Sashe 131
Gobe Na Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Wallahi ni nai kamar na saka kuka a gurin, da wanne zan ji da abunda Hajiya tai min ko da na Ahmad? Ko kuma da kaunar da suke nuna min ni da yayana? Sai na rasa da wane baki zan yi mata godiya na rasa kalmomin da zan hada su isar da sakon godiyata yadda ya kamata.
Ban wani dade sosai ba Ahmad yace na taso ya maida ni gida, Hajiya bata bar ni a fito haka nan ba, sai da ta hada min yan turaruka da man shafawa kamar yadda ta saba ta bawa Siyama ta kawo min.
Tun da muka bar gidan na kasa dauke idona akan Ahmad, wani irin kaunarsa da kimarsa suka cika min ido, farincikin da nake ji a raina ma shine sila, ina ta tunanin kalar da zan siye yanzu ya dauke min wannan nauyin.
“What”
Ya tambaya yana murmushi ganin irin kallon da nake masa. Sai ya kai hannunsa ya kamo hannuna ya saka yatsunsa cikin nawa kana ya sumbacin hannun nawa.
“Na san zaki ce zaki wahalarda kanki gurin siyen kaya wata kila dan abunda ke gareki ma ya kare, so tun da ina da hali da dama me zai sa na bari ki yi? I just wanted you to know that ke nake so, kuma ina son farincikinki”
“Thank you, i mean Thank you”
“You shouldn't”
Ya fada yana kara kissing din hannuna, da hannu daya yake tuki dayan hannun kuma yana rike na nawa hannun har muka isa wani shagon dinki.
“Zauna a nan ina zuwa”
Na fada min sannan ya bude motar ya fita, ya shiga shagon sai gashi ya fito tare da wata mace kabila, sai da ya shiga ya zauna sannan ta leko ta gilashin motar ta gaishe da da far'arta.
“Ya aikin ya gidan?”
“Lfy kalau Alhamdulillah, ki fada min address dinki zan zo na auna ki”
Na fada mata kamar yadda ta bukata sannan ya tashi motar muka bar wajen, mun dan yawata cikin gari kamin ya dawo da ni gida sai zolayata yake wai yana da kanwar hannu a dube ni ban tare ba amman har na yi fresh skin dina sai shinning har wani jan kumatuna yake.
“Allah kin ma fini fari fa, ji hancin har tsawo ya kara”
“To ai ba kai ya kamata ka fada ba mutane ya kamata ace sun fada”
Kallo tai baki sake.
“Su waye mutane? Baki san ni bane lims a kalleki ace kin yi kyau? Hmmmm”
“To ai mata ba maza ba”
“Har matan mana baki san yanzu akwai mata yan iska masu kwacewa miji mata ba? Maganar Allah ni ko mace ba zan yarda ta tsare ki da ido ba ba yarda zan yi ba”
Bude motar nai na fita ina dariya sai ya sauke gilashin motarsa ya kira ni jiyowa nai na dawo.
“Ina son na fada miki for the very last time bana son wata mu'amala na shiga tsakaninki da Aminu, na san akwai yayansa amman na dauke masa komai idan ba abunda ya zama dole ne a matsayin na uba ya gabatar da shi ba, idan zai yi magana da ke akan komai ya kira wayata da ni zai yi magana ni kuma sai nai magana da ke”
Babu alamun wasa a maganarsa kamar yadda fuskarsa ta nuna.
“In-Sha-Allah”
Ya gyada min kai ya bi ni da kallo har na shige cikin gida sannan na ji tashin motarsa.
Bayan kamar thirty minutes da dawowata mai dinki ta isko ni har gida ta auna ni.
ABDALLAH POV.
A cikin ko wane shafin rayuwar dan'adam akwai kaddarar rayuwarsa mai kyau ko marar kyau, wani ta so masa da sauki wani da wahala wani daga karshe ya samu cikar buri wani kuma ya koma a gurin mahallincinsa ba tare da rai ya samu abunda yake so ba.
Sai dai yarda da ko wace irin kaddara yana cikin cikar imanin bawa, yarda samu da rashi na Allah ne yana karawa bawa kwanciyar hankali da wadatar zuci, a iya yarda yanzu kam Abdallah ya yarda akwai son Halimatu a cikin kaddararsa, akwai rashin aurenta a tarihin rayuwarsa.
Iyakar hijadin da yai ne shine na rufe babin tahirin sonta a zuciyarsa wanda a da ya kasa haka sai a yanzu da ya yarda da kaddararsa kuma ya yarda ya rasa Halimatu har abada! Domin ko bayan Ahmad da yake da tabbacin ba zai sake ta ba, idan ma ta Allah ta kasance ace ya mutu ita tana raye aurenta ba zai taba yuyuwa ba domin Hajiya tace ko bayan ranta bata yafe nasa ya auri Halimatu ba, a dayan bangaren kuma idan ya zauna yai tunani a yanzu da son kai ya fitar masa a zuciyata, ya kan tausayawa dan'uwansa na rayuwar da yai da kuma wacce sai fuskanta a gaba, sai a yanzu ne yake ganin rashin dacewar auren Halimatu bayan kuma dan'uwansa yana raye, a yanzu yana jin cewar Halima ta cancani farinciki ko da ba a gurinsa ba ne idan har zata samu farinciki da kwanciyar hankali ya kamata ya kyaleta tun da ba zai taba aurenta ba, sai a yanzu yake nadamar neman aurenta da yai da auren wani akanta sai a yanzu gane girman laifin daya aikata a wacan lokacin idonsa ya rufe baya iya ganin laifin kansa baya iya ganin laifin Halima saboda so ya rufe masa ido da kuma neman haihuwar namiji.
Sai dai har zuciyarsa na dauke da kaunar da kuma muradin son haihuwar namiji domin maradinsa ne tun kamin yai aure, har yanzu ya kasa sauke burin da yake da yakinin ba zai taba tabbatuwa ba domin dan'uwansa ya riga ya soke shi da mashi.
Abubuwa uku suka fi tsaya masa a rai, haihuwar Namiji, matsalar dan'uwansa sai kuma damuwar da Mahaifiyarsa ta dauka ta saka a ranta na matsalar Abdulhamid.
HALIMATU POV.
Na yi zaton kamin na tare za a kawo min kayan duk kuwa da kasancewar ban masa maganar lefe ba, amman shiru ana ta shirye shiryen tarewar amman be aiko min da komai daga cikin sutura ba, hakan yasa na cire kudina na siye tufafina masu kyau lace da Atamfa da shadda lace yar ubansu a gurin Khadeeja Candy, na kaiwa tela ya dinka min tun kamin ranar da za a tare din.
Ba wani shirye shirye zan yi ba, bayan wunin biki wanda ya zama al'ada a ko wane biki na budurwa ko bazawara, ana sauran kwana uku wunin alert ya shigo watana mai nauyi har sai da na zare ido, ina ganin sunan wanda ya turo min nai murmushi na shiga contact list da zimmar kiransa sai ga kirashi ya shigo wayata. Cikin shauki da kauna na dauki kiran ina murmushi kamar ance yana gabana.
“Na ga Alert”
“Eh abububuwan da za ku yi na mothers day din, za su iya dai ko?”
“Haba dai wannan kudin ai yayi yawa”
“Da gaske?”
“Haba dai”
Na fada a shagwabe sai shi ma ya rama yadda nai masa.
“Haba dai Babe”
Daga ni har shi sai muka saka dariya kamin ya dauko min zancen yadda su a nasu gidan za su yi masu wunin da irin abubuwan da za su tsara nima na fada masa abubuwan da nake son yi da rabawa mutane.
Wanda yake cewa ba zai barni nai sati biyu a gida ba sai gani na yi wata har yan kwana biyu sama domin shi ma kansa da babu ishesshen lokaci ba zai samu damar aiwatarda komai na gidansa ba, Hajiya ma ba zata samu wadataccen lokacin yin wani abun ba, balle kuma ni uwar bikin gaba daya.
Na yi gayyata sosai har wandanda ba su san na yi aure ba sai da suka sani, an dafa abincin kusan kala hudu domin Ahmad ya wani wadataccen kudin da zan yi duk abunda nake so har na rage, lemu ma kala kala a siya, bayan yan abubuwan dande dande da lashe lashe da ake sakawa a takeway da kaskon turare da turaren wutar da kofi ko plate a bawa mutum idan zai je gida.
Nina makeupover (I like you girl 😘) ce ta gyara min fuskata na fito kamar wata yar sha biyar kowa sai yaba ni yake, ga dinkina dan ubansu na farin lace da farin mayafi kana ganina a cikin jama'a kasan ni ce amarya domin na haska kowa, duk wanda ya ganni sai yace na yi kyau. Na jidadin da Ahmad ya aiko mana da mai daukar hoto duk kuwa da kasancewar ya san akwai waya amman hakan be hana shi turo kwararen mai daukar hoto ba.
Cikin farinciki da jindadi akai yinin biki kowa sai sambarka yake, bayan sallah isha'i manyan motocin na alfarma suka faka kofar gidanmu kowa sai kallo yake wadanda ba su san wa zai aura ba a unguwar sai kallo ake ana mamaki masu neman salsala kuma suka fara.
Mama da Inna sun min nasiha sosai akan hakuri da biyaya kamar yadda suka saba min a kowane aure nawa da nake na dawo, sai dai wannan bana fatar dawowar fatana ba rubuwa da Ahmad har sai ta Allah ta kasance.
Yan'uwan mahaifina ma sun min nasiha suka min fatan alheri tare da addu'ar Allah yasa gidan zamana ne.
Ana kokarin fita da ni Hafiza ta zo ta rada min a kunne.
“Lims din Amadu dan Allah idan kin yi sallah ki saka da mu a addu'arki Allah ya kawo na mu na gari, wadannan yan iskan samarin masu zuwa zance kawai ba neman aure sai bakin rowa Allah ya bamu da su”
Dariya nai na kalleta sai tace.
“Wallahi fa ki duba aure na uku kika yi, mu nuna nan ko daya ba mu yi ba, kuma ba farin jinin ne babu ba, masu son auren da gaske ne basa zuwa”
“Komai ai yana da lokaci Hafiza, ni din da na riga ku aure baki ga yadda auren ya kasance min ba? Kowa ai da jarrabawarsa, wani abun nesa yake wani a kusa, idan akai hakuri za a cin ma komai”
Ban wani dade sosai ba Ahmad yace na taso ya maida ni gida, Hajiya bata bar ni a fito haka nan ba, sai da ta hada min yan turaruka da man shafawa kamar yadda ta saba ta bawa Siyama ta kawo min.
Tun da muka bar gidan na kasa dauke idona akan Ahmad, wani irin kaunarsa da kimarsa suka cika min ido, farincikin da nake ji a raina ma shine sila, ina ta tunanin kalar da zan siye yanzu ya dauke min wannan nauyin.
“What”
Ya tambaya yana murmushi ganin irin kallon da nake masa. Sai ya kai hannunsa ya kamo hannuna ya saka yatsunsa cikin nawa kana ya sumbacin hannun nawa.
“Na san zaki ce zaki wahalarda kanki gurin siyen kaya wata kila dan abunda ke gareki ma ya kare, so tun da ina da hali da dama me zai sa na bari ki yi? I just wanted you to know that ke nake so, kuma ina son farincikinki”
“Thank you, i mean Thank you”
“You shouldn't”
Ya fada yana kara kissing din hannuna, da hannu daya yake tuki dayan hannun kuma yana rike na nawa hannun har muka isa wani shagon dinki.
“Zauna a nan ina zuwa”
Na fada min sannan ya bude motar ya fita, ya shiga shagon sai gashi ya fito tare da wata mace kabila, sai da ya shiga ya zauna sannan ta leko ta gilashin motar ta gaishe da da far'arta.
“Ya aikin ya gidan?”
“Lfy kalau Alhamdulillah, ki fada min address dinki zan zo na auna ki”
Na fada mata kamar yadda ta bukata sannan ya tashi motar muka bar wajen, mun dan yawata cikin gari kamin ya dawo da ni gida sai zolayata yake wai yana da kanwar hannu a dube ni ban tare ba amman har na yi fresh skin dina sai shinning har wani jan kumatuna yake.
“Allah kin ma fini fari fa, ji hancin har tsawo ya kara”
“To ai ba kai ya kamata ka fada ba mutane ya kamata ace sun fada”
Kallo tai baki sake.
“Su waye mutane? Baki san ni bane lims a kalleki ace kin yi kyau? Hmmmm”
“To ai mata ba maza ba”
“Har matan mana baki san yanzu akwai mata yan iska masu kwacewa miji mata ba? Maganar Allah ni ko mace ba zan yarda ta tsare ki da ido ba ba yarda zan yi ba”
Bude motar nai na fita ina dariya sai ya sauke gilashin motarsa ya kira ni jiyowa nai na dawo.
“Ina son na fada miki for the very last time bana son wata mu'amala na shiga tsakaninki da Aminu, na san akwai yayansa amman na dauke masa komai idan ba abunda ya zama dole ne a matsayin na uba ya gabatar da shi ba, idan zai yi magana da ke akan komai ya kira wayata da ni zai yi magana ni kuma sai nai magana da ke”
Babu alamun wasa a maganarsa kamar yadda fuskarsa ta nuna.
“In-Sha-Allah”
Ya gyada min kai ya bi ni da kallo har na shige cikin gida sannan na ji tashin motarsa.
Bayan kamar thirty minutes da dawowata mai dinki ta isko ni har gida ta auna ni.
ABDALLAH POV.
A cikin ko wane shafin rayuwar dan'adam akwai kaddarar rayuwarsa mai kyau ko marar kyau, wani ta so masa da sauki wani da wahala wani daga karshe ya samu cikar buri wani kuma ya koma a gurin mahallincinsa ba tare da rai ya samu abunda yake so ba.
Sai dai yarda da ko wace irin kaddara yana cikin cikar imanin bawa, yarda samu da rashi na Allah ne yana karawa bawa kwanciyar hankali da wadatar zuci, a iya yarda yanzu kam Abdallah ya yarda akwai son Halimatu a cikin kaddararsa, akwai rashin aurenta a tarihin rayuwarsa.
Iyakar hijadin da yai ne shine na rufe babin tahirin sonta a zuciyarsa wanda a da ya kasa haka sai a yanzu da ya yarda da kaddararsa kuma ya yarda ya rasa Halimatu har abada! Domin ko bayan Ahmad da yake da tabbacin ba zai sake ta ba, idan ma ta Allah ta kasance ace ya mutu ita tana raye aurenta ba zai taba yuyuwa ba domin Hajiya tace ko bayan ranta bata yafe nasa ya auri Halimatu ba, a dayan bangaren kuma idan ya zauna yai tunani a yanzu da son kai ya fitar masa a zuciyata, ya kan tausayawa dan'uwansa na rayuwar da yai da kuma wacce sai fuskanta a gaba, sai a yanzu ne yake ganin rashin dacewar auren Halimatu bayan kuma dan'uwansa yana raye, a yanzu yana jin cewar Halima ta cancani farinciki ko da ba a gurinsa ba ne idan har zata samu farinciki da kwanciyar hankali ya kamata ya kyaleta tun da ba zai taba aurenta ba, sai a yanzu yake nadamar neman aurenta da yai da auren wani akanta sai a yanzu gane girman laifin daya aikata a wacan lokacin idonsa ya rufe baya iya ganin laifin kansa baya iya ganin laifin Halima saboda so ya rufe masa ido da kuma neman haihuwar namiji.
Sai dai har zuciyarsa na dauke da kaunar da kuma muradin son haihuwar namiji domin maradinsa ne tun kamin yai aure, har yanzu ya kasa sauke burin da yake da yakinin ba zai taba tabbatuwa ba domin dan'uwansa ya riga ya soke shi da mashi.
Abubuwa uku suka fi tsaya masa a rai, haihuwar Namiji, matsalar dan'uwansa sai kuma damuwar da Mahaifiyarsa ta dauka ta saka a ranta na matsalar Abdulhamid.
HALIMATU POV.
Na yi zaton kamin na tare za a kawo min kayan duk kuwa da kasancewar ban masa maganar lefe ba, amman shiru ana ta shirye shiryen tarewar amman be aiko min da komai daga cikin sutura ba, hakan yasa na cire kudina na siye tufafina masu kyau lace da Atamfa da shadda lace yar ubansu a gurin Khadeeja Candy, na kaiwa tela ya dinka min tun kamin ranar da za a tare din.
Ba wani shirye shirye zan yi ba, bayan wunin biki wanda ya zama al'ada a ko wane biki na budurwa ko bazawara, ana sauran kwana uku wunin alert ya shigo watana mai nauyi har sai da na zare ido, ina ganin sunan wanda ya turo min nai murmushi na shiga contact list da zimmar kiransa sai ga kirashi ya shigo wayata. Cikin shauki da kauna na dauki kiran ina murmushi kamar ance yana gabana.
“Na ga Alert”
“Eh abububuwan da za ku yi na mothers day din, za su iya dai ko?”
“Haba dai wannan kudin ai yayi yawa”
“Da gaske?”
“Haba dai”
Na fada a shagwabe sai shi ma ya rama yadda nai masa.
“Haba dai Babe”
Daga ni har shi sai muka saka dariya kamin ya dauko min zancen yadda su a nasu gidan za su yi masu wunin da irin abubuwan da za su tsara nima na fada masa abubuwan da nake son yi da rabawa mutane.
Wanda yake cewa ba zai barni nai sati biyu a gida ba sai gani na yi wata har yan kwana biyu sama domin shi ma kansa da babu ishesshen lokaci ba zai samu damar aiwatarda komai na gidansa ba, Hajiya ma ba zata samu wadataccen lokacin yin wani abun ba, balle kuma ni uwar bikin gaba daya.
Na yi gayyata sosai har wandanda ba su san na yi aure ba sai da suka sani, an dafa abincin kusan kala hudu domin Ahmad ya wani wadataccen kudin da zan yi duk abunda nake so har na rage, lemu ma kala kala a siya, bayan yan abubuwan dande dande da lashe lashe da ake sakawa a takeway da kaskon turare da turaren wutar da kofi ko plate a bawa mutum idan zai je gida.
Nina makeupover (I like you girl 😘) ce ta gyara min fuskata na fito kamar wata yar sha biyar kowa sai yaba ni yake, ga dinkina dan ubansu na farin lace da farin mayafi kana ganina a cikin jama'a kasan ni ce amarya domin na haska kowa, duk wanda ya ganni sai yace na yi kyau. Na jidadin da Ahmad ya aiko mana da mai daukar hoto duk kuwa da kasancewar ya san akwai waya amman hakan be hana shi turo kwararen mai daukar hoto ba.
Cikin farinciki da jindadi akai yinin biki kowa sai sambarka yake, bayan sallah isha'i manyan motocin na alfarma suka faka kofar gidanmu kowa sai kallo yake wadanda ba su san wa zai aura ba a unguwar sai kallo ake ana mamaki masu neman salsala kuma suka fara.
Mama da Inna sun min nasiha sosai akan hakuri da biyaya kamar yadda suka saba min a kowane aure nawa da nake na dawo, sai dai wannan bana fatar dawowar fatana ba rubuwa da Ahmad har sai ta Allah ta kasance.
Yan'uwan mahaifina ma sun min nasiha suka min fatan alheri tare da addu'ar Allah yasa gidan zamana ne.
Ana kokarin fita da ni Hafiza ta zo ta rada min a kunne.
“Lims din Amadu dan Allah idan kin yi sallah ki saka da mu a addu'arki Allah ya kawo na mu na gari, wadannan yan iskan samarin masu zuwa zance kawai ba neman aure sai bakin rowa Allah ya bamu da su”
Dariya nai na kalleta sai tace.
“Wallahi fa ki duba aure na uku kika yi, mu nuna nan ko daya ba mu yi ba, kuma ba farin jinin ne babu ba, masu son auren da gaske ne basa zuwa”
“Komai ai yana da lokaci Hafiza, ni din da na riga ku aure baki ga yadda auren ya kasance min ba? Kowa ai da jarrabawarsa, wani abun nesa yake wani a kusa, idan akai hakuri za a cin ma komai”