Sashe 107
Gobe Na Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
“Zata iya yin komai wannan yarinyar da kake gani, ni sam ban yarda da ita ba ma”
“Babu hannunta a cikin nan, kuma na fada miki ki bari nan da kwana biyu idan ba mu ga wani abun ba, sai mu fada musu wanda muke zargi”
“To ko ma dai minene Allah ya bayyana shi”
“Amin”
Yayi kusan awa daya a dakin sannan yai mata sallama ya fice. Aiko kamar fitarsa take jira ta fito falo ta labartawa yan'uwanta abunda ya faru dukansu sun cika da mamaki.
“Wannan maganar ai ba abar a kyale ba ce”
Cewar Hajiya Altine, sai Hajiya ta amsa ta tana ware hannu.
“Ni ma shi na gani ban zafafa abun ba ne saboda a gabansa ne, na san zai iya shiga cikin lamarin tun da uwarsa ta shigo ciki, yadda kika san ta wanke gaba ta zuba masa ya shanye haka yake da ita, ko sunanta baya son a ambata a wani abu”
Hajiya Rukaiyah ta dora da.
“To waya sani, ko wani abun tai masa, amman duk yadda akai ta san inda Abdulhamid yake”
“Nima shi nake tunani, saboda bakinciki zai yi aure gashi ita ba tai ba zai iya sawa tace shi mutunen ya sace shi, ko kashe shi ma zasu iya yi, ko kuma su masa wani illar, kuma Allah kadai yasan gaskiyar lamarin nan wata kila ma daman can ta san abokinsa nw ta aure shi dan su kashe shi su ci dukiya Allah ba basu sa'a ba, Allah ya gani ko da akai auren nan ba zan ce miki yaron nan yana son Halimatu ba, be taba nuna min ba, kuma a lokacin ma ta neman lafiyarsa yake amman sai ya zo min da maganar aure daga sama, ban san yadda akai ta janyo hankalinsa ba ma, kamar abun magani, cikin kankanen lokaci akai komai”
“Kin san abunda za ayi? Ko yanzu ita ya kamata a kama, idan ta ji wuya dole ta fadi inda shi Abraham din yake da Abdulhamid din, wannan ai ba maganar bari ba ce”
Cewar Hajiya Altine tana tabe baki alamun mamaki ya gama cikata.
“To yanzu a kira Yusuf a fada masa, gobe tun da farar safiya a doka masu sammako a kamo yar iskar, yarinya ta same mana fitina a cikin dangi”
Hajiya ta fada tana kara yamutsa fuska. Hajiya Altine ta ce.
“Haka za ayi, daman Yusuf din ya fada min ai akwai inda suke saka mutum su saka masa wata hula duk iskancinsa sai ya fadi abunda yake gaskiya, bari na kira shi....”
Ta karasa tana danna number dan nata rai a bace, Hajiya kuma ta zauna saman cushion tana ta rawa da kafa tana kara kashe ido, babu komai a zuciyarta sai tsanar Halimatu.
HALIMATU POV.
Na iso gida cikin wani yanayi da ban taba samu kaina ba, ni dai ba zan ce ina son Ahmad ba, haka kuma bana kin shi, sai dai a yau kalamansa sun kashe min jiki sosai.
Mama ta yi mamakin ganin na dawo gida da wuri bayan a a lokacin na saba dawowa ba sai yamma, karya nai mata na ce mata yau babu aiki da yawa shiyasa aka tashemu. Har na yi kamar na labarta mata abunda ya faru da Abdulhamid sai kuma wata zuciyar ta hana ni, domin na san ita ma din zata zargi Ahmad da saka a ka masu kamar yadda nima zuciyata take zargi, kuma zata iya cewa zatai wa Hajiya jaje gudun kar ace bata ji ba idan taje kuma dole zata bada labarin abunda na fada mata ne, idan kuwa Hajiya ta ji haka zata zarge ni, so rufin asirina kawai nai shiru da bakina na bar abun a cikina, har sai ya bayyana.
Babu irin tunanin da ban yi ba a ranar har cikin daya ina abu daya, dan son gano abunda Abdulhamid da Abraham suke aikata marar kyau, idan na saka wannan na kwance wacan na kulla wannan, sata yake? Tare da Abraham din suke fashi? Ko kuma wata sana'ar ce dabam? Duk wani mugun aiki da zan kwatanta Abdulhamid da shi sai na ga kamar ba zai iya aikatawa ba, wata kila ma dai Abraham din shari yai masa saboda kar ya cutu shi kadai, domin ko a lokacin da na ke aurensa ban ga wata alama da ta nuna rashin gaskiya a tare da shi ba, duk da yake baka iya gane gaskiyar mutum mai boyo, Abdulhamid kuma yana daga ciki irin mutanen nan da suke boye abu, soyayyar da muka da shi ma a lokacin da nake budurwa a boye muka yi saboda baya son kowa ya sani.
Haka dai nai ta sakesake na har dare raba ban yi bachi ba, domin tun ina jin alamar bachi bachin a idona har ya fitar min gaba daya, tashi nai na fito bakin balcony na zauna ima ta kallon taurari kamar mai kidayarsu, babu komai a tare da ni sai tunani kala kala. Can ciki ciki na ji wayata dake kan drawer tana vibration alamar kira yana shigowa wayata. Sai na tashi na koma dakin, hannu na kai na cire carjin sannan na dauki wayar sai nai arba da number Ahmad, gabana ne ya fadi kamin mamaki ya rufe ni, miyasa ya kira ni yanzu? Abunda be tana ba, ko kirana a gida balle a wannan lokacin da agogon wayata ya nuna karfe biyu saura, to ko dai fada min zai yi an sako Abdulhamid? Ko kuma wani abun zai fada min dabam, kiran na daf da tsinkewa nai picking na kara a kunne sai dai ban yi magana ba sai da na fito balcony. Ina ta jiran yai magana be ce min komai ba, idan na duba wayar sai na ga kiran na tafiya har sai da na gaji da kaina na ce
“Hello”
“Lims, kema kin kasa bachi kamar ni kenan?”
“Eh”
“Kin san me? Dakina yai min ba dadi sai na fito na zauna harabar gida sai kidayar taurari nake, yanzu kuma haka nan kawai na ji ina bukatar jin muryarki, duk ban yi zaton za ki dauka ba”
Ya fada da murmushin da zan iya jiyowa, kana jin muryarsa ka san ransa kal yake fa farinciki. Na yi shiru ban ce masa komai ba.
“Fada min miya hanaki bachi?”
“Ni ma ban sani ba, na samu kaina da kasa bachin ne”
Murmushinsa mai sauti ne ya daki dodon kunnena.
“To je ki kwanta, so that's ki tashi da wuri i need to see early in the morning”
“Okay”
“Sweet dreams Lims, ki rufe idonki ki tuna duk wani beautiful memories we share together za ki yi bachi, kuma ina rokon ki yi mafarkina take good care of yourself for me pls”
Be jira abunda zan ce ba ya yanke wayar, for the first time na samu kaina da shiga calls list na kurawa number ido for no reason, before murmushi ya biyo fuskata, sai da na sake kallon taurarin sannan na tashi na koma daki na kwanta. Lumshe ido nai thinking all the good memories we share together kamar yadda ya fada, babu abunda na fi tunawa kamar tears din da muka share with one tissue, and location da yai maganar wai ko dai ina son sa ne? Samun kaina nai da murmushi, kamin wani lokacin bachi yai gaba da ni.
Na farka raina Fresh har wani shauki nake ji, domin ina aiki ina yan wake wake na, ina cikin shiryarwa su Namra su tafi makaranta muka ji muryar wata mace wacce hausa bata isheta sosai ba.
“Dan Allah wacece Halima”
Zumut nai na fito ance son kira kamar bazarawa, na amsa da cewar ga ni ina kallon matan ashe ba daya bace sai dai dukansu su biyun suna sanye ne da uniform din yan sanda. Kamar jira suke na amsa suka nufo inda nake suna fadin.
“Zamu je da ke office din mu ki amsa wasu tambayoyi”
“Me nai?...”
Ban gama rufe baki ba suka rika ni muka fara ja in ja da su, da gudu Hafiza ta zo ta buge hannu police din ta hau ta da masifa.
“Mi tai muku? Haka kawai za ku shigo cikin gida mu kamata? Wace duka ta baku izinin shiga gidan mutane anyhow”
Police din ta nuna ta a fusace.
“Ke mahaukaci ki san abunda kike yi, karki ce zaki taba police zan ci mutuncinki, marar kunya kawai”
“Yes louder pls mu nan gidan sai mu kashe mutum ba komai ba ne a gurin mu, dan haka mun fiki tantiranci”
Cewar Hafiza tana zare mata ido kamar ba da police take fada ba. Sai da Mama ta daka mata tsawa sannan ta umarce da ta dauko min Hijabina.
“Amman Mama...”
Hafiza bata gama fadar abunda zata fada ba Mama ta tari numfashinta.
“Dauko mata Hijabinta na ce, duk inda za a je indai tana da gaskiya gaskiyarta zai fito da ita, Allah yana tare da mai gaskiya”
Ranta be so ba taje ta dauko min Hijabi na karba na saka, sai da muka fara tafiya sannan yarana suka fashe da kuka, ba ma kamar Amal wacce ta biyoni har kofar gida tana kiran sunana.
“Momy.....”
Ban san lokacin da hawaye ya wanke min fuska ba, ko ba komai sun tozarta ni, sun saka ni a motar police patrol, duk wanda zai gan ni a ciki dole na zargi wani laifin na aikata, duk kuwa da kasancewar ban san abunda nai ba, ga kuma mutane da suka tara mana a kofar gida, domin motar har da maza sai suka tsaya daga waje. Ina jin lokacin da Inna take tambayatar wane station ne za a kai ni sai mai tukin motar ya amsa mata da.
“State CID”
“Babu hannunta a cikin nan, kuma na fada miki ki bari nan da kwana biyu idan ba mu ga wani abun ba, sai mu fada musu wanda muke zargi”
“To ko ma dai minene Allah ya bayyana shi”
“Amin”
Yayi kusan awa daya a dakin sannan yai mata sallama ya fice. Aiko kamar fitarsa take jira ta fito falo ta labartawa yan'uwanta abunda ya faru dukansu sun cika da mamaki.
“Wannan maganar ai ba abar a kyale ba ce”
Cewar Hajiya Altine, sai Hajiya ta amsa ta tana ware hannu.
“Ni ma shi na gani ban zafafa abun ba ne saboda a gabansa ne, na san zai iya shiga cikin lamarin tun da uwarsa ta shigo ciki, yadda kika san ta wanke gaba ta zuba masa ya shanye haka yake da ita, ko sunanta baya son a ambata a wani abu”
Hajiya Rukaiyah ta dora da.
“To waya sani, ko wani abun tai masa, amman duk yadda akai ta san inda Abdulhamid yake”
“Nima shi nake tunani, saboda bakinciki zai yi aure gashi ita ba tai ba zai iya sawa tace shi mutunen ya sace shi, ko kashe shi ma zasu iya yi, ko kuma su masa wani illar, kuma Allah kadai yasan gaskiyar lamarin nan wata kila ma daman can ta san abokinsa nw ta aure shi dan su kashe shi su ci dukiya Allah ba basu sa'a ba, Allah ya gani ko da akai auren nan ba zan ce miki yaron nan yana son Halimatu ba, be taba nuna min ba, kuma a lokacin ma ta neman lafiyarsa yake amman sai ya zo min da maganar aure daga sama, ban san yadda akai ta janyo hankalinsa ba ma, kamar abun magani, cikin kankanen lokaci akai komai”
“Kin san abunda za ayi? Ko yanzu ita ya kamata a kama, idan ta ji wuya dole ta fadi inda shi Abraham din yake da Abdulhamid din, wannan ai ba maganar bari ba ce”
Cewar Hajiya Altine tana tabe baki alamun mamaki ya gama cikata.
“To yanzu a kira Yusuf a fada masa, gobe tun da farar safiya a doka masu sammako a kamo yar iskar, yarinya ta same mana fitina a cikin dangi”
Hajiya ta fada tana kara yamutsa fuska. Hajiya Altine ta ce.
“Haka za ayi, daman Yusuf din ya fada min ai akwai inda suke saka mutum su saka masa wata hula duk iskancinsa sai ya fadi abunda yake gaskiya, bari na kira shi....”
Ta karasa tana danna number dan nata rai a bace, Hajiya kuma ta zauna saman cushion tana ta rawa da kafa tana kara kashe ido, babu komai a zuciyarta sai tsanar Halimatu.
HALIMATU POV.
Na iso gida cikin wani yanayi da ban taba samu kaina ba, ni dai ba zan ce ina son Ahmad ba, haka kuma bana kin shi, sai dai a yau kalamansa sun kashe min jiki sosai.
Mama ta yi mamakin ganin na dawo gida da wuri bayan a a lokacin na saba dawowa ba sai yamma, karya nai mata na ce mata yau babu aiki da yawa shiyasa aka tashemu. Har na yi kamar na labarta mata abunda ya faru da Abdulhamid sai kuma wata zuciyar ta hana ni, domin na san ita ma din zata zargi Ahmad da saka a ka masu kamar yadda nima zuciyata take zargi, kuma zata iya cewa zatai wa Hajiya jaje gudun kar ace bata ji ba idan taje kuma dole zata bada labarin abunda na fada mata ne, idan kuwa Hajiya ta ji haka zata zarge ni, so rufin asirina kawai nai shiru da bakina na bar abun a cikina, har sai ya bayyana.
Babu irin tunanin da ban yi ba a ranar har cikin daya ina abu daya, dan son gano abunda Abdulhamid da Abraham suke aikata marar kyau, idan na saka wannan na kwance wacan na kulla wannan, sata yake? Tare da Abraham din suke fashi? Ko kuma wata sana'ar ce dabam? Duk wani mugun aiki da zan kwatanta Abdulhamid da shi sai na ga kamar ba zai iya aikatawa ba, wata kila ma dai Abraham din shari yai masa saboda kar ya cutu shi kadai, domin ko a lokacin da na ke aurensa ban ga wata alama da ta nuna rashin gaskiya a tare da shi ba, duk da yake baka iya gane gaskiyar mutum mai boyo, Abdulhamid kuma yana daga ciki irin mutanen nan da suke boye abu, soyayyar da muka da shi ma a lokacin da nake budurwa a boye muka yi saboda baya son kowa ya sani.
Haka dai nai ta sakesake na har dare raba ban yi bachi ba, domin tun ina jin alamar bachi bachin a idona har ya fitar min gaba daya, tashi nai na fito bakin balcony na zauna ima ta kallon taurari kamar mai kidayarsu, babu komai a tare da ni sai tunani kala kala. Can ciki ciki na ji wayata dake kan drawer tana vibration alamar kira yana shigowa wayata. Sai na tashi na koma dakin, hannu na kai na cire carjin sannan na dauki wayar sai nai arba da number Ahmad, gabana ne ya fadi kamin mamaki ya rufe ni, miyasa ya kira ni yanzu? Abunda be tana ba, ko kirana a gida balle a wannan lokacin da agogon wayata ya nuna karfe biyu saura, to ko dai fada min zai yi an sako Abdulhamid? Ko kuma wani abun zai fada min dabam, kiran na daf da tsinkewa nai picking na kara a kunne sai dai ban yi magana ba sai da na fito balcony. Ina ta jiran yai magana be ce min komai ba, idan na duba wayar sai na ga kiran na tafiya har sai da na gaji da kaina na ce
“Hello”
“Lims, kema kin kasa bachi kamar ni kenan?”
“Eh”
“Kin san me? Dakina yai min ba dadi sai na fito na zauna harabar gida sai kidayar taurari nake, yanzu kuma haka nan kawai na ji ina bukatar jin muryarki, duk ban yi zaton za ki dauka ba”
Ya fada da murmushin da zan iya jiyowa, kana jin muryarsa ka san ransa kal yake fa farinciki. Na yi shiru ban ce masa komai ba.
“Fada min miya hanaki bachi?”
“Ni ma ban sani ba, na samu kaina da kasa bachin ne”
Murmushinsa mai sauti ne ya daki dodon kunnena.
“To je ki kwanta, so that's ki tashi da wuri i need to see early in the morning”
“Okay”
“Sweet dreams Lims, ki rufe idonki ki tuna duk wani beautiful memories we share together za ki yi bachi, kuma ina rokon ki yi mafarkina take good care of yourself for me pls”
Be jira abunda zan ce ba ya yanke wayar, for the first time na samu kaina da shiga calls list na kurawa number ido for no reason, before murmushi ya biyo fuskata, sai da na sake kallon taurarin sannan na tashi na koma daki na kwanta. Lumshe ido nai thinking all the good memories we share together kamar yadda ya fada, babu abunda na fi tunawa kamar tears din da muka share with one tissue, and location da yai maganar wai ko dai ina son sa ne? Samun kaina nai da murmushi, kamin wani lokacin bachi yai gaba da ni.
Na farka raina Fresh har wani shauki nake ji, domin ina aiki ina yan wake wake na, ina cikin shiryarwa su Namra su tafi makaranta muka ji muryar wata mace wacce hausa bata isheta sosai ba.
“Dan Allah wacece Halima”
Zumut nai na fito ance son kira kamar bazarawa, na amsa da cewar ga ni ina kallon matan ashe ba daya bace sai dai dukansu su biyun suna sanye ne da uniform din yan sanda. Kamar jira suke na amsa suka nufo inda nake suna fadin.
“Zamu je da ke office din mu ki amsa wasu tambayoyi”
“Me nai?...”
Ban gama rufe baki ba suka rika ni muka fara ja in ja da su, da gudu Hafiza ta zo ta buge hannu police din ta hau ta da masifa.
“Mi tai muku? Haka kawai za ku shigo cikin gida mu kamata? Wace duka ta baku izinin shiga gidan mutane anyhow”
Police din ta nuna ta a fusace.
“Ke mahaukaci ki san abunda kike yi, karki ce zaki taba police zan ci mutuncinki, marar kunya kawai”
“Yes louder pls mu nan gidan sai mu kashe mutum ba komai ba ne a gurin mu, dan haka mun fiki tantiranci”
Cewar Hafiza tana zare mata ido kamar ba da police take fada ba. Sai da Mama ta daka mata tsawa sannan ta umarce da ta dauko min Hijabina.
“Amman Mama...”
Hafiza bata gama fadar abunda zata fada ba Mama ta tari numfashinta.
“Dauko mata Hijabinta na ce, duk inda za a je indai tana da gaskiya gaskiyarta zai fito da ita, Allah yana tare da mai gaskiya”
Ranta be so ba taje ta dauko min Hijabi na karba na saka, sai da muka fara tafiya sannan yarana suka fashe da kuka, ba ma kamar Amal wacce ta biyoni har kofar gida tana kiran sunana.
“Momy.....”
Ban san lokacin da hawaye ya wanke min fuska ba, ko ba komai sun tozarta ni, sun saka ni a motar police patrol, duk wanda zai gan ni a ciki dole na zargi wani laifin na aikata, duk kuwa da kasancewar ban san abunda nai ba, ga kuma mutane da suka tara mana a kofar gida, domin motar har da maza sai suka tsaya daga waje. Ina jin lokacin da Inna take tambayatar wane station ne za a kai ni sai mai tukin motar ya amsa mata da.
“State CID”