Sashe 56
Gobe Na Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Bata fuska tai tana kokarin kuka. Kanwata Salima tai dariya ta ce.
“Kin ganta nan wallahi dole sai an goyata a cikin gidan nan, ko dai Namra ta goyata ko wani a cikin gidan nan idan ba haka ba sai ta shige cikin daki tai ta kuka tana kiranki, yanzu kuma kin dawo dan haka ki yi ta goyon abarki daman can ke kika saba mata”
Dariya nai na kai hannu na dauke na dorata a bayana, ina kokarin kwance dankalin kaina na goyata da shi na ji Sallamar Baby Namra wato kawar Namra yar mutumen nan marar mutunci, da kuzarinta ta shigo da far'a har da yar ledarta a hannu. Gaba daya yan matan gidan mu suka hau yi mata oyoyo suna ta murna da zuwanta da alama dai sun saba da ita ba kamar yadda na ke tunani ba. Ita ma da far'a take ta gaishe su daya bayan daya sannan ta nufi dakin Mama inda ta san su Namra suna can.
Ni dai ina goye da Amal ina dahuwar indomie sa gata ta shigo tare da Namra, Namra na nuna min ledar hannunta.
“Momy kalla turare da chocolate Hajiyarta ta ce ta kawo mana”
“Eyeee lallai kun gode”
“Laaaa Momy Good afternoon”
Ta fada tana mamakin ganina
“Ykk ya makaranta?”
“Fine”
Sosai yarinyar take kama da mahaifinta, sai dai ita tana da far'a da son mutane ba kamar shi ba. Kana ganin fuskarta ita da Namra ka san suna murna da ganin junansu, daman kwana biyu nan suna da damuna da maganar zuwa gidan ni kuma na banzantar da maganar sai ga ta a yau ta zo. Amal ma sauka tai daga bayana ta bi bayansu.
Ina sallame sallar la'asar Adnan da Namra suka shigo tambaya wai za su je waje su yi wasa, har ta bukaci na bata kudi ta biya kudin lilon da ake kusa da mu su biya su hau, ban musa musu ba na dauko jakata na ciro naira hansin na mika mata suka fita da gudu har suna rigengen. Wani irin faduwar gaba ne ya same ni sai na ji kamar na kira su na ce su dawo, gaba daya na ji babu dadi, ban kuma san dalilin hakan ba, zuciyata tai ta bugawa da karfi kamar zata fito tsabar faduwar gaban da nake, a take na soma ambaton Allah, sai dai ban wani damu ba ganin yamma ce na san shaidanun aljanu ma suna saka haka. Bayan na gama azkar na dauko wayata na shiga YouTube in duba wasu videos har biyar da rabi tai sannan na fito tsakar gidan kamar yadda muka saba zama na zauna cikin ya'uwana. Sallama akai mana muka amsa sai yaro ya shigo yace wai ana kiran Baby Namra direban ta ne ya zo daukarta. Kamin mu ba shi amsa Adnan ya shigo gidan da gudu har ya faduwa wasu yara na biye da shi jikinsa duk kasa ya fado kaina.
“Momy Namra Namra....ta fada rijiya..... ”
Ban san lokacin da na ture shi ba na mike tsaye na daki kirji idanuwana a waje.
“Wace Namra?”
*Jiya na yi 5k words yau kuma na yi 5k+ words 🤔 wace addu'a kuka min ne?🙄 Pls ku ba ni ita nai ma Halimatu ta koma gidan Abdulhamid 💔😪*
7/21/21, 10:44 PM - Buhainat: *GOBE NA...*
By Khadeeja Candy
2️⃣9️⃣
“Baby Namra....”
Jin maganar tasa nai kamar daga sama, ban san lokacin da na doshi kofar fita da gudu ba, har sai da Inna ta riko ni.
“Tsaya ki saka hijab dinki”
Sai na koma cikin gidan da gudu na shiga dakin Mama ban tsaya neman hijab na janyo zanen da nai arba da shi a saman gadonta na lufe kaina kamar wata tsohuwa na fito hankali a tashe. Yan mata gidan mu na biye da ni, rijiyar da na sani a unguwar mu na nufa sai Adnan yace min ba ita ba.
“Momy ba ita ba, rijiyar malam ya'u”
Tsayawa nai cak jin ya ambaci rijiyar da na manta when last a dibi ruwa a cikinta, rijiyar da ake cewa har ma sha ruwa akwai a ciki.
“Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un, miya kaiku gurin rijiyar malam ya'u”
Sai na maida dubana gurin Salma wacce tai maganar.
“Namra ce ta ce muje can mu yi wasa”
A nan ma kallon Adnan nake, kamar wacce bata da makoma haka na zama, jikina yai sanyi ga uban sara da kaina ya soma yi. Tafiya nake ina jin kamar ana mayarda ni baya ina tafiyar ina jin kamar ba kasa nake takawa, sam ban lura da babu talkami a kafafuwana ba sai da na isa bakin rijiyar kafafuwana suka taka sanyin ruwan da ke gurin. Leka rijiyar da nai ma sai da wani jiri ya kama ni saboda hudunta da kuma dadewarda tai ba a bude ta ba. Wasu mazan unguwar mu ne suka shiga ciki suka daukota a yanayin da na ganta na sam abu ne mai wahala ta rayu, ta ji ciwo a kai a fafafuwanta ma ta samu rauni hannunta har zubar da jini yake.
“Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un”
Shine abunda kawai na iya furta na saka hannu biyu na dauke, abun ka da marar karfi ga kuma rashin kuzari na tashin hankali sai na fadi a gurin tare da ita, har sai da kanena suka zo suka dauketa ni kuma na bi bayansu hankali tashe, har na isa gida kuka nake ina jin mutane na tambayar ko mi ya kai su can, garin ya suka fada a wannan tsohuwar rijiyar, sam ni kam ba tambayar ce a gabana yanzu ba ceto ran yar mutane ne a gabana. Muna shiga gida na dauko hijabi da jakar kudina na saka takalmi na muka nufi titi ni da kanena kusan rabin unguwar suna biye da mu wasu na fadi bata da rai wasu na tambayar yadda abun ya afku. Napep muka shiga kai tsaye muka nufi asibitin fmc, mun tararda mutane da yawa a emergency kuma sai mu ka yi rashin sa'a babu likitoci da yawa kasancewar yau Saturday. Sun karbe ta domin duk wanda ya ganta a dole ya tausaya mata, sai dai duk da sun karbe ta din hankalina be kwanta ba na kasa zaune na kasa tsaye, zuciyata ta na ta raya min cewar bata da rai ganin tun da aka cirota daga rijiyar bata motsi bata numfashi ga raunukan da ta ji.
“Anty ki zauna”
Salma ce ta dafa ni tana fadin haka, sai na girgiza mata kai ina kuka domin ba zan iya ba.
“Ko ki kira yaya Abdallah...”
Salma na fadin haka zuciyata ta raya min yes na kira shi maybe he can help, jaka na lalaba ban ji wayata ba sam ban lura da jakar kudi ce kawai a hannuna ba har sai da Salma ta miko min ta ta wayar.
“Gashi ki yi magana”
Da na karbi wayar sai na rike na rasa yadda zan yi da ita.
“Ya dauka fa”
Sai nai saurin karawa a kunne.
“Hello....”
“Wake magana”
Muryar Suwaiba ce da alama wayar tana hannunta ne.
“Ni ce Halima ce Ina Abdallah”
Ta dade bata ce min komai ba har sai da nai zaton wayar ta tsinke.
“Hello”
“Bachi yake”
“Ki taimaka min dan Allah ki tashe shi, ina cikin matsala yarinyar da..... ”
Ban gama fadar abunda zan fada ba ta tari numfashina da masifa.
“Haba Halima ya kamata ki gane Abdallah fa kanen mijinki ne, duk da ya rabu da ke be kamata wata alaka na shiga tsakaninku ba, ki shafa matsa lafiya dan Allah”
“Yanzu ma in cikin matsala ne shiyasa na kira shi...”
Na fada domin kawai ta fahimci akwai dalilin kiran ba hakan nan kawai nake kiransa ba.
“To bachi yake”
Ta tsinke wayar. Kwallar idona ta hanani ganin komai, hayaniyar mutanen da suke emergency sai na ji kamar ina wata duniyar, tabbas ina jin bakina yana motsi amman ban san me nake fada ba, Salma ta karbi wayarta ko na bata ko jefarwa nai duk ban sani ba, sai kuma na ji wani na tambayar ina yayen yarinyar nan, wata kila da mu yake wata kila kuma ba da mu yake ba duk ba zan iya ganewa a yanzu wani hudu ne ya rufe min ido ga idon a bude amman na kasa ganin komai.
“Anty.....”
Can cikin a na ji muryar Salma ta kirani kamar tana wata uwa duniyar. Tassssss na ji saukar wani azababben mari a gefen kumatuna, marin da ba a taba min irinsa ba tun da uwata ta haife ni a duniya, wani zafi na ji ya mamaye min ilahirin fuskata kamar wuta, a take kafafuwana suka kasa daukata.
“Ku rike ta....”
Shine abunda na iya jiyowa shi ma kamar daga can wata uwa duniyar, ji jai na buga hannuna a wani abun mai kamar karfi sai dai ko kadan ban ji zafin ba har numfashin da ke jikina yai gaba abunsa...
7/21/21, 10:45 PM - Buhainat: *GOBE NA...*
By Khadeeja Candy
3️⃣0️⃣
AHMAD POV.
Aikin yake ta yi zuciyarsa na gurin yarsa, hakan nan kawai yake jin cewar baby Namra is not safe, yana ta ganin kamar matar nan zata mata kallon banza ko ta fada mata magana marar dadi saboda shi, and he can't take it anymore ko akansa balle akan yarsa da yake ji da ita, zuciyarsa na ta raya masa abubuwa, he feels like ba zai sake barinta taje gidan ba zai dauke mata hankali da wani abun.
“Daga ganin matar nan bata da mutumci ko na five naira”
Ya furta zuciyarsa na kara raya masa cewar macen auren mai mutumci ba zata iya tsayawa ta fada masa magana marar dadi kamar yadda Halimatu tai ba. Sai yanzu ma yake jin shi be yarda fa tarbiyar gidansu ba kar su lalata masa ya. Mikewa yai tsaye yana kallon agogo hannunsa da ya nuna masa karfe biyar da yan mintuna. Takardunsa ya kwashe ya dauko laptop dinsa ya nufi part dinsa ya aje su a can sannan ya fito harabar gidan ya kira almu direba, Almu ya zo da gudunsa.
“Kaje ka dauko Baby inda ka kaita dazun”
“To Alhaji”
“Kin ganta nan wallahi dole sai an goyata a cikin gidan nan, ko dai Namra ta goyata ko wani a cikin gidan nan idan ba haka ba sai ta shige cikin daki tai ta kuka tana kiranki, yanzu kuma kin dawo dan haka ki yi ta goyon abarki daman can ke kika saba mata”
Dariya nai na kai hannu na dauke na dorata a bayana, ina kokarin kwance dankalin kaina na goyata da shi na ji Sallamar Baby Namra wato kawar Namra yar mutumen nan marar mutunci, da kuzarinta ta shigo da far'a har da yar ledarta a hannu. Gaba daya yan matan gidan mu suka hau yi mata oyoyo suna ta murna da zuwanta da alama dai sun saba da ita ba kamar yadda na ke tunani ba. Ita ma da far'a take ta gaishe su daya bayan daya sannan ta nufi dakin Mama inda ta san su Namra suna can.
Ni dai ina goye da Amal ina dahuwar indomie sa gata ta shigo tare da Namra, Namra na nuna min ledar hannunta.
“Momy kalla turare da chocolate Hajiyarta ta ce ta kawo mana”
“Eyeee lallai kun gode”
“Laaaa Momy Good afternoon”
Ta fada tana mamakin ganina
“Ykk ya makaranta?”
“Fine”
Sosai yarinyar take kama da mahaifinta, sai dai ita tana da far'a da son mutane ba kamar shi ba. Kana ganin fuskarta ita da Namra ka san suna murna da ganin junansu, daman kwana biyu nan suna da damuna da maganar zuwa gidan ni kuma na banzantar da maganar sai ga ta a yau ta zo. Amal ma sauka tai daga bayana ta bi bayansu.
Ina sallame sallar la'asar Adnan da Namra suka shigo tambaya wai za su je waje su yi wasa, har ta bukaci na bata kudi ta biya kudin lilon da ake kusa da mu su biya su hau, ban musa musu ba na dauko jakata na ciro naira hansin na mika mata suka fita da gudu har suna rigengen. Wani irin faduwar gaba ne ya same ni sai na ji kamar na kira su na ce su dawo, gaba daya na ji babu dadi, ban kuma san dalilin hakan ba, zuciyata tai ta bugawa da karfi kamar zata fito tsabar faduwar gaban da nake, a take na soma ambaton Allah, sai dai ban wani damu ba ganin yamma ce na san shaidanun aljanu ma suna saka haka. Bayan na gama azkar na dauko wayata na shiga YouTube in duba wasu videos har biyar da rabi tai sannan na fito tsakar gidan kamar yadda muka saba zama na zauna cikin ya'uwana. Sallama akai mana muka amsa sai yaro ya shigo yace wai ana kiran Baby Namra direban ta ne ya zo daukarta. Kamin mu ba shi amsa Adnan ya shigo gidan da gudu har ya faduwa wasu yara na biye da shi jikinsa duk kasa ya fado kaina.
“Momy Namra Namra....ta fada rijiya..... ”
Ban san lokacin da na ture shi ba na mike tsaye na daki kirji idanuwana a waje.
“Wace Namra?”
*Jiya na yi 5k words yau kuma na yi 5k+ words 🤔 wace addu'a kuka min ne?🙄 Pls ku ba ni ita nai ma Halimatu ta koma gidan Abdulhamid 💔😪*
7/21/21, 10:44 PM - Buhainat: *GOBE NA...*
By Khadeeja Candy
2️⃣9️⃣
“Baby Namra....”
Jin maganar tasa nai kamar daga sama, ban san lokacin da na doshi kofar fita da gudu ba, har sai da Inna ta riko ni.
“Tsaya ki saka hijab dinki”
Sai na koma cikin gidan da gudu na shiga dakin Mama ban tsaya neman hijab na janyo zanen da nai arba da shi a saman gadonta na lufe kaina kamar wata tsohuwa na fito hankali a tashe. Yan mata gidan mu na biye da ni, rijiyar da na sani a unguwar mu na nufa sai Adnan yace min ba ita ba.
“Momy ba ita ba, rijiyar malam ya'u”
Tsayawa nai cak jin ya ambaci rijiyar da na manta when last a dibi ruwa a cikinta, rijiyar da ake cewa har ma sha ruwa akwai a ciki.
“Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un, miya kaiku gurin rijiyar malam ya'u”
Sai na maida dubana gurin Salma wacce tai maganar.
“Namra ce ta ce muje can mu yi wasa”
A nan ma kallon Adnan nake, kamar wacce bata da makoma haka na zama, jikina yai sanyi ga uban sara da kaina ya soma yi. Tafiya nake ina jin kamar ana mayarda ni baya ina tafiyar ina jin kamar ba kasa nake takawa, sam ban lura da babu talkami a kafafuwana ba sai da na isa bakin rijiyar kafafuwana suka taka sanyin ruwan da ke gurin. Leka rijiyar da nai ma sai da wani jiri ya kama ni saboda hudunta da kuma dadewarda tai ba a bude ta ba. Wasu mazan unguwar mu ne suka shiga ciki suka daukota a yanayin da na ganta na sam abu ne mai wahala ta rayu, ta ji ciwo a kai a fafafuwanta ma ta samu rauni hannunta har zubar da jini yake.
“Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un”
Shine abunda kawai na iya furta na saka hannu biyu na dauke, abun ka da marar karfi ga kuma rashin kuzari na tashin hankali sai na fadi a gurin tare da ita, har sai da kanena suka zo suka dauketa ni kuma na bi bayansu hankali tashe, har na isa gida kuka nake ina jin mutane na tambayar ko mi ya kai su can, garin ya suka fada a wannan tsohuwar rijiyar, sam ni kam ba tambayar ce a gabana yanzu ba ceto ran yar mutane ne a gabana. Muna shiga gida na dauko hijabi da jakar kudina na saka takalmi na muka nufi titi ni da kanena kusan rabin unguwar suna biye da mu wasu na fadi bata da rai wasu na tambayar yadda abun ya afku. Napep muka shiga kai tsaye muka nufi asibitin fmc, mun tararda mutane da yawa a emergency kuma sai mu ka yi rashin sa'a babu likitoci da yawa kasancewar yau Saturday. Sun karbe ta domin duk wanda ya ganta a dole ya tausaya mata, sai dai duk da sun karbe ta din hankalina be kwanta ba na kasa zaune na kasa tsaye, zuciyata ta na ta raya min cewar bata da rai ganin tun da aka cirota daga rijiyar bata motsi bata numfashi ga raunukan da ta ji.
“Anty ki zauna”
Salma ce ta dafa ni tana fadin haka, sai na girgiza mata kai ina kuka domin ba zan iya ba.
“Ko ki kira yaya Abdallah...”
Salma na fadin haka zuciyata ta raya min yes na kira shi maybe he can help, jaka na lalaba ban ji wayata ba sam ban lura da jakar kudi ce kawai a hannuna ba har sai da Salma ta miko min ta ta wayar.
“Gashi ki yi magana”
Da na karbi wayar sai na rike na rasa yadda zan yi da ita.
“Ya dauka fa”
Sai nai saurin karawa a kunne.
“Hello....”
“Wake magana”
Muryar Suwaiba ce da alama wayar tana hannunta ne.
“Ni ce Halima ce Ina Abdallah”
Ta dade bata ce min komai ba har sai da nai zaton wayar ta tsinke.
“Hello”
“Bachi yake”
“Ki taimaka min dan Allah ki tashe shi, ina cikin matsala yarinyar da..... ”
Ban gama fadar abunda zan fada ba ta tari numfashina da masifa.
“Haba Halima ya kamata ki gane Abdallah fa kanen mijinki ne, duk da ya rabu da ke be kamata wata alaka na shiga tsakaninku ba, ki shafa matsa lafiya dan Allah”
“Yanzu ma in cikin matsala ne shiyasa na kira shi...”
Na fada domin kawai ta fahimci akwai dalilin kiran ba hakan nan kawai nake kiransa ba.
“To bachi yake”
Ta tsinke wayar. Kwallar idona ta hanani ganin komai, hayaniyar mutanen da suke emergency sai na ji kamar ina wata duniyar, tabbas ina jin bakina yana motsi amman ban san me nake fada ba, Salma ta karbi wayarta ko na bata ko jefarwa nai duk ban sani ba, sai kuma na ji wani na tambayar ina yayen yarinyar nan, wata kila da mu yake wata kila kuma ba da mu yake ba duk ba zan iya ganewa a yanzu wani hudu ne ya rufe min ido ga idon a bude amman na kasa ganin komai.
“Anty.....”
Can cikin a na ji muryar Salma ta kirani kamar tana wata uwa duniyar. Tassssss na ji saukar wani azababben mari a gefen kumatuna, marin da ba a taba min irinsa ba tun da uwata ta haife ni a duniya, wani zafi na ji ya mamaye min ilahirin fuskata kamar wuta, a take kafafuwana suka kasa daukata.
“Ku rike ta....”
Shine abunda na iya jiyowa shi ma kamar daga can wata uwa duniyar, ji jai na buga hannuna a wani abun mai kamar karfi sai dai ko kadan ban ji zafin ba har numfashin da ke jikina yai gaba abunsa...
7/21/21, 10:45 PM - Buhainat: *GOBE NA...*
By Khadeeja Candy
3️⃣0️⃣
AHMAD POV.
Aikin yake ta yi zuciyarsa na gurin yarsa, hakan nan kawai yake jin cewar baby Namra is not safe, yana ta ganin kamar matar nan zata mata kallon banza ko ta fada mata magana marar dadi saboda shi, and he can't take it anymore ko akansa balle akan yarsa da yake ji da ita, zuciyarsa na ta raya masa abubuwa, he feels like ba zai sake barinta taje gidan ba zai dauke mata hankali da wani abun.
“Daga ganin matar nan bata da mutumci ko na five naira”
Ya furta zuciyarsa na kara raya masa cewar macen auren mai mutumci ba zata iya tsayawa ta fada masa magana marar dadi kamar yadda Halimatu tai ba. Sai yanzu ma yake jin shi be yarda fa tarbiyar gidansu ba kar su lalata masa ya. Mikewa yai tsaye yana kallon agogo hannunsa da ya nuna masa karfe biyar da yan mintuna. Takardunsa ya kwashe ya dauko laptop dinsa ya nufi part dinsa ya aje su a can sannan ya fito harabar gidan ya kira almu direba, Almu ya zo da gudunsa.
“Kaje ka dauko Baby inda ka kaita dazun”
“To Alhaji”