← Book details Gobe Na Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 34 OF 136

Sashe 34

Gobe Na Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Zare masa ido tai ta wurgarda remote din tv a kujera.

“Idan a gurinka ba komai ba ne, ni a gurina komai ne, ba zan bari ka auri yarinyar da zata mallake min Kai ba, ka juya min baya ni da Baby Namra ba zai yiyu ba”

Tana kai wa nan ta mike tsaye ta nufi upstairs tana fadin.

“Ai dole ne idan za ayi aure ayi bincike ba zan yarda ka auro min yarinyar da zata canja ka ba, ko wacce zata zo ta kashe ka ta kwashe dukiyarka ba, mata ba abun yarda ba ne musamman na yanzu.... ”

Tana shigewa dakinta, kanwarsa ta taso ta dawo kusa da shi ta zauna tana masa rada.

“Wallahi ka kai je ka kaita gurin wani boka ayi mata asiri ta yarda ka auri wannan yarinyar... ”

Duk yadda yake cikin bacin rai sai da ta saka shi murmushin dole saboda wautarta, sannan ya mike tsaye yasa hannuns aljihu ya fice daga falon harabar gidan ya fito ya jingina da motar yana cikawa bakinss iska ya san halin mahaifiyarsa idan ta ce bata yarda da abu ba, babu yadda za ayi ta yarda da shi har abada, idan kuma bata son abu babu mai cilasta ta so shi, shi yanzu ya zai yi da matsalarsa a duk lokacin da ya taso da maganar aure sai ta nuna bata so, ya kasa fahimta wace irin uwa ce ita? Miyasa ko da yaushe take kishin ganin yayi aure? Ko take kishin duk matar da ya aura? Forget about the past shi yanzu ya zai yi da yar mutane idan ya barta za a ce ya yaudareta daman can ba auren yai niya ba, after that idan ya nemo wata ita ba Momy zata iya cewa tana da wata matsalar. Kansa ya daga yana kallon katon gidan mai cike da kayan alatu, mi mahaifiyarsa ta nema ta rasa? Then miyasa shi ba zata bar shi ya samu nasa farincikin ba? Miyasa ba zata bar shi ya gina rayuwarsa ba? Kara wayar da ke hannunsa tai alamar sako number Momy ce.

_Ka dawo karfe 8pm_

Yana karanta sakon ya shafa kansa yana busar da iskar bakinsa.

“Ohhh Momy ni fa ba yaro ba ne why all these rules?”

Bude motarsa yai shiga ransa babu dadi yai ma motar key ya danna horn aka bude masa gate ya hau titi ba tare da sani inda zai je ba, gari yake ta zagawa a titi, maganganun Hajiya ne suke ta masa yawo a kai shi ya rasa gane abunda yake damun mahaifiyarsa. Har ya daga wayarsa ya kira abokinsa wanda ya saba labarta masa damuwarsa sai kuma wata zuciyar ta hana shi, he decided ya faka motarsa gefen titi yai relaxing cikin motar for a while sannan ya koma gida, after ya faka motarsa gefen titi ya sauke gilashin motar ya kwantar da kujerar motar tare da cire hular kansa.
Wata yarinya ya hango gefen titi tana kuka, sai da ya kalli ko'ina yaga babu kowa a tare da ita sannan ya bude motar ya fita ya nufi inda take.

“Ke lafiya? Me kike yi ma kuka?”

“Bacewa nai”

Ta amsa masa cikin kuka.

“Garin ya?”

“Muna tare da Mama Hafiza mun zo biki shine kuma yanzu ban ganta ba, tace na zo bakin titi na same ta mu wuce na zo ban ganta ba kuma na koma ban gane gidan da na fito ba”

“Ina Mamanki?”

“Tana can gidanta”

“Babanki fa”

“Ban san inda yake ba”

“Rasuwa yai?”

“Aa tunda ya saki Momy mu ban sake ganinsa ba, ita kuma Momy mu ta auri wani...”

The way da tai masa maganar sai ta bashi tausayi, ya san da ace tare take da mahaifiyarta ko mahaifinta ba zai su tafi su barta ba ko kuma su yi saken da zata bata, risinawa yai yana kallon fuskarsa.

“Miye sunanki”

“Namra”

“Wow cute you sunan yata, yanzu za ki iya gane gidan ku?”

Ta girgiza kai alamar no.

“Wace unguwa kike zaune?”

“Yan magurora”

“Gurin wa?”

“Karkar mu”

“Ita ke rikonku?”

Ta gyada masa kai.

“To yanzu kin san yadda za mu yi? Zan saka ki a motata na kai ki gidanmu da safe sai na kai cigiyarki, ko kuma naje unguwarku na nemi nai unguwar na damka masa ke kin yarda”

A take ta gyada kai sai ya rika hannuta ya nufo motarsa da ita ya saka ta shi ma ya zagaya ya shiga.

“Ita Mamanki wane unguwa take?”

“Ban san sunan unguwar ba”

“Ba ki taba zuwa ba?”

“Na taba zuwa sau daya”

“Sau daya?”

Ya tambaya yana kallonta da mamaki sai ta gyada masa kai.

“Miyasa sau daya kawai?”

“Kaka tace mana wanda ta aura baya son yara shiyasa bata tafi da mu ba”

Tabe baki yai yana yi ma motar key.

“Ji wani irin selfishness dan Allah mutum be son yara kuma ka yi aure ka tafi ya bar su, yanzu nan idan ni bana kwarai ba ne shikenan kin fada mugun hannu mtsszzzzzzzzzzzzzzzzz”

Yaja wani dogon tsaki yana jin kamar ace shine uban yarinyar ya ci mutunci uwar, ko da yake shi miyasa uban ma ya bar su hannunta.

“Imagine ayi ta haihuwa bana iya kula da yara ko ba a son dawainiya da su, shi uban baya so ita ma bata so”

Ya fada yana mai jin haushi iyayen duka biyu.

‘Ba ma gidan uban da zan kai ki cigiya, idan suna son ki su nemi ki da kansu’

Wannan karon a zuciyarsa yai maganar. Sannan ya cigaba da tuka motar, abun da yaro ta man ta sha kuka ta koshi kamin ya isa gida har ta yi bachi. After yayi farkin ya zagayo ya bude motar yana kokarin daukarta ya dora a kafadarsa ta farka, sai dai hakan be hana shi daukarta ba ya nufi cikin gidan da ita, kamin ya karasa Baby Namra ta fito daga falon tana masa oyoyo.

“Daddy sannu da zuwa”

“Yauwa Baby”

Ya fada yana shafa kansa da dayan hannunsa tare da murmushi.

“Daddy wacece wannan?”

Ta tambaya tana kallonsa be amsa mata ba sai da ya shiga falon Hajiya ya sauke Namra saman kujera.

“Je ki kawo mata ruwa ta sha, kawa na samo miki”

Sai ta bata fuska.

“Ni Allah ya tsare ni ba kawata ce ba”

Ta fada tana nufar hanyar kitchen, shi kuma yai murmushi yana kallon Namra wacce ta takure guri daya kamar mai jin tsoro, shi sai yanzu yake ganin kamar ma ya taba ganinta.

“Ina ka samo ya?”

Hajiya da ke tsaye upstairs tana latsa waya ta tambaya daga can inda take tsaye tana kallonsa.

“Wasu mahaukatan iyaye ne da ba su san darajar yaya ba suka jefar da ita”

“Jefarwa kuma?”

Hajiya ta tambaya tana saukowa daga stairs din.

“Yes”

Ya amsa mata yana maida dubansa gurin Baby Namra wacce ta fito kitchen rike da kofin ruwan.

*Khadija Abubakar Alkali*
7/20/21, 8:33 AM - Buhainat: *GOBE NA...*

By Khadeeja Candy

1️⃣9️⃣

Labarin GOBE NA ba labari irin wanda na saba yi ba, shiyasa tun kamin na fara sakinsa na fada muku cewar rayuwar aure ce mai cike da kalubale, idan ba ku manta ba inkiyar labarin ZAWARCIN HALIMATU, labari ne na rayuwar kala kala ta gidan aure da zawarci, da kuma rikon yara da kula da tarbiyarsu, zancen dan Allah Candy kar ayi kaza ko ki canja kaza be taso ba, matukar ana son labarin ya tafi a yadda aka tsara kuma a isar da sakon da ake son isarwa.

GOBE NA ba labarine na zallar soyayya ba, yana tafe ne da kalubalen na rayuwa, duk irin halin da Halimatu take ciki ko zata kasance a ciki akwai mata da yawa da suka dade da shiga cikin wannan halin, ko suka fita shiga matsala ma. Wallahi a three weeks ago akwai wacce ta kirani tana kuka tana fada min abunda akai wa Namra a labarin haka akai wa yarta kuma har yau babu wanda ya sani mijinta ya hanata magana, secondly mijinta kamar Aminu yake, a lokacin da ta ba ni labarin mijinta sai da kaina ya daure Wallahi. So akwai mata da yawa da suke fuskantar rayuwar gida aure kala kala, ko da ba mu tabo duka ba ya kamata ace muna taba wani bangaren na rayuwarmu ta yau da kullum ai.

Labarin zai tafi a yadda na tsara shi ga wanda yaji zai iya bi fine.

*** *** ***

“Aa Gwarzo wace uwar ce zata jefar da yarta haka nan kawai? Ka taba ganin bolar yaya?”

Momy ta fada bayan ta zauna tana kallon Namra.

“Oh Momy ba ki ji inda na samo ta ba, uwarta na son ta zata jefar da ita”

“Idan ma haka ne ai ba laifi uwar ba ne, na uban ne akan me zaka bar yarinya na tsawon lokaci ba ka neme su ba? Taya ma zaka bar ma mace dawainiyar yara bayan ba da su ta zo ba?”

“Ita na fa uwar da laifinta”

“Baka san abunda ya fito da ita daga gidan mijin ba, ba duk mace ce bata son yaranta ba ni ban yarda akwai mace da bata son yaranta ba, wata kila ma hankalinta yana can tashe”

“Ko dai zan maida ita sai gobe sai jikinsu ya fada musu, ko goben ma sai da maraice”

Ya fada yana shafa kan Namra.

“Yarinya kyakkyawa suna son wufintar da ita”

Momy ta yi murmushi.

“Ya sunanki?”

“Namra”

Ta amsa hankalinta kwance kamar ta san su.

“Allah sarki Baby Namra kin samu takwara”

Baby Namra dai bata komai ba sai wani shigewa take jikin Momy.

“Sai gobe zan bada cigiyarta a radio idan sun ga dama su zo nan su dauke ta”

Ya fada yana mikewa tsaye. Sai ita Namra ta mike tsaye zata bi shi.

“Zauna nan Momy zata kula da ke”

Momy ta mika mata hannu tana murmushi.

“Zo nan jikata yar albarka”

Ba musu taje ta zauna saman kujerar sai Momy ta dorata a kafafuwanta.

“Ajikin nawa?”

“Uku”

“Wace makaranta kike?”

“Gwarzo International school”

Momy ta yi dariya, Ahmad ma da ke kokarin fita juyowa yai ya kalleta.

“Wow i feel it tun farko na ji kamar ina da alaka da ita, ashe yarinya yar makarantar mu ce shiyasa take da natsuwa”
Chapter 34 · 0% Book details