Sashe 29
Gobe Na Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Al-hamdulillah shine abunda na ke yawan maimaitawa tun daga lokacin da na saka kafata a gidan Abdulhamid, duk wani abun na jindadi rayuwa da mace zata nema a gidan miji Abdulhamid ya tanadar min shi, tun daga na ci har na sakawa a jikin har na kallo, kamar wata kwai haka yake tarairaiya ta a yadda yake nuna min kulawa da soyayya ban tsamanci samunta a gurinsa kamar haka ba. Yana yawan nanata min cewar ina da wani irin girma da daraja a idonsa saboda aurensa da nai alokacin da yake dauke da lulurar da ba ko wace mace ce za ta yarda ta aure shi a haka ba, wannan dalilin yasa yake da kara gwarjini a idonsa. Ya kara maida hankalinsa gurin neman magani fiye da da, ni ma kuma ina kokarin yi masa abubuwan da zasu taimaka duk dai bana ganin wani alamu na warkewar sai ban taba gajiyawa ba ko na fitar da rai domin na san babu cutar da bata da magani. Ina samun kwanciyar hankali a aurena da Abdulhamid fiye da wanda nai a baya da Aminu, ko ba komai zai nuna min kulawa zan kwanta a kirjinsa na farka a gefensa mu ci abinci tare mu yi fira mu yi hara mu yi nishadi, ba kamar a gidan Aminu ba da ba shi da lokaci na.
Bana da wani fargaba ko tunani a gidan aurena bayan ta mutum biyu yayana da kuma Hajiya wato mahaifiyarsa domin na lura a duk zuwan da muke gaishewa kamar bata na'am da ni, bayan a baya kuma ba haka na santa ba, duk dai ba wani zuwa muke sosai ba amman a duk lokacin da muka je gaisheta ko kuma muka fito daga wani gurin muka biya sai ta yi min tarba ba a baya da kai ba, ko kuma ta bar a nan a falon ba ita kadai ba har yayanta mata biyu na lura haka suke min basa son fira da ni balle kuma irin wasar nan ta matar yaya, namijin ne kawai babu ruwansa shi kan idan muka tarar da shi a gida mu yi ta fira abun kamar ba kanen mijina ba, amman bayan wannan bana da wata matsala da Abdulhamid idan ka cire na kyamar yayana da yake yi, domin na lura ko zancensu baya son ina yi idan aka kira waya da sunan za mu gaisa da su a lokacin da yake kusa da ni da a take yanayinsa zai canja, be taba siye ko da biscuit din maira goma ya mika min ko ya bawa wani yace a kai musu balle kuma har ya tambayi lafiyarsu ko karatunsu, sai dai ina masa uzuri da wannan ganin cewar shi din be taba aure ba sai yanzu kuma daman can ba mutum ne mai son yara ba, ballanta na san yadda wasu mazan suke basa son yayan wasu a kusa da su, musamman Abdulhamid da na lura da alamar yana ďan da kishi ba kamar wasu ba, tun daga lokacin da yai kokarin hana ni aikina na lura da hakan ga kuma ya hana yin ko. Wane irin social media saboda kar na hadu da maza, yana yawan fada min cewar na rike masa kaina na tsare masa kaina kar na bar shaidan ya rinjaye ni, wani lokacin na kan amsa masa da to ko nai masa alkawarin haka ba wani lokacin kuma sai dai na yi dariya, domin a tunani babu abunda zai kai ni na aikata wani alfama ko da bana da aure balle ina da shi, ba wai na fi karfin shaidan ba ne, kawai dai ina tuna baya ne a lokacin da Aminu zai iya shafe wata da watannani ba neme ni ba kuma babu kulawa da magana mai dadi ga shi ina zuwa aikin ina ganin mazan amman ban aikata ba, balle yanzu da nake auren mutumen da ya san darajar aure kuma bana ganin mazan ma, to mi kam Allah na tuba wace tsiyar ce zata saka ni aikata hakan.
A zaman aure da Abdulhamid wani abun da zai baka mamaki shine rashin iya girki, wanda ni kaina yake bani mamaki kuma ya ba ni tsoro, tun da na zo gida ban taba dora girki ko da ruwan zafi ne ya tafasa ba, idan na dora miya yadda na hada ta haka zan zo na tararda ita haka tuwo ma, shiyasa ban taba yin jalof ba lalle shimkafa da wake, indai har za mu sha tea sai dai Abdulhamid ya dora mana, indai har ni na dora ba zai tafasa ba ko da kuwa a gas ne ko electric kettle. Sai dai be taba sakawa Abdulhamid ya min fada ko nuna bacin ransa a hakan hakan ba, kullum safe shi zai dora mana ruwan da za mu amfani da su da rana kuma yai mana take away haka ma da dare, na kuma rasa gane dalilin haka bayan a can baya na iya girki na kamar ko wace mace, amman tun da na tsinci kaina a gidan Abdulhamid sai komai ya lalace.
Ranar wata labara da misalin sha daya da yan mintuna na ji an buga kofar falona, na yi tsamammi ko daya daga cikin yan matan gidan mu ne hakan yasa na tashi da kuzari na bude, abun mamaki sai nai arba da Suwaiba matar Abdallah kuma uwar yayansa mata guda biyu, na yi mamakin maganinta domin ta dade tana min waken zuwa amman bata zo ba sai yau, mun sha fira a ranar daman can Suwaiba mace ce mai son fira da far'a da haba haba da jama'a, ban yi zaton Abdallah ya kawo ta ba har da ta labarta min cewar shi ya kawo ta amman ya aje ta gurin gate wai yana sauri jaye gurin aiki.
Ta labarta min abubuwa da yawa a ciki har da na rashin son yara da Abdulhamid yake da shi, sannan ta dora min da cewar yawanci maza basa son yayan da ba na su ba, balle kuma Abdulhamid da yake saurayi, tana ta nanata min cewar sai na yi hakurin haka kamar ta san abunda ya fi damu na kenan, duk kuwa da kasancewar ban taba fadawa kowa ba.
Ganin na dauki waya na kira Abdulhamid na ce yai mana takeaway sai abun yai ta bata mamaki.
“Kar dai ace har yanzu baki fara girkin ba, ko kuwa amarcin ne ya motsa kike jin ba za ki iya dafawa ba?”
Dariya nai kamin na bata masa.
“Wallahi ba haka ba ne, idan na dora girkin baya dahuwa yadda na saka shi haka zan tararda shi kuma ga wuta ga komai amman ba ya yi”
“Too kar dai ace Abdulhamid ma yana da kohi kamar Abban Suhaima, ni ma idan nai masa wani laifin ko kuma na bata masa rai haka zan dafa abinci a ranar ba zai dafu ba sai na bashi hakuri”
Ta fada tana dariya... Ni ma dariyar nai sai dai ba irin ta ta domin ni wani tunanin ne ya zo min, kar dai ace Abdallah ne yai min kohi nake ta samun wannan matsalar?
“Ko da yake shi ma a tawaye ne dole za a samu dukansu suna yi, wata kila wani abun kika masa sai kin ba shi hakuri sannan za ki daidaita, amman fa ni kin san da na dauka ko Abdulhamid ba shi da kohi”
Zancenta ne ya dawo da ni daga duniyar tunani sai na sake yin murmushi a karo na biyu.
“Haka ne ai wani ba a iya ganewa sai idan wani abun ya faru”
“Haka ne”
Sai guraren karfi biyu ya kirata a waya yace ta fito bakin gate yana jiranta, a lokacin Abdulhamid be dawo ba, sai na saka Hijabina na rakata har gurin motarsa bayan na deba mata wasu abubuwan daga turaruka na da kayan kwaliya, gilashin motarsa a sauke yake amman ko da wasa Abdallah be dago ya kalleni ba da na gaishe ma sai ya amsa min a gajarce kamar be san ni ba, bayan sun wuce na dawo ciki gidan ina ta nazarin kalamanta. Daga karshe na yanke shawarar kiran Abdallah nai masa magana, haka kuwa akai bayan Abdulhamid ya dawo mun ci abinci mun yi fira ya fita sallah la'asar ni kuma na nemo number Abdallah ya aika masa kira, ringing tai kamar zata katse sannan ya daga, ban tsaya yi masa sallama ba balle gaisuwa kai tsaye na ce.
“Abdallah magana na ke son mu yi”
Sai na yi shiru bayan na fada masa hakan ina jiran na ji amsar da zai ba ni kamin na dora amman be ce min komai ba har sai da nai zaton ko wayar ta katse ne.
“Idan ka kullace ni da wani abun dan Allah ka kwance, tun da na zo gidan nan kullum nai girki ba ya yi”
“Babu hannuna a ciki”
Ya amsa da muryar da na jita kamar ba ta shi ba.
“Wata kila kana jin haushina ne, ko kuma kana jin bacin rai a kaina ne”
“Ban taba jin haushinki ba, kuma ba ki bata min rai ba, abunda kika aikata ne kawai idan na tuna ina jin babu dadi ne”
“To ka daina jin babu dadin, shiyasa bana iya girkin idan na yi ba yayi, dan Allah ka kwance Kohin da kai min”
Ina iya jiyo saukar numfashinsa kamin ya ce.
“Ban kullace ki da komai ba Halimatu, ke yanzu yar'uwata ce kawai kuma matar dan'uwana, yan'uwanta ta fi gaban wasa ko babu Abdulhamid babu abunda zai shiga tsakanin mu”
Yana fada min hakan ya kashe wayar, a take wani abun marar dadi ya kawo ma zuciyata ziyara. Har na gabatar da sallah la'asar ban daina jinsa ba, bayan sallah isha'i ina kwance saman kujera falo Abdulhamid ya fito daga bedroom ya nufo inda nake kwance, sumbatar kaina yai kamin ya daga ni na tashi zaune sai ya zauna sannan ya kwantar da kaina saman kijinsa yana shafa fuskata.
“Gobe fa ina tunanin zanje Abuja”
Dagowa nai na kalleshi sai na ga murmushi a fuskarsa.
“I know za ki yi mamaki ai, ni ma zuwan dole ya zame min kuma i think idan na samu yadda na ke so zan dawo ranar da na tafi”
A take na marairaice fuska kamar zan masa kuka.
Bana da wani fargaba ko tunani a gidan aurena bayan ta mutum biyu yayana da kuma Hajiya wato mahaifiyarsa domin na lura a duk zuwan da muke gaishewa kamar bata na'am da ni, bayan a baya kuma ba haka na santa ba, duk dai ba wani zuwa muke sosai ba amman a duk lokacin da muka je gaisheta ko kuma muka fito daga wani gurin muka biya sai ta yi min tarba ba a baya da kai ba, ko kuma ta bar a nan a falon ba ita kadai ba har yayanta mata biyu na lura haka suke min basa son fira da ni balle kuma irin wasar nan ta matar yaya, namijin ne kawai babu ruwansa shi kan idan muka tarar da shi a gida mu yi ta fira abun kamar ba kanen mijina ba, amman bayan wannan bana da wata matsala da Abdulhamid idan ka cire na kyamar yayana da yake yi, domin na lura ko zancensu baya son ina yi idan aka kira waya da sunan za mu gaisa da su a lokacin da yake kusa da ni da a take yanayinsa zai canja, be taba siye ko da biscuit din maira goma ya mika min ko ya bawa wani yace a kai musu balle kuma har ya tambayi lafiyarsu ko karatunsu, sai dai ina masa uzuri da wannan ganin cewar shi din be taba aure ba sai yanzu kuma daman can ba mutum ne mai son yara ba, ballanta na san yadda wasu mazan suke basa son yayan wasu a kusa da su, musamman Abdulhamid da na lura da alamar yana ďan da kishi ba kamar wasu ba, tun daga lokacin da yai kokarin hana ni aikina na lura da hakan ga kuma ya hana yin ko. Wane irin social media saboda kar na hadu da maza, yana yawan fada min cewar na rike masa kaina na tsare masa kaina kar na bar shaidan ya rinjaye ni, wani lokacin na kan amsa masa da to ko nai masa alkawarin haka ba wani lokacin kuma sai dai na yi dariya, domin a tunani babu abunda zai kai ni na aikata wani alfama ko da bana da aure balle ina da shi, ba wai na fi karfin shaidan ba ne, kawai dai ina tuna baya ne a lokacin da Aminu zai iya shafe wata da watannani ba neme ni ba kuma babu kulawa da magana mai dadi ga shi ina zuwa aikin ina ganin mazan amman ban aikata ba, balle yanzu da nake auren mutumen da ya san darajar aure kuma bana ganin mazan ma, to mi kam Allah na tuba wace tsiyar ce zata saka ni aikata hakan.
A zaman aure da Abdulhamid wani abun da zai baka mamaki shine rashin iya girki, wanda ni kaina yake bani mamaki kuma ya ba ni tsoro, tun da na zo gida ban taba dora girki ko da ruwan zafi ne ya tafasa ba, idan na dora miya yadda na hada ta haka zan zo na tararda ita haka tuwo ma, shiyasa ban taba yin jalof ba lalle shimkafa da wake, indai har za mu sha tea sai dai Abdulhamid ya dora mana, indai har ni na dora ba zai tafasa ba ko da kuwa a gas ne ko electric kettle. Sai dai be taba sakawa Abdulhamid ya min fada ko nuna bacin ransa a hakan hakan ba, kullum safe shi zai dora mana ruwan da za mu amfani da su da rana kuma yai mana take away haka ma da dare, na kuma rasa gane dalilin haka bayan a can baya na iya girki na kamar ko wace mace, amman tun da na tsinci kaina a gidan Abdulhamid sai komai ya lalace.
Ranar wata labara da misalin sha daya da yan mintuna na ji an buga kofar falona, na yi tsamammi ko daya daga cikin yan matan gidan mu ne hakan yasa na tashi da kuzari na bude, abun mamaki sai nai arba da Suwaiba matar Abdallah kuma uwar yayansa mata guda biyu, na yi mamakin maganinta domin ta dade tana min waken zuwa amman bata zo ba sai yau, mun sha fira a ranar daman can Suwaiba mace ce mai son fira da far'a da haba haba da jama'a, ban yi zaton Abdallah ya kawo ta ba har da ta labarta min cewar shi ya kawo ta amman ya aje ta gurin gate wai yana sauri jaye gurin aiki.
Ta labarta min abubuwa da yawa a ciki har da na rashin son yara da Abdulhamid yake da shi, sannan ta dora min da cewar yawanci maza basa son yayan da ba na su ba, balle kuma Abdulhamid da yake saurayi, tana ta nanata min cewar sai na yi hakurin haka kamar ta san abunda ya fi damu na kenan, duk kuwa da kasancewar ban taba fadawa kowa ba.
Ganin na dauki waya na kira Abdulhamid na ce yai mana takeaway sai abun yai ta bata mamaki.
“Kar dai ace har yanzu baki fara girkin ba, ko kuwa amarcin ne ya motsa kike jin ba za ki iya dafawa ba?”
Dariya nai kamin na bata masa.
“Wallahi ba haka ba ne, idan na dora girkin baya dahuwa yadda na saka shi haka zan tararda shi kuma ga wuta ga komai amman ba ya yi”
“Too kar dai ace Abdulhamid ma yana da kohi kamar Abban Suhaima, ni ma idan nai masa wani laifin ko kuma na bata masa rai haka zan dafa abinci a ranar ba zai dafu ba sai na bashi hakuri”
Ta fada tana dariya... Ni ma dariyar nai sai dai ba irin ta ta domin ni wani tunanin ne ya zo min, kar dai ace Abdallah ne yai min kohi nake ta samun wannan matsalar?
“Ko da yake shi ma a tawaye ne dole za a samu dukansu suna yi, wata kila wani abun kika masa sai kin ba shi hakuri sannan za ki daidaita, amman fa ni kin san da na dauka ko Abdulhamid ba shi da kohi”
Zancenta ne ya dawo da ni daga duniyar tunani sai na sake yin murmushi a karo na biyu.
“Haka ne ai wani ba a iya ganewa sai idan wani abun ya faru”
“Haka ne”
Sai guraren karfi biyu ya kirata a waya yace ta fito bakin gate yana jiranta, a lokacin Abdulhamid be dawo ba, sai na saka Hijabina na rakata har gurin motarsa bayan na deba mata wasu abubuwan daga turaruka na da kayan kwaliya, gilashin motarsa a sauke yake amman ko da wasa Abdallah be dago ya kalleni ba da na gaishe ma sai ya amsa min a gajarce kamar be san ni ba, bayan sun wuce na dawo ciki gidan ina ta nazarin kalamanta. Daga karshe na yanke shawarar kiran Abdallah nai masa magana, haka kuwa akai bayan Abdulhamid ya dawo mun ci abinci mun yi fira ya fita sallah la'asar ni kuma na nemo number Abdallah ya aika masa kira, ringing tai kamar zata katse sannan ya daga, ban tsaya yi masa sallama ba balle gaisuwa kai tsaye na ce.
“Abdallah magana na ke son mu yi”
Sai na yi shiru bayan na fada masa hakan ina jiran na ji amsar da zai ba ni kamin na dora amman be ce min komai ba har sai da nai zaton ko wayar ta katse ne.
“Idan ka kullace ni da wani abun dan Allah ka kwance, tun da na zo gidan nan kullum nai girki ba ya yi”
“Babu hannuna a ciki”
Ya amsa da muryar da na jita kamar ba ta shi ba.
“Wata kila kana jin haushina ne, ko kuma kana jin bacin rai a kaina ne”
“Ban taba jin haushinki ba, kuma ba ki bata min rai ba, abunda kika aikata ne kawai idan na tuna ina jin babu dadi ne”
“To ka daina jin babu dadin, shiyasa bana iya girkin idan na yi ba yayi, dan Allah ka kwance Kohin da kai min”
Ina iya jiyo saukar numfashinsa kamin ya ce.
“Ban kullace ki da komai ba Halimatu, ke yanzu yar'uwata ce kawai kuma matar dan'uwana, yan'uwanta ta fi gaban wasa ko babu Abdulhamid babu abunda zai shiga tsakanin mu”
Yana fada min hakan ya kashe wayar, a take wani abun marar dadi ya kawo ma zuciyata ziyara. Har na gabatar da sallah la'asar ban daina jinsa ba, bayan sallah isha'i ina kwance saman kujera falo Abdulhamid ya fito daga bedroom ya nufo inda nake kwance, sumbatar kaina yai kamin ya daga ni na tashi zaune sai ya zauna sannan ya kwantar da kaina saman kijinsa yana shafa fuskata.
“Gobe fa ina tunanin zanje Abuja”
Dagowa nai na kalleshi sai na ga murmushi a fuskarsa.
“I know za ki yi mamaki ai, ni ma zuwan dole ya zame min kuma i think idan na samu yadda na ke so zan dawo ranar da na tafi”
A take na marairaice fuska kamar zan masa kuka.