a tare da kamar yadda tunani ya kawo min ziyara a yanzu. Kar dai ace saboda ya rabe ni hakan ya same shi? Kaddararta ta fara wuce iya ni kawai har ta fara taba yayana da mutanen da suke kusa da ni? Tambayar da na yi ma kaina kenan tambayar da ban san wanda zai amsa min ita ba. Guri na samu kusa da gate din na zauna a saman wani guntun dakali idona cike da kwalla, ban samu kaina a cikin tausayin wani mutum wanda ba jinina kamar yadda tausayin Kabir ya dirar min a zuciya yai min kawaya a ruhi, ya nemi jijiyoyin jinina da jiki ya rike.
“Halimatu”
Muryar Abdallah ce ta hankalto ni har na dago kaina na kalleshi hawaye na min zuba.
“Zama kikai a guri kamar wannan har kina kuka a public? Mutane fa suna ta kallonki”
Cikin wani irin sanyin muryar da natsuwa yai min maganar da sautin da ni kadai zan iya ji da kuma fahimtar kalmomin da yake furta min. Sauke kaina nai daga kallonsa zuwa kallon titi ina ta yawo da ido.
“Abdallah ina tunanin Gobena ne, ya zata kasance? Miyasa abubuwan nan za su faru ta dalilina? Na farko yata? Na biyu kuma abokin aikina? Abunda ya faru da Namra kamar jiya ne, ban sammaci wani abun da zai taba zuciyata kamar haka zai sake faruwa ba, idan wani abun nai nauyi ya sake faruwa da ni ina jin kamar ba zan iya jure ba”
Risinowa yai gabana yana kallon fuskata.
“Share hawayenki zo muje a mota ki min bayani maybe zan sama miki mafita”
Sai na sake dago kai na kalleshi a karo na biyu, a yau Abdallah yai magana ta hankali da nuna kulawarsa a kaina, ko da yake a can baya ma ai yana nunawa sai dai wacan karon ina ganin rashin dacewar hakan saboda akwai igiyar aure a kaina, kuma a baya duk wata magana da zai min ta Aminu ce da abunda ya shafe shi.
“Abdallah zan iya rikon ka kamar dan'uwan? Abokin shawara? Wanda zan labartawa damuwata ya nema min mafita? Dan Allah?”
Sai ya kasa ce min komai, ba dan komai ba dan sai dan ya san inda manufata ta dosa, daga lokacin da zai rike ni a matsayin yar'uwa to babu zancen soyayya ko aure a tsakaninmu, ni kuwa abunda na fi so kenan, domin ban tana yi ma Abdallah kallon so ko kauna ba balle har ta ga kai ga aure! Mikewa yai tsaye ya nufi inda motarsa take, sai a lokacin na lura da inda ya faka ta, tashi nai na bi bayansa ba tare da na share hawayena ba. Na bude front seat ma shiga shi kuma ya tashi motar ya koma da ni cikin asibitin, a daya daga cikin guraren da aka tanada domin likitoci su faka motocinsu ya faka motarsa sannan ya juyo ya kalleni.
“Idan har hakan zai faranta miki rai Halima zan yi, amman ki sani zan cutu domin ba abunda nake so kenan ba, sai dai zan jira har lokacin da zaki fahimci da gaske na ke, fada min minene damuwarki?”
“Abokin aikina yayi hadari saboda ni, kuma yanzu na ji cewar akwai yiyuwar jimin ya tana kansa wata kila ya haukace ko ya manta komai ko ya mutu”
Na fada kai tsaye ina share hawayena. Sosai ya nuna min damuwarsa.
“Subhanallahi miya same shi haka?”
A take na labarta masa komai har zuwa fadan da mukai da matarsa. Na yi zaton ko zai tausaya masa ne sai na ga murmushi a fuskarsa.
“Kin kasa yarda cewar kina da kyau da kan iya jan hankali wasu mazan izuwa gareki saboda Aminu yana yawan fada miki cewar baki da kyau ko? Kina da kyau Halima seriously kina da jikin da ko wane namiji zai so ki kasance a tare da shi, ina tunanin abunda ya ja hankali abokin aikinki kenan har ya kai ga mallakar hotunanki da sakawa sunanki spacial saboda ke din ta musamman ce”
Na yi kasa da kaina ina tuna lokacin da Aminu yake fada min cewar kibar jikina ta masa yawa shi yar siririyar mace yake so wacce ke kamar zata kare, mace da zai nuna mata soyayya ta nuna masa yai zaman jindadi da ita ba zaman tara masa yaya ba.
“Bana son ki saboda kawai wadannan abubuwan da na lissafa miki, no ina fada miki hakan ne saboda ki yarda cewar ke din kyakkyawa ce kuma Allah be rage ki da komai ba”
Maganar da yai ce ta dawo da ni daga duniyar tunanin da na fara zuwa, hakan yasa nai kokarin kawarta maganar.
“Taya zan fahimtar da matarsa cewar ni ba karuwarsa ba ce”
Sai da ya danna horn din motarsa kamar wani ne a gaban mu alhalin babu komai a gabanmu sai fulawoyi.
“Ki sakawa ranki sallama for now Halimatu, ki cire zancen cewar saboda ke wannan abun ya samu abokin aikinki, kuma ki manta da zancen fahimtar da matarsa, ki daga musu kafa na wani lokacin idan ya samu lafiya kamin lokacin sai ki je ki ganshi kuma ki fada masa ya fahimtar matarsa sannan kuma ki gargade shi daya cire kansa akan duk wani abun daya shafe ki, Halima kin san abunda nake so da ke?”
Na girgiza masa kai alamar ban sani ba.
“So na ke ki manta da komai da kowa a gabanki ki maida hankalinki gurin aikinki kuma ki kula da yaranki sai kuma zancen Namra shi ma ki jajirce wajen ganin kin kwato mata hakkinta barin wannan maganar zai bawa kanen mahaifinta damar yi ma wata yar ne”
“Amman Mama tace na bar maganar saboda kar na jawa Namra abun kunya idan ta girma”