Sashe 37
Gobe Na Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
“Ashe kana iya damuwa da ganinta ai na dauka ka manta da kana da yaya”
“Halima bari kiji na fada miki wallahi duk yata ta bata ko wani abun ya sameta sai na wulakanta ki, sai na sa kin yi nadamar haihuwarki da akai a duniyar nan Wallahi Wallahi dan haka ki nemo min yata tun wuri”
Be jira abunda zance ba ya katse kiran, wani uban haushi ne ya cika ni har na ji ina ma dai ace ban dauki wayar ba.
Da tambaya muka gane gidan, domin number da aka bamu mun yi ta kira ba a dauka ba, daga baya ma sai aka kashe wayar. Wani irin katon gidane mai katon gate irin na manyan mutanen nan da suka ci arziki har sukai kashinsa, kai idam ma baka sani ba za kai zaton gidan fillar kai ne saboda girmansa da tsaruwarsa, ko ina na gidan an kawatashi da fulawoyi da kuma irin dagayen itacen nan masu haska gida.
“Sannu Malam dan Allah yata na ke nema kuma ance tana nan”
Na fadawa mai gadin bayan nai kwankwasa kofar gidan ya bude min na shiga ciki.
“Ina aka ce miki?”
“Ce min akai gidan Alhaji Muhammad Gwarzo”
“Eh nan ne shiga ciki”
Kai tsaye na doshi cikin gidan, a maimakon na shiga part din farko sai na nufi dayan part din da shi nake hango kofarsa tsabanin babban part din da na kasa ganin kofar shigarsa, wata kila kuma ta karamin ake shiga.
Kofar falon na hango a bude tun ka na karasa, na yi iya yadda shari'a tace wato yin sallama da na ji ba amsa min ba na kunna kai cikin katon falon mai cike da sanyin ac da daddadan kamshi sai dai ban fasa sallamar duk kuwa da ban ga kowa ba.
Ina kokarin juyawa na fita wani mutun ya fito daga wani bangare na falon yana rike da plate da ke dauke da soyayyen kwai sai kofin tea. Wani shegen short ne a jikinsa kirjinsa kuma a tsirara dan babu riga a jikinsa. Da gila ya tambayi abunda ya kawo ni falon.
“Yata ta bata aka ce tana nan gidan Alhaji Muhammad Gwarzo... ”
Wani kallo na watsa min daga sama zuwa kasa sannan ya zauna ya aje plate din hannunsa a saman center table din dake kusa da shi yana cigaba da kallo, zuwa can kuma ya dauke kai ba tare da ya ce da ni komai ba.
“Yata nake nema na fada maka”
Banza yai min kamar ba zai amsani ba, sannan ya ce.
“Idan kin ganta ai sai ki dauka”
“Idan bata nan ka fada min bata nan ba sai ka wulakanta ni ba domin ba bara na zo yi ba”
Na fada a fusace, ina tuna inda na taba ganinsa. Uffan be ce min ba ya dauki tea gabansa yana sha tare da maida hankalinsa gurin katuwar plasma dake manne a wallpaper falon. Juyowa nai a hasale na fito daga falon marasa na murdawa, kamin na isa dayan part din sai da na rike cikina kusan sau uku. Ina isa na zauna a gurin na runtse ido ina sauraren radadin da take min. Daker na iya tsada hankalina har na lura da kofar falon, cike da karfin hali na unkura na mike tsaye na isa bakin kofar ina kokarin kai hannu na nai knocked aka bude kofar daga can ciki. Fuskar Mutumen dazun din nan ne da ke wacan part din da na baro, sai dai wannan karon akwai jallabiya a jikinsa, mamaki ya kama ni shi din ko kuwa su ma twins ne kamar Abdallah da Abdulhamid? Ko kuma wata hanyar ya biyo ta can ciki ya isa wannan part din? Sai da nai kamar ba zan masa magana ba, sai kuma wata zuciyar ta hana ni abunka da nama.
“Dan Allah yata nake nema aka ce min tana nan”
Be ce min komai ba ya fito daga falon ya sauko stairs din ya nufi gurin wata mota dake fake kusa da inda nake zaune.
“Tana nan ciki”
Ya fada bayan ya bude motar. Unkurawa nai na tashi na nufi kofar falon na shiga ina takawa a hankali saboda abu nake jin kamar zai zubo min. Na yi mamakin karamci da sakin fuskar da na tarar a fuskar Hajiyar gidan ina yin sallama ta amsa min tana min sannu da zuwa kamar ta san ni, Namra na ganina ta taso da sauri ta nufo inda nake tana dariya.
“Momy”
Rumgumeta nai na lumshe ido.
AHMAD POV.
Da gangan yake son ya shiga motarsa ya yi tafiyarsa saboda kar ma mahaifiyar yarinyar ta ga fuskar yi masa godiya ko yi masa wata maganar. Ji yake kamar ya fada mata bakar magana son ransa aka my wufintar da yar da tai amman ba shi da damar wannan tun da shi ba uban yar ba ne kuma ba shi da alaka da ita. Ko ba komai dai ya san hankalinta ya tashi tun da ga shi har tana zubar jini.
Tun kamin ya karasa gate aka bude masa gate din, ganin wani tsaye da mota a bakin gate din gidan yasa ya tsaya ya sauke gilashin motar yana kallon Abdulhamid da na shi gilashin yake sauke.
“Malam lafiya?”
“Wata yarinya muke nema aka ce tana nan gidan mun kira number da aka ba da a sanarwa muka jita a kashe shiyasa na zo”
“Kai ne mahaifinta?”
“No ni ne dai nake auren mahaifiyarta”
Abdulhamid ya amsa kai tsaye, sai Ahmad ya kalleshi da kyau sannan ya dauke kai.
“To ka tsaya nan za a fito maka da matarka”
Ya karasa yana kallon wayarsa. Number sis dinsa ya lalubo ya aika mata kira, in few seconds tai picking.
“Sis ki fadawa matarta mijinta yana jiranta a waje”
“Okay Ammn bro bleeding ta ke, ya dan jira ta shiga bandaki”
“Ki fada mata na ce”
Yana fadar haka ya kashe wayar ya karawa motarsa wuta ya hau titi, Abdulhamid na zaune cikin wata mai kama da Ahmad din ta budo karamar kofar gate din ta leko shi daga can cikin motar da yake zaune tace.
“Kai ne mijinta?”
Abdulhamid ya gyada mata kai.
“To ka dan jira ta fito tana bleeding amman ta dan shiga toilet ne”
“Ta ji ciwo ne?”
“No i think ta samu miscarriage ne... ”
Ta fada tana dan zare.
“Miscarriage...?”
Ya maimaita.
“Yes ban dai tabbatar ba, amman kasan idan am samu tashin hankali yana iya causing wannan matsalar, amman ba lallai ne ya zube duka ba, amman dai shawara ka kaita asibiti yanzu dan tabbatarwa”
Tun da ta fara yake kallon yadda take ta zuba masa zance har ta gama, daman daga ganinta irin yan matan nan ne masu surutun fadi baa tambaye ka ba.
“Okay”
Ya amsa mata zuciyarsa cike da mamaki, kai ta gyada masa sannan ta juya ta koma ciki, kamin ta isa falon wayar da ke hannunta tai ringing alamar kira. Soul mate ne rubuce a saman screen din, murmushi ne ya bayyana a fuskarta jikinta har rawa yake ta kara wayar a kunnenta sannan ta nufi wani bangare na gida cike da shauki tana amsa wayar.
HALIMATU POV.
Ban lura da jini dake zubo min ba har sai da na zauna a saman manyan cushion din dake falo, shi ma saboda Hajiyar ta yi magana ne.
“Subhanallahi kin ji ciwo ne?”
A lokacin da na duba sai na lura da jinin ya bata duk sawun kafata yake jini ya bata gurin. A iya sanina dai ban ji ciwo ba ban fadi ba balle na ce na ji ciwo ne, jini ba ta kafa yake min zuba ba ta cikina ne duk da kuwa da bana da tabbacin hakan domin ban ji zubowar komai ba sai jin alamar zubowar da na ji dazun ashe har ya zubo ban sani ba.
“A a ban ji ciwo ba”
Na amsa mata gabana na faduwa wani sabon tashin hankali na kusantata.
“Allah ya tsare idan ba miscarriage kika samu ba”
Hajiyar na rufe baki wata budurwar da ke zaune a dinning ta ta amsa da.
“Shi ne ma, kin san tashin hankali yana saka haka ko da ciki ya yi kwari ba re kuma ace yana sabo kuma.... ”
Bata karasa Hajiyar ta daka mata tsawa.
“Haba idan kin fara zubawa ba ki san ki tsaya ba? Shiyasa kike samu matsala da Yayanki kina da yawan magana”
Da hannu tai zip up din bakinta.
“Taso muje ciki ki gyara jikinki”
Naga karamci sosai a gurin matar nan babu kyama ta shiga da ni har cikin dakinta ta kai ni bandakin ta bani duk wani abu da nake bukata tun daga pad da pant da doguwar rigar da zan canja. Kamar kazar da kwai ya fashewa haka na fito daga bandaki jikina babu kwari na dawo falon a maimakon na zauna sai na yi tsaye kamar an dasa ni wasu sabbin hawayen na cika min ido.
“Baiwar Allah ki zauna mana yau masu aikin na mu basa nan balle akwai miki ruwa”
“Aa na gode sosai Hajiya, gida zan tafi yan uwana suna can suna ta neman Namra, na gode sosai da karamci na ji dadi da yata ta fada hannun mace mai karamci da son mutane kamar ki Allah ya saka da alheri”
“Babu komai Gwarzo za ki m godiya ai, muna zaune ya zo da ita sai fada yake wai kun wofintar da ita, dan Allah a rika kula”
“In-Sha-Allah”
Bayan na amsa mata, ta dauki wayarta dake gefen cushion din ta kira number da na ke zaton ta wacan mutumen ce.
“Za ta tafi da yarinyar nan”
Shine abunda na ji ta fada ban ji abunda ya fada mata ba, murmushi kawai na ga ta yi sannan ta aje wayar tana kallona.
“A kula dan Allah ina zuwa”
Tsakanin shigarta dakinta da fitowarta be wuce minti biyar ba ta mikowa Namra dake rike da hannuna abu a leda sannan ta shafa kanta.
“To bye bye jikata”
“Halima bari kiji na fada miki wallahi duk yata ta bata ko wani abun ya sameta sai na wulakanta ki, sai na sa kin yi nadamar haihuwarki da akai a duniyar nan Wallahi Wallahi dan haka ki nemo min yata tun wuri”
Be jira abunda zance ba ya katse kiran, wani uban haushi ne ya cika ni har na ji ina ma dai ace ban dauki wayar ba.
Da tambaya muka gane gidan, domin number da aka bamu mun yi ta kira ba a dauka ba, daga baya ma sai aka kashe wayar. Wani irin katon gidane mai katon gate irin na manyan mutanen nan da suka ci arziki har sukai kashinsa, kai idam ma baka sani ba za kai zaton gidan fillar kai ne saboda girmansa da tsaruwarsa, ko ina na gidan an kawatashi da fulawoyi da kuma irin dagayen itacen nan masu haska gida.
“Sannu Malam dan Allah yata na ke nema kuma ance tana nan”
Na fadawa mai gadin bayan nai kwankwasa kofar gidan ya bude min na shiga ciki.
“Ina aka ce miki?”
“Ce min akai gidan Alhaji Muhammad Gwarzo”
“Eh nan ne shiga ciki”
Kai tsaye na doshi cikin gidan, a maimakon na shiga part din farko sai na nufi dayan part din da shi nake hango kofarsa tsabanin babban part din da na kasa ganin kofar shigarsa, wata kila kuma ta karamin ake shiga.
Kofar falon na hango a bude tun ka na karasa, na yi iya yadda shari'a tace wato yin sallama da na ji ba amsa min ba na kunna kai cikin katon falon mai cike da sanyin ac da daddadan kamshi sai dai ban fasa sallamar duk kuwa da ban ga kowa ba.
Ina kokarin juyawa na fita wani mutun ya fito daga wani bangare na falon yana rike da plate da ke dauke da soyayyen kwai sai kofin tea. Wani shegen short ne a jikinsa kirjinsa kuma a tsirara dan babu riga a jikinsa. Da gila ya tambayi abunda ya kawo ni falon.
“Yata ta bata aka ce tana nan gidan Alhaji Muhammad Gwarzo... ”
Wani kallo na watsa min daga sama zuwa kasa sannan ya zauna ya aje plate din hannunsa a saman center table din dake kusa da shi yana cigaba da kallo, zuwa can kuma ya dauke kai ba tare da ya ce da ni komai ba.
“Yata nake nema na fada maka”
Banza yai min kamar ba zai amsani ba, sannan ya ce.
“Idan kin ganta ai sai ki dauka”
“Idan bata nan ka fada min bata nan ba sai ka wulakanta ni ba domin ba bara na zo yi ba”
Na fada a fusace, ina tuna inda na taba ganinsa. Uffan be ce min ba ya dauki tea gabansa yana sha tare da maida hankalinsa gurin katuwar plasma dake manne a wallpaper falon. Juyowa nai a hasale na fito daga falon marasa na murdawa, kamin na isa dayan part din sai da na rike cikina kusan sau uku. Ina isa na zauna a gurin na runtse ido ina sauraren radadin da take min. Daker na iya tsada hankalina har na lura da kofar falon, cike da karfin hali na unkura na mike tsaye na isa bakin kofar ina kokarin kai hannu na nai knocked aka bude kofar daga can ciki. Fuskar Mutumen dazun din nan ne da ke wacan part din da na baro, sai dai wannan karon akwai jallabiya a jikinsa, mamaki ya kama ni shi din ko kuwa su ma twins ne kamar Abdallah da Abdulhamid? Ko kuma wata hanyar ya biyo ta can ciki ya isa wannan part din? Sai da nai kamar ba zan masa magana ba, sai kuma wata zuciyar ta hana ni abunka da nama.
“Dan Allah yata nake nema aka ce min tana nan”
Be ce min komai ba ya fito daga falon ya sauko stairs din ya nufi gurin wata mota dake fake kusa da inda nake zaune.
“Tana nan ciki”
Ya fada bayan ya bude motar. Unkurawa nai na tashi na nufi kofar falon na shiga ina takawa a hankali saboda abu nake jin kamar zai zubo min. Na yi mamakin karamci da sakin fuskar da na tarar a fuskar Hajiyar gidan ina yin sallama ta amsa min tana min sannu da zuwa kamar ta san ni, Namra na ganina ta taso da sauri ta nufo inda nake tana dariya.
“Momy”
Rumgumeta nai na lumshe ido.
AHMAD POV.
Da gangan yake son ya shiga motarsa ya yi tafiyarsa saboda kar ma mahaifiyar yarinyar ta ga fuskar yi masa godiya ko yi masa wata maganar. Ji yake kamar ya fada mata bakar magana son ransa aka my wufintar da yar da tai amman ba shi da damar wannan tun da shi ba uban yar ba ne kuma ba shi da alaka da ita. Ko ba komai dai ya san hankalinta ya tashi tun da ga shi har tana zubar jini.
Tun kamin ya karasa gate aka bude masa gate din, ganin wani tsaye da mota a bakin gate din gidan yasa ya tsaya ya sauke gilashin motar yana kallon Abdulhamid da na shi gilashin yake sauke.
“Malam lafiya?”
“Wata yarinya muke nema aka ce tana nan gidan mun kira number da aka ba da a sanarwa muka jita a kashe shiyasa na zo”
“Kai ne mahaifinta?”
“No ni ne dai nake auren mahaifiyarta”
Abdulhamid ya amsa kai tsaye, sai Ahmad ya kalleshi da kyau sannan ya dauke kai.
“To ka tsaya nan za a fito maka da matarka”
Ya karasa yana kallon wayarsa. Number sis dinsa ya lalubo ya aika mata kira, in few seconds tai picking.
“Sis ki fadawa matarta mijinta yana jiranta a waje”
“Okay Ammn bro bleeding ta ke, ya dan jira ta shiga bandaki”
“Ki fada mata na ce”
Yana fadar haka ya kashe wayar ya karawa motarsa wuta ya hau titi, Abdulhamid na zaune cikin wata mai kama da Ahmad din ta budo karamar kofar gate din ta leko shi daga can cikin motar da yake zaune tace.
“Kai ne mijinta?”
Abdulhamid ya gyada mata kai.
“To ka dan jira ta fito tana bleeding amman ta dan shiga toilet ne”
“Ta ji ciwo ne?”
“No i think ta samu miscarriage ne... ”
Ta fada tana dan zare.
“Miscarriage...?”
Ya maimaita.
“Yes ban dai tabbatar ba, amman kasan idan am samu tashin hankali yana iya causing wannan matsalar, amman ba lallai ne ya zube duka ba, amman dai shawara ka kaita asibiti yanzu dan tabbatarwa”
Tun da ta fara yake kallon yadda take ta zuba masa zance har ta gama, daman daga ganinta irin yan matan nan ne masu surutun fadi baa tambaye ka ba.
“Okay”
Ya amsa mata zuciyarsa cike da mamaki, kai ta gyada masa sannan ta juya ta koma ciki, kamin ta isa falon wayar da ke hannunta tai ringing alamar kira. Soul mate ne rubuce a saman screen din, murmushi ne ya bayyana a fuskarta jikinta har rawa yake ta kara wayar a kunnenta sannan ta nufi wani bangare na gida cike da shauki tana amsa wayar.
HALIMATU POV.
Ban lura da jini dake zubo min ba har sai da na zauna a saman manyan cushion din dake falo, shi ma saboda Hajiyar ta yi magana ne.
“Subhanallahi kin ji ciwo ne?”
A lokacin da na duba sai na lura da jinin ya bata duk sawun kafata yake jini ya bata gurin. A iya sanina dai ban ji ciwo ba ban fadi ba balle na ce na ji ciwo ne, jini ba ta kafa yake min zuba ba ta cikina ne duk da kuwa da bana da tabbacin hakan domin ban ji zubowar komai ba sai jin alamar zubowar da na ji dazun ashe har ya zubo ban sani ba.
“A a ban ji ciwo ba”
Na amsa mata gabana na faduwa wani sabon tashin hankali na kusantata.
“Allah ya tsare idan ba miscarriage kika samu ba”
Hajiyar na rufe baki wata budurwar da ke zaune a dinning ta ta amsa da.
“Shi ne ma, kin san tashin hankali yana saka haka ko da ciki ya yi kwari ba re kuma ace yana sabo kuma.... ”
Bata karasa Hajiyar ta daka mata tsawa.
“Haba idan kin fara zubawa ba ki san ki tsaya ba? Shiyasa kike samu matsala da Yayanki kina da yawan magana”
Da hannu tai zip up din bakinta.
“Taso muje ciki ki gyara jikinki”
Naga karamci sosai a gurin matar nan babu kyama ta shiga da ni har cikin dakinta ta kai ni bandakin ta bani duk wani abu da nake bukata tun daga pad da pant da doguwar rigar da zan canja. Kamar kazar da kwai ya fashewa haka na fito daga bandaki jikina babu kwari na dawo falon a maimakon na zauna sai na yi tsaye kamar an dasa ni wasu sabbin hawayen na cika min ido.
“Baiwar Allah ki zauna mana yau masu aikin na mu basa nan balle akwai miki ruwa”
“Aa na gode sosai Hajiya, gida zan tafi yan uwana suna can suna ta neman Namra, na gode sosai da karamci na ji dadi da yata ta fada hannun mace mai karamci da son mutane kamar ki Allah ya saka da alheri”
“Babu komai Gwarzo za ki m godiya ai, muna zaune ya zo da ita sai fada yake wai kun wofintar da ita, dan Allah a rika kula”
“In-Sha-Allah”
Bayan na amsa mata, ta dauki wayarta dake gefen cushion din ta kira number da na ke zaton ta wacan mutumen ce.
“Za ta tafi da yarinyar nan”
Shine abunda na ji ta fada ban ji abunda ya fada mata ba, murmushi kawai na ga ta yi sannan ta aje wayar tana kallona.
“A kula dan Allah ina zuwa”
Tsakanin shigarta dakinta da fitowarta be wuce minti biyar ba ta mikowa Namra dake rike da hannuna abu a leda sannan ta shafa kanta.
“To bye bye jikata”