← Book details Gobe Na Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 7 OF 136

Sashe 7

Gobe Na Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

“Canjin jikina kadai be isa ya saka ka wulakanta ni ba, ban sani ba ko na aikata maka wani laifi mai girma da ban sani ba, ko kuma a sani ni ina ganin kamar ba laifi ba ne, dan Allah ka yafe min Abban Namra, na kasa sabawa da zamankewar auren da muke, na kasa fahimtar juya min baya da kai ka yafe min idan wani abun nai maka dan girman Allah”

Be ce min uffan ba har ya gama cin abincin ya sha ruwa sannan ya dago kansa ya kalleni ya ce.

“Indai kina son mu shirya da ke, to ki aje aikin nan babu yadda za ayi kina aiki kina mu'amala da wasu maza a waje ni kuma kina zaune a gidana kawai a matsayin mata, gashi nan har idonki ya fara zarewa kina fita ba tare da kin tambaye ni ba abunda baki saba ba, Allah kadai yasan kalolin mazan da kike gamuwa da su”

“Ka rika kyautata min zato, ko da yaushe kana yawan cewa ina mu'amala da wasu mazan a waje, kana yawan ganin kamar ina aikata fasikanci ne da aurena, ba zan iya aikata zina ba ba zan iya da hakki hudu ba, naka na iyeyena na yayana da kuma na Ubangijina, ina aikin nan ne saboda daukewa kaina wasu lalurorin kai ma ka sani, muna da hidima da yawa a gidanmu iyayena ma suna bukatar taimakona”

“Dauke ma kanki wasu lalurorin? Miye bana miki ci ko sha?”

“Ba ci da sha ne kadai abunda mace take bukata a gurin mijinta ba Abban Namra, akwai kulawa da wasu bukatun na yau da kullum da kuma ta yan'uwa da iyaye, amman indai har aje aikin nan zai saka ka shirya da ni mu koma muna zama da juna cikin amince da kauna, zan aje sai na kama sana'a”

“Aa idan kin san idan kika aje aikin wata sana'ar zaki kama kar na ki aje aikinki daman ai ban isa da ke ba”

Kasa cewa komai nai har kuma lokacin hawaye nake, Aminu wani irin murdadden mutum ne wanda baya fahimtar abu idan baya so ba. Taya zai hanani aiki kuma yace ba zan yi sana'a ba, kuma ba zai dauke min duka lalurorina ba?

“Ga cikin nan na ce miki a zubar kin ki yarda, haba wane irin abu ne haihuwa hudu a shekara goma sha biyu, ai gashi nan duk kin bude kin wani tsufa, kuma yanxu ana ta abinci ai ba ta haihuwa ake ba ina zan iya da lalurar yara biyar a yanzu, idan kin yaye ki sake daukar wani kuma? Haba abu ai yayi yawa”

Ya fada min kai tsaye, sai a yanzu na gane dalilin kauracewa shimfidata da Aminu yai. Mikewa nai tsaye na juyo da zimmar fitowa na baro masa dakin, sai na ji ya ce.

“Zanje Kaduna gobe gurin wani aiki, wata kila nai kwana hudu ko sati”

Ban juyo ba ban kuma ce masa komai ba, na baro masa dakin na dawo falo na zauna na rungume hannayena ina wani abun a zuciyata, idan nace zan kashe aurena hakika ban san wane hali yarana zasu fada ba, ban kuma san wane kalar mijin zan aura ba, idan kuma na cigaba da zama da shi zan saka kaina cikin damuwa ne kawai marar misaltuwa, domin ko a yanzu idan aka auna na san ba za a sara samuna da hawan jini ba, shekara goma sha daya ba yau ko jiya ba ne.

“Idan kika cigaba da zama da mutumen nan, hawan jini ne zai kama ki, zaki kai wani mataki da baki iya komai daga lokacin kin tashi aiki, ba zaki iya tsinanawa kanki komai ba, ban ga dalilin da zai saka ki yi hakurin zama da mutunen nan ba wai wani zaman yayanki shi be san da yayan ba ne yake musguna miki? Ko ke kadai aka dorawa hakkin kula da su”

Dafe kaina nai tunawa da maganar da Abdallah yai min akan Aminu, wani bangaren yana da gaskiya idan na ce nai hakurin zama ni ce zan cutu idan kuma na bar gidan still zan cutu da rashin yayana a kusa da ni.

“Ko wane aure yana da kalubale Halimatu, ki yi hakuri ki ta addu'a ki karbi kaddararki da hannu biyu, idan kin bar Aminu kina da tabbacin shi mijin da za ki aura ba kamar Aminu ba ne? Idan ba ki hakurin zama da uban diyanki ba ba zaki iya hakurin zama da kowa ba, kuma daga haka za a fara kirga miki aure”

Haka Mama take yawan fada min idan ina mata complain din Cewar na gaji da zaman auren nan. Yanzu kumaga sharadin Aminu na aje aiki idan har ina son ya shirya da ni, ba ni da tabbacin idan na aje aiki zai kula ni domin tun kamin aiki ya fara min wannan wulakancin, idan kuma na bar aikin wasu abubuwan da nake iya yi ma iyayena ba zan iya daukar dawainiyar ba, wasu abubuwan da nake iya yi ma kaina dole za su gagareni. Haka dai nai ta tunanina kala kala har kusan biyu na dare sannan na tashi na nufi dakina, wutar dakin na kashe sannan na hau saman gadon na kwanta na lumtse idona ba dan ina jin bachi zai dauke ni ba. Dilllll wayata tai kara alamar shigowar sako bude idona nai na ka hannuna saman aljihun gadon na dauki wayar ina dubawa.

_Ki yafe min dan Allah, na kasa bachi saboda na san yau na bata miki rai, amman ban yi zimmar daba ki da wata manufa ba, ina ganin kamar ni da ke mun zama daya ne, kuma ni na dauke shi a matsayin wayewa ba wai dan wani abun ba, sai dai naga kamar ranki ya bace ki yi hakuri dan Allah ki shafa min kan yaran nan ki gaishe su_

_Kabeer_

Ina gama karant sakon hawaye ya wanke min fuska, wani wanda ba mijina ba shi yake damuwa da fushi da bacin raina har ya gaishe da yarana. Rumgume wayar nai a kirjina ina jin wani irin kyautata da ganin kimar Kabeer.

__________________

Anya Halimtu zata aje aikin kuwa? Ko kuwa dai zata zabi zama da Aminu a haka? Wai mi yake damun Namra ne? 🤔
7/20/21, 8:29 AM - Buhainat: *GOBE NA...*
_My Tomorrow_

By Khadeeja Candy

5️⃣

Iyayena na gari abun alfahari idan kai dace da iyaye hakika ka yi babban dace, bayan su kuma sai miji shi ma idan kai dace da miji na gari ka samu ingantacciyar rayuwa idan Allah yai maka falala ka sake dace da yayana nagari ko kai an gama maka komai a rayuwarka. Al-hamdulillah ban san yanda tarbiyar yarana zata kasance ba bayan girmansu amman ina fatar su tashi akan tafarkin da na dora su akai, idan na samu haka ko da shi kadai zan iya gode Allah, duk kuwa da na san babbar jarabawar duniya ita ce ta rashin dacen miji.
Ban taba jin kewar budurci ba irin yau, ji nake kamar ace yau ni din budurwa ce da na sake zaben wani mijin ba Aminu ba, na kwana rungume da sakon wani a kirjina saboda rashin kulawar mijina, da ace na san rayuwa zata sauya min haka bayan aure da na zabi zama a budurcin har na bar duniyar nan, bachi be dauke ni da wuri ba, haka kuma ban dade ina bachin ba na farka, kaina har wani nauyi nake jin yana min ga wani uban ciwon zuciya da nake jinsa har cikin kashin bayana.

After sallah nai addu'o'in da na saba sannan na nufi kitchen domin hada ma yarana abincin zuwa makaranta, misalin bakwai saura na safe ya shigo kitchen din rike da jakarsa sai ya tsaya a jikin kofa, ni kuma nai kamar ba san da mutum a gurin ba har sai da yai gyaran murya sannan na juyo na kalleshi

“Ina kwana?”

“Lafiya kalau, ga wannan ki rike da wuri zan tafi saboda bana son rana yai min”

Ya fada yana miko min dubu uku, kallon kudin nai na girgiza masa kai.

“Ka kara akwai kudin da za su ishemu har ka dawo”

Be ce min komai ba, ya aje kudin saman kitchen cabinet ya juya, a karon farko yau zai tafi wani gari amman na kasa ce masa Allah ya tsare sai binsa da nai da kallo. Juyowa yai ya kalleni.

“Da ki min addu'a da karki min duka uwarsu daya ubansu daya, sai abunda Allah ya rubuto zai same ni, mugun nufinki ya koma kanki”

Yana fadar hakan ya juya ya fice, ni kuma nai murmushi ina jin bakar maganar da ya fada min har cikin raina. Kaina na daga ina kallon kitchen din yadda tsarin gidanmu yake da siffar masu arziki ko kyautar rabin miliyan nai ba za ayi mamaki ba saboda ana ganin mai arzikin nake aure, amman yau zai yi tafiya saboda bakar keta irin nasa ya dauki dubu uku ya bani.
Dauke kai nai domin na san idan na ce zan cigaba da tunani zan iya faduwa a gurin ko kuma wani abun ya same ni.

Bakwai da rabi na shiga na tashi yarana nai musu wanka sukai alwala sukai sallah sannan na shirya su cikin uniform dinsu na makarantar boko ban da Namra da har yanzu bachi take jikinta kuma da dan zafi. Kasa suka sauko suka karya tare da Amal sannan na shiga dakina na saka hijab na fito na saka su gaba muka nufi gate. Sai dai mun yi sa'ar haduwa da mijin Hajara kamar jiya.

“Ina Namra yau?”

“Bata jindadi”

“Subhanallahi Allah ya sauwake”

“Amin”

Sai ya saka yaran a motarsa har da Amal suka tafi, daman ta saba idan yan kwarai suna kanta tana yarda ta bisu su tafi idan ya dawo sai ya kaita gurin Hajara.
Juyowa nai na dawo cikin gidan, sai na shiga dakina nai wanka ina cikin shiryawa wayarta tai ringing, dauka nai na duba sai ga number Abdulhamid hakan yasa ni picking na kara a kunne.

“Hello”

“Good morning Halima ya gida ya yaran?”

“Lafiya kalau”

“Na miki sako ta whatsapp wai baki hau ba so i decided na kira ki”

“Lafiya dai?”

“Account number dinki na k so dan Allah zan dan saka miki wani a ciki”
Chapter 7 · 0% Book details