← Book details Gobe Na Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 48 OF 136

Sashe 48

Gobe Na Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Hannu na kai na dauki jakata na yi gaba abuna ina jin zuciyata kamar zata fito, na taki sa'a ina kawowa bakin gate din gurin Motar Abdulhamid na kunno kai a harabar gurin, sai da ya faka motar yana kokarin fita na nufi gurin motar na bude na shiga. Ba tare da yace da ni komai ba yai ma motar key muka kama hanyar gida.

__________________

Wai ni kadai na ke hango wani abu?🤔
Bari mu ga masu brain me kuke hangowa? 🤔
Tafdijam 😲 fatar dai kun shirya tafiyar domin yanzu aka fara..... 😊
7/21/21, 10:44 PM - Buhainat: *GOBE NA...*

By Khadeeja Candy

2️⃣6️⃣

Na yi mamakin ganin kawata Sa'adatu tana jirana a farkon shiga falona, ko wa nuna mata gidana ma oho ni har na manta da ita a cikin duniyar nan. Tun kam Abdulhamid ya faka motarsa ta mike tsaye tana ta kallon motarmu. Har ya faka motar ya bude ya fita be ce mim komai ba kamar yadda nima ban ce masa ba tun bayan shigowa a motar.
  Irin kallon nan da ta saba na yan bariki ta fara yi min kamin ta mikawa Abdulhamid shi tare da gaisuwa. Shi kuma ya amsa mata da fuskarsa ta rashin sakewa da mutane, ma'ana ba yabo ba fallasa ba kamar Aminu ba da idan ya ganta bakinsa har rawa yake wajen amsa mata gaisuwa.

“Wa nake ganin kamar Sa'adatu?”

“Ba kamar ba ce ni dince, tun da kin yadani ni ai na nemo ki”

Na yi dariya kamar yadda ita ma tai tana bin Abdulhamid da kallo har ya shige falon sannan ta kalleni.

“Shine angon na mu?”

“Eh shine”

Sai ta tabe baki har da wani lumshe ido ta bude.

“No wonder ake mana rowarsa, ashe kyakkyawa ne mai naira, gaskiya Halima kina dacen auren maza masu kyau da kudi, ko da yake kina da kyau ne shiyasa, da ni ke da kyaunki da yanzu na ci kudi”

‘Yes ina dacen aure a gidan hutun amman ba dan na hutu ba, sai dan na fuskanci wani kabulen’

Na fada a raina a fili kuma sai nai dariya na ce.

“A takaice dai mijina ya burge ki, gashi kuma shi ba kamar Aminu ba ne balle ku kulla”

Kallon rashin fahimta tai min tana yar dariya kamar ta ji kunya.

“Ban gane ba?”

“To ya za'ayi ki gane kuwa? Ke dai zo muje ciki”

Ina gaba tana biye da ni a baya har muka shiga falo. A kujerar da ke kusada kofar ta zauna ta zubawa Abdulhamid ido ni kuma na nufi two seater da yake zaune yana lasa waya na zauna a kusa shi, kamar wanda wani abun ki ya zauna kusa da shi haka yai saurin tashi ya nufi dakinsa, iyakar kokarin da nai na danne damuwar da na ji ne dan kar Sa'adatu ta zargi wani abu. Na tashi na shiga kitchen na dauko mata ruwa da lemun mu na hausa na kawo mata. Sai gashi ya sauko ko inda nake be kalla ba ya nufi kofa ya fice a uzurce.

“Halimatu wane irin zama kike da mijinki?”

Kamar daga sama na ji tambayar Sa'adatu tana mire baki.

“Kamar ya?”

“Ato kin san ni bakina baya shiru, na ga kamar akwai yar matsala a tsakaninku ko kuma shi haka rayuwarsa take?”

“Wai Sa'adatu sakin fuska yasa raini ya shiga tsakaninmu har ta kai kike iya fada min duk abunda ya zo bakin kina mu'amulantata yadda kika ga dama”

Sakin baki tai ganin kamar na taso mata da fada.

“Haba Hajiya ta, makano ne kawai zai shigo gidan nan yace be fahimci akwai rashin jituwa tsakaninki da mijinki ba, kuma wanda ya damu da kai ne ya damu da matsalar ne kawai yake nuna maka damuwarsa, kalle ki Halima Wallahi har kin fi auki a gidan Aminu dama da nan”

“Zuciyarki bata raya miki ko bana da lafiya ba? Babu abunda ya zo kanki sai rashin Jituwa?”

“Hmm yanzu dai Allah ya baki hakuri, mu bar wannan maganar, ya yaranmu ya su Amal?”

“Suna lafiya”

Na amsa mata ina kara hade fuska tare da dauke kai. Shiru ya shiga tsakaninmu kamin ta sake dauko wata maganar.

“Amman wai Halimatu ba kya kewar yayanki? Na ga Aminu ma da ke damu da yaya ba, yanzu yana ta shiga damuwar rashinku balle ke da kike tare da su kullum”

“Ke da kike iya barin Salim da Yusura kina zuwa wani gurin, ba tare da sanin irin kulawar da za a basu ba kika tafi hankalinki kwance har wani gari, balle ni da a gari daya ne kuma bautar Allah zan yi?”

“Ba ki gane ba ne, ni ai tafiyar kwana biyu ce ko uku, idan na dade na yi sati ke kuma aure ne fa, kin san wani lokacin baka sanin darajar abu sai idan baya kusa da kai kamar yadda Aminu yake a yanzu karki so ganin yadda ya koma abun tausayi duk inda ya zauna sai zancenki yake da na yaransa”

“Idan abu yana da muhimmanci a gurinka baka taba yarda ka rasa shi, tattalinsa kake, kana Ala ala kar ya subuce maka, domin duk ranar da ka rasa abun nan ka rasa shi kenan har abada, be kamata ki kawo min zancen wani namijin ba a gidan mijina, na dade da mantawa da Aminu ko wani abun daya shafe shi, ko da wasa karki sake min maganar Aminu”

“Ai na san Aminu ya kuntata miki amman Wallahi Halimatu yana cikin damuwar rashinki a yanzu, matar da ya aura ma ta rasa gane kansa”

“Wai Aminun ne ya turo ki yace ki zo ki fada min yana cikin matsala?”

Ta dan wara ido.

“Ahhh ni ina na ga Aminu da har zai ce min haka”

“Za ki gansa mana ke ai falkalsa ce, za ki iya sanin halin da yake ciki ko ma ya fada miki da kansa”

“Subhanallahi Haba Halimatu wannan bawa irin magana ce, na san dai ina raba wasu mazan, amman taya za ayi na raba mijinki Fisabilillahi, ni ba zan iya wannan cin amanar ba”

“Shiyasa a kike biyarsa kuna zuwa har wani garin kuna kwana, ke fa san komai da ke tsakaninki da Aminu, na samu ido ne kawai saboda na bar ku da Allah, shiyasa na tattara lamarinku na aje gefe, ba Aminu ba ko mai sunansa bana son ji yanzu balle shi din da kansa daga ke har shi na tsaneku tashi ki bar min gida”

Da sauri ta mike tsaye jikinta har bari yake.

“Kamar ba Halimar da na sani ba, da alama dai wani ya shiga tsakaninmu”

“Za ki fita ko sai na wulakanta ki”

Daukar jakarta tai ta juya da sauri ta fice tana waigena. Har bakin kofar gate na bita na tsaya sai da na tabbatar ta fice daga gidan sannan na rufe gate din na dawo cike da bacin rai.
  A lokacin dana zauna falo sai bacin ran abunda Abdulhamid yai min a gaban Sa'adatu ya tsaya min a rai, yanzu har ta kai Abdulhamid na kyamar zama a kusa da ni kuma ba zai iya boyewa a gaban mutane ba sai ya nuna? To ko dai ina dauke da cutar ne?ko kuma kiyayyar ce tai zurfi har haka a zuciyarsa. Ba yau kadai ba tun daga lokacin da abun nan ya faru na fahimci irin zaman da nake da Abdulhamid sai dai na yau yafi na ko yaushe.
Ba zan iya wannan zaman ba, sai kace an masa dole da ni ko kuma auren kiyayya mu ka yi? Idan har ya zai iya rabu da ni kai tsaye ba to ni zan iya neman rabuwa da shi domin rabuwar ce mafi a'ala a yanzu, zai fi samun natsuwa idan bana kusa da shi kamar yadda ni ma zan fi samun natsuwa idan na san bana tare da shi.
Ba Abdulhamid kadai ba ni inajin idan ma na rabu da shi ba zan sake auren wani namijin ba, domin na fahimcin gaba daya maza basa da kirki kansu kawai suka sani, ina ji a raina da ace ni ce ba zan iya yi ma Abdulhamid haka ba bazan iya rabuwa da shi ko nuna masa damuwa ba.

“Gaba daya mazan duniyar nan ba su da karki, gaba daya kansu kawai suka sani, su auri mace suna wulakantata suna yi mata yadda suka ga dama”

Na furta da karfi ina fashewa da kuka tare da dafe kai.

“Zan nemi saki, dole ne Abdulhamid ya sakeni, kuma ba zan sake aure ba, zan samu wani aikin zan rike yayana na cigaba da kula da su, ba zan sake yarda ciwon da namiji ya kashe ni ba, na gahi hakan nan wahalar ta isa haka...... ”

Wani abu na ji ya taso min ya tsaya min a kahon zuciya ya danne min numfashi, a guje naje na bude freezer na dauko ruwa mai sanyi na sha sannan na samu relief. Ji nai bana bukatar komai sai shan maganina shi kadai na ke sha ya lulani wata duniyar da nake mantawa da komai, gashi kwana biyun da nai ba sha ba har wani abu nake ji a cikin kaina kamar hayaki. Falon na dawo na bude jakata na dauko 2k na saka Hijab din da n cire na shiga bedroom na dauko keys na rufe gidan na nufi chemist din unguwar inda na saba siyen maganin.

AHMAD POV.

“Maganar gaskiya ba ka kyauta ba Gwarzo....”

Yayi saurin taron numfashinsa yana shafa kansa.

“Na sani.... Ni kaina bayan na mata fadan na ji cewar ban yi daidai ba, musamman da bata min tsawa ba kamar yadda nai mata, you know i hate mutum yai min tsawa”

“Ita ai ba laifinta ba ne laifin ma'aikantan gurin ne kuma.... ”

“Kuma What Rahim...? Sai son nanata maganar nan kake yi, i feel like na yi abunda be dace ba hakan be wadatar ba?”

Da mamaki Rahim yake kallon abokin na sa, daman can haka yake wani irin murdaden mutum ne mai wuyar sha'ani, shi ya kawo maganar abunda yai ma Halima, kuma ya fadawa masa be ji dadin yadda yai mata ba and now yana kokarin bleme Rahim akan ya bashi laifinsa.
Chapter 48 · 0% Book details