← Book details Gobe Na Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 69 OF 136

Sashe 69

Gobe Na Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read

Mun dade muna fira da ita kamin na bijiro mata da zancen mutumen nan da ke bibiyata, ita ma kanta ga tsorata da lamarin har ta ce mai reporting ma yan sanda saboda gudun abunda zaije ya dawo, kuma ban ki ta taba domin dan'adam abun tsoro ne a yanzu. Na dauki shawararta na zuwa bawa Abdallah hakuri dan haka daga gidanta sai na wuce gidansa kai tsaye da kwarin guiwa na. Na dade ina knocked din kofar falon kamin matarsa Suwaiba ta bude min, muna hada ido sai yanayinta ya sauya.

“Ah ah ahhh Abun kuma yanzu har cikin gida Haba Halimatu?”

Ina ta tunin abunda zan fada mata sai na ji muryar Abdallah yana amsa mata.

“Ni nace ta zo....”

Sakin kofar tai wanda hakan ya bani damar shigowa cikin falon, sai na hango shi zaune saman sofa sanye da Jallabiya laptop a jikinsa da alama wani aikin yake. Daga inda nake nai tsaye na kasa cewa komai sai ya aje laptop din ya nufo ya ratsa gefena ya fito daga falon, sai nima na juya na fice a harabar gidan muka tsaya ni da shi, yana ta kallona kamar zai cinye ni, ni kuma na gagara ce masa komai na gagara daga ido na kalleshi kwarjinsa da kimarsa ta cika min ido ga wani uban faduwar gaba da nake ji kamar mai jin tsoro.

“Kin lalata komai Halimatu, kin aikata kuskure, taya zaki auri Abdulhamid bayan kin san ina sonki? Why? Saboda ki musguna min? Haka Hajiyata ta fada min, kin san me? Da Hajiya ta fi kowa son ki saboda ina sonki kuma gana ganin kamar kina so na, daga lokacin da kika ja ra'ayi Abdulhamid a kanki sai ta lamarin ya lalace, gashi yanzu aurensa be haifa miki da mai ido ba, kuma ya haifar mana da matsala gaba dayan mu, baki tunani idan za ki yi abu Halimatu baki tunani.... ”

Ya fada yana hada duka hannayensa ya daki kaina. Dagowa nai na kalleshi idona taf da hawaye zan yi magana ya tari numfashina.

“Sai kuka da an miki abu sai kuka.. ”

Yayi saurin juyawa sai kuma ya juyo.

“Ya akai? Miyasa kika zo nan?”

Na fara matsar yatsuna ina hawaye.

“Zuwa nai na baka hakuri akan abunda na fada maka a asibiti wanda ya saka kake fushi da ni....”

“Yanzu kin fara jin son na a cikin ranki? Shiyasa har kika damu da fushin da nake da ke? Bayan komai ya lalace?”

Ya juya ya fara tafiya.

“Ka yi hakuri dan Allah Wallahi ba abunda ke raina kenan ba”

Juyowa yai ya kalleni

“Ni bana fushi da ke ba zan iya fushi da ke ba....”

Haka kawai ya fada min ya cigaba da tafiyarsa har ya shige cikin falon. Ni kuma na juyo hawaye wasu na bin wasu na fito daga cikin gidan, ina tafiya ina jin ana bina a baya a lokacin sa na waiga sai sake arba da fuskar mutumen nan da ya saba bibiyata. Faka motarsa yai ya fito ya miko min handkerchief.

“Pls...”

“Waye kai? Me kake nema a gurina? Idan ma sace ni za kai ni bani da wanda zai karbo ni, idan kuma yarana zaka sace ban da kudin karbo su”

Murmushi na gani a kyakkyawar fuskarsa.

“Zaki iya shiga motana na kai ki gida, sai ki aminta da ni”

“Ba zan shiga ba, miye hadi n dake kai rista ni musulma”

“Soyayya ai babu ruwanta da addini, haka dai aka fada min mai irin addinin suna da kirki da karanci ba kamar yadda na same ki ba”

“Wani yayi amfani da hakuri na ya cutar da ni, wani yayi amfani da soyayyata ya cutar da ni, kai kuma kana son kai amfani da addinina ka cutar da ni, to ba zan yarda ba ban yi kowa komai ba ba zan yarda ayi ta cutar da ni ba”

Ina fada masa haka na cigaba da tafiyata.

“Idan cutar da ke na zo yi kar Allah ya bar ni da raina a yau”

Tsayawa nai cak kamin ya juyo na kalleshi da mamaki.

“Kai kuma daga ina?”

Matsowa yai kusa da ni ya miko min hannunsa.

“Sunana Abraham akwapo”

Tsayawa nai kallon hannunsa sake sanye da manyan zobuna sai dai ba irin wadanda can ba ne na zinari wasu kala ne na dabam sai dai duka alphabet dinsu A ne. Sai kuma na kalli fuskarsa.

“Ni musulma ce miyasa kake bibiyata? Zan kai report dinka a gurin police yau”

“Okay”

Ya juya ya shiga motarsa na yi zaton tafiya zai yi amman sai ya fito rike da wani kamin littafi yai rubutu akai ya mika min.

“Sunana Abraham ga number motata nan da number wayata da address din gidana ko da sun bukaci gani na”

Ni kan a tsaye da nake mamaki ya kusan kashe ni.

“Waye kai....?”

Sai yai murmushi ya saka hannayensa aljihu.

“Za ki ba ni damar kasancewa abokinki?”

Shiru da nai ban bashi amsa ba ban kuma daina masa kallon mamaki ba yasa shi sake sakar min murmushi.

“Ina mika kyakkyawar gaisuwata a gurin yaranki”

Sannan ya shiga motarsa yai mata key ya bar ni a gurin tsaye da mamaki....

_____________

Wake irin tunanin da na ke 🤔
7/21/21, 10:45 PM - Buhainat: *GOBE NA...*

By Khadeeja Candy

3️⃣6️⃣

Na kasa jefarda takardar kuma na kasa fadawa kowa cewar ya bani takardar kamar yadda na kasa fadawa yan sanda. Shi kuma be fasa chusa kansa a cikina ba, har kara ma da bibiyata kawai yake amman a yanzu har yarana yake yi ma siyayya ta kudi mai yawa ya kai musu a scul a gida kuma ya aiko min da ita, a kullum ina fargabar idan Mama ta tambayi wanene shi wa zan fada mata ba? Bayan karyar da nai mata cewar wani ne dana hadu da shi yake min haka yai ma su Namra, amman idan aka samu akasi yarana ko kuma Mama da kanta ta ganshi fa? Duk wanda ya gan ni da kafiri zai yi mamaki abunda ya hada ni da shi ina diyar musulmai.
Sai dai a yadda na fahimta kamar shima yana gudun mutane domin baya min magana a inda yakr ganin jama'a da yawa, sai idan ina a kebance kamar idan zan hau napep ko na sauka ko zanje wani gurin sai kuma da dare zai aika yace ana min sallama. Duk kuwa da ban tana fitowa da sunan amsa sallamar da yake min ba, hakan be hana shi aiko min lokaci zuwa lokaci ba, kamar yadda yake yawan bibiyata yana rokon na saurareshi.
Ni kuma na kasa saurarensa saboda bana jin aminci a tare da shi wata kila saboda ba addinin mu daya da shi ba oho, sai dai a yadda na lura yana da kamun kai da taka tsantsan da kuma natsuwa wacce ba ko a musulman mu ba kowa kake samu da wannan ba.
  Ba ni da wata fargaba a yanzu sai ta abubuwa uku,wannan Abraham din sai kuma Aminu wanda shi ma ya saka ni a gaba da yawan bugo min waya da sunan zai gaisa da yayansa tun yana kira ina dagawa na bawa yaransa har ta kai yanzu idan ma ya kirani sai dai na mika musu wayar su su yi magana da shi, hakan kuma be hana idan ya kare magana da su yace su ba ni wayar idan ni kadai ce ko kuma da kanen sai na yanke kiran idan a gaban Mama ne kuma na kan dauka saboda ta gargade ni cewar na daina kin karbar wayarsa ko dan darajar yarana, ina yi mamata biyaya ne kawai saboda ina gudun bacin ranta gudun kar tace ban dauki shawararta ba, amman har ga Allah bana kaunar jin sunan Aminu ma balle jin muryarsa, shi kuma yanzu har wani zillon rashin kunya yake domin wani sa'in har cikin gida yake shigowa ya gaishe da Mama da Baba sannan ya fita, ga wata bakar al'ada da ya tsiro ta daukar yaran yana tafiya da su gidansa ko wani gurin daban su wuni can sai dare zai kawo su gida. Idan na nuna zan hana sai Mama tace min ba haka ba. Wani lokacin sai dai nai ta jin haushin a zuciyata kawai amman ban isa na nuna a fili ba saboda kar mama tace saboda ita nake yi.
  Na tattara komai a yanzu na aje a gafe, babu da bukakata da damuwa kamar abu na ukun nan wato neman aiki, duk inda naji wata ma'aikata ko wani kamfani sai na mika takarduna, sannan na saka addu'a a gaba nai ta yi ko Allah zai saka a dace.!
Chapter 69 · 0% Book details