← Book details Gobe Na Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 98 OF 136

Sashe 98

Gobe Na Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Na amsa tare da amsa sallamar yaron dake ta doko sallama tun daga kofar gida.

“Wai ance ana sallama da Halima”

“Je kace waye”

Yaron ya fita be dade ba ya dawo yace.

“Yace wai Abraham ne”

“Je kace gani nan zuwa

Bayan yaron ya wuce Mama ta kalleni tace.

“Abraham kuma? Wane irin sunana ne wannan?”

“Mama bari na dawo dai”

Na tashi already ina sanye da Hijab dina na nufi kofar waje, a inda ya saba tsayuwa ya tsaya, ni kuma na karasa gurin ina tunanin da me kuma zo wannan karon.

“Gani”

Na fada ina kallonsa. Sai ya fito daga cikin motar da yake zaune ya kalleni.

“Na taba fada miki ina son ki”

“Ka sha fada min”

Sai yai murmushi mai sauti.

“Ina son ki Halima, ko da ba zaki so ni ba ni dai ina sonki, na kwanta da mata da yawa, ba su yi ciki ba sai ke da nai ma fyade, likito ma sun fada min ba zan iya haihuwa ba saboda kwayoyin halittata ba su da karfin da zasu ba mace ciki, na sha magani har na gaji, amman ji just one mistake kikai ciki, mi zai saka ba zan so ki ba? Na fada miki rayuwata tana cikin hadari zan iya mutuwa a ko yaushe, domin a duk lokacin da asirina ya tonu wow....”

Sai yai shiru yana sotsa bakinsa.

“Na kamu da mugun son ki, ba zan iya cutar da ke ba, idan ma tsoro kike ji ki daina, ki kwantar da hankalinki ki daina sakawa ana bincike akaina, domin idan asirina ya tonu bomb....”

Ya fada yana cikawa bakinsa iska, ni kam mamaki ya gama cika ni, sakawa ana bincike akansa kuma?

“Ni ban saka kowa yai bincike ka ba”

“To wa ya saka? Mutumen nan ko? Why kika fada masa sirrina”

“Ni ban fada masa ba”

“Ya za'ayi ya sani idan ba ki fada masa ba”

“A wasikar da na rubuta ranar children day ya ji”

“Ko mutum yaji idan be san ki ba ba zai gane waye ba just tell me the truth”

“Ban maka karya ba, labarin yarsa da kamfaninsa ya shigo ciki shiyasa ya gane cewar nice, a ranar da ya gan ni da kai kuma sai ya gane cewar kai ne mutumen da ke bibiyata”

“Okay.....”

Ya furta kamar mai nazari.

“Saurayinki ne?”

“Why”

“Nothing”

Ya amsa ni fuska ba yabo ba fallasa.

“Miya ssmu goshinki?”

“Na ji ciwo ne”

“Garin ya?”

Na yi shiru ban amsa shi ba, be sake ce min komai ba, ya bude motarsa ya shiga, ta gilashin motar ya miko min bandir din yan 1000.

“Zaki iya yin wani abu”

“Na gode”

Na fada ba tare da na karbi kudin ba na juya.

“Halima magana ta karshe ina rokonki dan Allah ki amince ki aure ni, i promise you zan kula da ke ba zan taba barin ki samu damuwa ba, ban ce ki so ni auren kawai nake bukata dan Allah”

Juyowa nai na kalleshi hannayensa biyu a hade suke alamar rokona yake yi.

“Dan alfarmar Annabinki, dan Alfarmar Addininki, dan darajar mahaifinki, i promise you zan kula da yayanki zan taimaki familynki zan saka ki cikin farinciki marar misaltuwa”

Kasa ce masa komai nai jiki a sanyaye naa juya na dawo gida, zuciyata na kyautata zaton Ahmad ne ko Abdallah yake bincike akansa.

AHMAD POV.

Zaune yake a dakin Hajiya hannunsa rike da karamin plate wanda aka zubawa kwadon zogale da yaji kayan hadi ga tumatir da albasa a ciki.

“Kasan Khadija ai ta gama karantarta”

“Wace Khadija?”

“Khadija dai, yar Hajiya Hanne”

“Okay na gane”

“Shekarar nan zata fara service”

“Okay congrats to her”

“Shine shekaranjiya na ke yi ma mahaifiyarta maganarka nace me zai hana a hada ku?”

“What?”

Ya tsaya da cin zogalen da yake yana kallon Hajiya.

“Ni. Did i say ina son ta?”

“Tana da kyau ai”

“Ban ce bata da kyau ba Hajiya, ni ma ai ina da kyau, ammn ban ce miki ina sonta ba Hajiya”

“To ai naga ita din budurwa ce, kuma na san budurwa kake so shiyasa”

Kasa cewa komai yai kuma ya kasa hade zogalen da ke bakinsa, ya san Khadija tana da tarbiya ga kyau ga ilmin ga wayeye kuma gata budurwa amman shi har ga Allah be ji ta kwanta masa a rai ba, and taya zai yi facing mahaifintar kanwar mahaifiyarsa yace mata be amince ba? Why Hajiya zata masa haka? Siyama ce ta shigo dakin rike da waya tana latsawa.

“Yaya mutanen nan fa suna ta jiranka a falo”

“Oh ni wallahi har na manta da su, wai me suke so ne”

Hajiya ta fada tana kallon Ahmad, daker ya hade zogalen da ke bakinsa ya aje plate din yana kallon kanwarsa.

“Je ki fada musu, ba ni za su bawa hakuri ba, su je su roki Halima idan ta yafe musu then their son will be free”

Siyama ta yi wani fari da ido.

“Wace Halima kuma?”

“Just go and tell them”

Ba musu ta juya ta fice daga dakin.

“Wace Halima Gwarzo?”

“Halima dai matar nan mahaifiyarsu Namra, ex-husband dinta ne ya fasa mata goshi da motata”

“Garin ya”

Mikewa yai tsaye yana fadin.

“Ina zuwa”

Ya fice daga dakin Hajiya na binsa da kallo.

__________________
Halimatu & Aminu
Halimatu & Ahmad
Halimatu & Abdallah
Halimatu & Abraham

Bari muga Team da suka fi yawa.
7/21/21, 10:47 PM - Buhainat: *GOBE NA...*

By Khadeeja Candy

4️⃣9️⃣

A lokacin daya fito falon ya samu Mahaifiyar Aminu da wata yar'uwarta da dan'uwan mahaifinsa.
  Ganin Ahmad yasa suka kara marairaice fuska, shi kuma ya mikawa namijin hannu suka gaisa. Sannan ya amsa gaisuwar da mahaifiyar Aminu ke musu.

“Case din ba a hannuna yake ba, kuma ba ni aka jiwa ciwon ba, so if ita Halima tace ta yafe then ur son is free”

“To yanzu ita zamu je mu roka kenan?”

“Definitely”

Hajiyar Aminu ta marairaice fuska.

“Dan Allah dan Annabi ka taimaka mana, a saki Aminu hankalinmu duk a tashe yake”

“Haba Hajiya me kike so nace miki dan Allah? Idan Halima ta hafe masa Wallahi ba ni da matsala ni”

“Idan kai baka san ni ba ai ita Hajiya ta san ni, dan Allah kira min ita Yarinyar”

Ta karasa tana kallon Siyama, ba musu Siyama ta tashi ta nufi sama, bata dade ba ta sauko tana latsar waya.

“Gata nan zuwa”

Ba a bata lokaci ba Hajiya ta sauko ta zauna saman kujera, tana yi ma Hajiyar Aminu kallon rashin fahimta.

“Hajiya ina wuni?”

“Lafiya kalau ya gida?”

“Alhamdulillah Hajiya ba ki waye ni ba?”

“Wallahi ban gane ba, kila an kwana biyu”

“Be ke kika yi Shugabar lamurran mata ba, a lokacin Gwanna Garba Doru?”

“Eh Haka ne”

“Ni kuma ai na yi bawa matar Gwanna shawara a wacan lokacin”

“Allah sarki kin san abun da yawa, ya kwana biyu”

“Alhamdulillah, dan Allah Hajiya alfarma nake nema ki saka baki dan ki ya sako min da na Aminu, ance yana hannun sojoji dazun sun kira ta wayarshi suka sanar mana suka ce wai ya samu matsala da dan wajenki, shi kan shi Aminun na san be san Gwarzo ba da ba zai yi fada da shi ba Wallahi”

Hajiya ta kalli Ahmad.

“Wani abun ya hada ku ne?”

“No ba komai, kawai dai ina tare da Halima ne dazun mun je yin wani abu, sai ya fito a titi yana mana ihu kamar mahaukaci, kamin nai wani abu ya buga ta da mota, that's why na kira Faruk yasa a aka dauke min shi”

“Subhanallahi, to ita Halima ta san shi ne daman?”

Hajiyar Aminu ce ta amsa mata.

“Eh shine baban yayanta, tsohon mijinta ne da kaddara ta raba”

“Allah sarki, Gwarzo ka kyale shi dan Allah”

Ta karasa tana kallon Ahmad, shi ma kallonta yai.

“Ba ni da matsala Hajiya, kawai taje ta bawa Halima hakuri ita akai wa laifi idan ta hakura, shikenan ai ba matsala ba ce”

Hajiya ta sake kallonsu.

“To kuje ku ji ta bakinta idan ta amince a sake shi, ba matsala ba ne, tunda ita a kaiwa laifin yana da kyau aji ta bakinta”

“To Hajiya, bara muje indai Halima ce ai bata da matsala”

Cikin rashin jindadi Hajiya ta tashi tare da yan'uwanta suka fice. Siyama kamar jiran take su fita sai ta kalli Ahmad da sauri.

“Yaya ina kuka je hala?”

Kallonta yai yasan ba komai ke cinta ba sai gulma, ashe duk abunda ake hankalinta na gurin amman ta fake da latsar waya.

“Wani guri”

“Wani guri ina? Ya ganku a inda be dace ba ne?”

Tambayar da Hajiya tai masa tana kallonsa cike da son jin irin amsar da zai bata. Dan murmushi yai ya shafa kansa.

“No akan wani marar lafiya ne da nace zan dauki nauyin maganinsa, kuma ita ta san mutunen shiyasa muka je tare tai ma familynsa magana shine kawai”

Dariya Siyama tai.

“Oh kishi yake dan ya ga kana sonta”

“She's just my friend”

Ya amsa ba tare da ya kalleta ba.

“Yeah i mean friend, like friend....”

Ta maimaita tana yi ma Hajiya kallon gulma.

“Gwarzo ai baya son bazarawa, shiyasa na nema masa auren Khadija ai, budurwa ce kuma mai tarbiya”

Kallon Hajiya kawao yai ya dauke kai be ce uffan ba.

HALIMATU POV.
Chapter 98 · 0% Book details