Sashe 93
Gobe Na Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Yana fadar hakan yai gaba abunsa ya shiga cikin gurin, ya bar a bakin kofar tsaye da mamaki, to miye wani abun mamaki? Wata kila baya son aji muryarsa ne shiyasa yai haka. Umarninsa na bi na dauko wayar na kashe sannan na maida ta a jaka na shiga cikin gurin.
Ina shiga na fara rabon ido, babu mutane sosai amman kusan rabin taron duk turawa ne, wasu a taeburin manyan baki wasu a teburin masu daukar darasi irinmu, ga wani katon majigi da ke saman gurin wanda da shi suke ta nunawa mutane abubuwansu.
A zagayayyen tebur muka zauna ni da shi, sai dai kujerar tawa tana fuskantar tashi ne kamar yadda shi ma yake fuskanta ta, amman idonsa yana gurin abunda ake nunawa a majigin.
Nikam sam hankali baya gurin abunda ake fada yana gurin mutanen dake gurin ne, idan na kalli wannan na kalli wacan har na kallo Ahmad, da idon yai min alama da na maida hankalina gurin abunda ake, ba musu na tattara hankalina na maida gurin mutanen, muna zaune a gurin har kusan karfe daya. Direban dazun ne wanda ya kawo mu ya sake shigowa gurin ya nufo inda muke zaune ya kai bakinsa saitin kunnen Ahmad ya fada masa wani abu. A take na ga yanayinsa ya sauya, sai ya tashi tare da diraban suka fita, ni dai ina zaune a gurin har ya dawo a yanzu kuma baya kallon kowa sai ni, just me and me alone, har aka tashi daga taron 1,30pm bayan an bi ko wane tebur an dora takeaway da ruwa da lemu.
An yi mana hoto da turawan da kuma sauran wadanda suka zo taron, sannan mutane suka fara watsewa, nima na tashi ganin ogan ya tashi shi be dauki komai ba daga abunda aka kawo masa na sha da ci sai direbansa ne ya dauka ni kam na kai hannu na dauki abuna, ko ruwan ban bari ba, balle kuma yar karamar takadar da aka dora mana sama wacce nake kyautata zaton kudi ne. A kofar fitowa suke bawa mutane memo da magazine da kuma calender.
Sai da muka shiga motar sannan ya kalleni ya kalli kayan hannuna har na ji yar kunya.
“Ina wayarki?”
“Tana cikin jaka”
“Mu gani”
Ya zuro min farin hannunsa.
“Na kashe ta fa”
Ganin be janye hannun ba kuma be dauke idonsa daga kaina ba yasa na saka hannu a jakar na dauko wayar na mika masa, a zato na dubawa kawai zai yi ya bani sai na ga ya zura ta aljihu, kamar nai magana sai kuma wata zuciyar ta hana ni.
Ba mu yi nisa sosai da hotel din na ga direban ya faka motar gafe ya fita ya zaga bayan motar ya dauki abubuwan da ya dauko a gurin taron sannan ya rufe, Ahmad kuma ya fita daga motar ya shiga mazaunin direba yaja motar, ni kam ina zaune baya abuna sai dai sanyin ac yayi min yawa har na fara jin kamar ciwon kai na son kamani.
A nesa da masallacin gada biyu ya faka motarsa ya bude ya fita sannan ya zagayo inda nake ya bude min.
“Zanje nai sallah ki dawo gaba”
“Ban iya tukin mota ba”
“Ban ce ki tuka ba, a front seat zaki zauna”
Na fito na bar kayan a baya sannan na rufe motar na bude gidan gaba na zauna ina ta mamakin karbe min waya da yai, can kuma na tuna da abunda yai min jiya, wata kila dan kar ayi ta kirana ne muna tare kuma baya son hayaniyar kiran, amman ai sai ya bar min wayata yace kar na kunna.
Ni dai ina zaune a motar har aka sauko daga sallah juma'a mutane suna ta wuce, sannan ya bude motar ya shigo yai mata key muka hau titi, a hankali yake tukun kusan ko wace mota ta zo sai ta wuce mu, kusan da mu da masu tafiya kasa duk daya idan ma akwai tazara kadan ne.
“Kin na rasa yata ko?”
Na juyo na kalleshi sai na ga ba ni yake kallo ba, amman tabbas na san da ni yake domin daga ni sai shi ne a motar.
“Eh”
“Na rasa mahaifina ma, na rasa Matata mahaifiyar Baby”
Ya sake fada still be kalleni ba.
“Allah ya musu rahama”
Be amsa da amin ba, sai yai wata maganar ta dabam.
“You got lucky baki tana rasa kowa ba, the pain of losing someone is unforgettable, mahaifina na fara rasawa, mahaifina yana da ciwon suga, a lokacin da abun ya taso masa an fitar da shi waje, a cairo ya rasu a lokacin na shiga tashin hankali sosai, kin san saboda me?”
Na girgiza kai.
“Saboda Hajiyata, ya mace zata ji idan ta rasa mijinta? Ya da zai ji idan ya rasa mahaifinsa? Ya yar'uwa zata ji idan ta rasa mahaifinta? A lokacin nauyin Hajiya da Siyama da nawa ni kaina sai taro duk a kaina, tausayin kaina tausayin Hajiya tausayin Siyama, mu biyu kawai Allah ya bashi, daga ni sai Siyama, Hajiya tana son yayana sosai, sai dai duk haihuwarta yaranta rasuwa suke daga ni sai Siyama muka tsaya, shiyasa take son Siyama sosai wani lokacin tana kiranta da autarta, kamar yadda nima take so na sosai har take kishina, tana ganin kamar wata macen zata karbe mata ni, lokacin da muka rasa mahaifi komai na mu ya tsaya cak, ciki har da rayuwarmu domin mahaifinmu shine komai na mu, kullum Hajiya tana cikin damuwa Siyama ma haka”
Yayi shiru ya kai hannunsa ya dauki gorar ruwan da ke cikin motar ya bude ya kurba sannan ya aje.
“Daga lokacin na fara tunanin gina rayuwata, da ta mahaifiyata da kuma ta kanwata, a lokacin ne na fara neman aure har akai nasara na auri wata yarinya, she's my first wife but not my first love, domin na aureta ne ba wai dan na san miye soyayya ba a lokacin, a gida daban muka tare, daga lokacin da nai aure sai rayuwa ta ta canja daga matashi wanda yake zaune a gidan mahaifinsa zuwa mai mata da yake zaune a gidansa, na aje aikin da nake na soja a lokacin na cigaba da kula da kamfanin mahaifina na zinari, a cikin na bude makaranta wa Hajiyata duk wani abu na makaranta a hannun Hajiya yake zuwa, a da kullun tare da Hajiya muke karyawa komai kusan tare muke amman da nai aure sai abubuwa suka sauya, daga lokacin sai Hajiya ta fara ganin kamar matar da na aura tana kokarin mallake ni ne, sai ta cilasta min dole sai na dawo a cikin gidan mahaifina na kama part daya na zauna da ita, ita kuma tace ba zata zauna da Hajiya ba, daker na samu kanta ta amince muka zauna tare, sai kuma ta hanani cin abincinta tana cewa zata saka min magani a ciki, ta fara takura mata ta saka abubuwan da ya kamata ace mai aiki ce zatai, da ta kasa jurewa sai ta nemi fita Hajiya tace na sake ta, a haka nai aure har uku yana mutuwa saboda takurar Hajiya, ban zamu wacce ta dade ba sai mai sunanki, mace mai hakuri kamar ke, mai kawaici da sanin ya kamata, ita ta haifa min Baby Namra, a cikinta na biyu ne ta rasu, a ranar da ya rasu ni kaina bana iya gane kaina, domin rasa abokin rayuwa yana nufin rasa wani bangare na jikinka...”
Ya karasa muryarsa na rawa, hannuna na kai na dauki daya daga cikin tissue da ke cikin tissue ibox na mika masa sai ya karba.
“Thank you”
Ya tare gefen idonsa sannan ya sake kurba ruwan, ya bude gilashin motar iska ya shigo wata kila sanyin ac baya wadatar da shi.
“Sai ta bar ni da Baby, after that na sake aure biyu ya mutu, dayan saboda Hajiya dayan kuma saboda matar bata son Baby sai ta rika kishin yata tana ganin kamar ina nuna mata so da yawa ne, daga lokacin sai an gimgine maganar aure a gafe, na cigaba da rayuwata da yau da kullum, sai gashi na samu kaina cikin farinciki a haka muke rayuwa da kanwata da mahaifiyata da yata sai kuma sauran dangi na yan'uwa, amman dai a familyn mu mu kadai muka rage yayan Abbah, so the day I lost Baby, ba zan iya fada miki abunda naji ba, at first ban ji komai ba sai daga baya, kuma na kasa blaming kowa sai ke saboda a gurinta ta rasu, and she always talking about her friend i mean your daughter, tace na baki hakuri be kamata nai fada da mahaifiyar abokiyarta ba, so the day that i decided zan baki hakuri....”
A nan din m shiru yai sai hawaye ya gangaro ta gefen idonsa.
“Ina son yata sosai....”
Ya fada yana rumtse idonsa na wani lokaci kamin ya bude.
“Tana da sakewa, tana da kyauta duk da kasancewar ta karama, ga ta da wayo, ga son mutane bata da abokin shawara sai ni bata da abokin wasa daga ni sai Siyama wacce ta zame mata kamar kawa, sai kuma Hajiya wacce ta zame mata mahaifiya, Baby bata da kawa ko daya sai yarki da ta samu daga baya, that's why take yawan damun kanta kullum sai ta ganta.... ”
Ya lumshe idonsa yana sauke ajiyar zuciya da karfi.
“Abubuwa da yawa suna faruwa saboda ni, kai ma idan kana tare da ni wani abun zai iya samunka Dan Allah ka sauke ni a nan”
Na fada ina kawarda fuskata wasu hawaye masu zafi da radadi suna sauko min, a yau kan na manta da damuwata labarin Ahmad ya ban tausayi, domin rasa uba, ya, mata, abubuwa ne da basa fassaruwa da ko wane kalar yare. Murmushi yai ya miko min tissue da na bashi
“Take your tissue back”
Na karba na share hawayen, sannan ya miko min ruwa na karba na kurba sai na rike gorar, ina jin kamar wani hawayen zai sauko min.
“Can I imagine your life without your parents?”
Dam dam dam na ji gabana ya yanke ya fadi, kallonsa nai kamin na kalli gorar ruwan dake hannuna.
Ina shiga na fara rabon ido, babu mutane sosai amman kusan rabin taron duk turawa ne, wasu a taeburin manyan baki wasu a teburin masu daukar darasi irinmu, ga wani katon majigi da ke saman gurin wanda da shi suke ta nunawa mutane abubuwansu.
A zagayayyen tebur muka zauna ni da shi, sai dai kujerar tawa tana fuskantar tashi ne kamar yadda shi ma yake fuskanta ta, amman idonsa yana gurin abunda ake nunawa a majigin.
Nikam sam hankali baya gurin abunda ake fada yana gurin mutanen dake gurin ne, idan na kalli wannan na kalli wacan har na kallo Ahmad, da idon yai min alama da na maida hankalina gurin abunda ake, ba musu na tattara hankalina na maida gurin mutanen, muna zaune a gurin har kusan karfe daya. Direban dazun ne wanda ya kawo mu ya sake shigowa gurin ya nufo inda muke zaune ya kai bakinsa saitin kunnen Ahmad ya fada masa wani abu. A take na ga yanayinsa ya sauya, sai ya tashi tare da diraban suka fita, ni dai ina zaune a gurin har ya dawo a yanzu kuma baya kallon kowa sai ni, just me and me alone, har aka tashi daga taron 1,30pm bayan an bi ko wane tebur an dora takeaway da ruwa da lemu.
An yi mana hoto da turawan da kuma sauran wadanda suka zo taron, sannan mutane suka fara watsewa, nima na tashi ganin ogan ya tashi shi be dauki komai ba daga abunda aka kawo masa na sha da ci sai direbansa ne ya dauka ni kam na kai hannu na dauki abuna, ko ruwan ban bari ba, balle kuma yar karamar takadar da aka dora mana sama wacce nake kyautata zaton kudi ne. A kofar fitowa suke bawa mutane memo da magazine da kuma calender.
Sai da muka shiga motar sannan ya kalleni ya kalli kayan hannuna har na ji yar kunya.
“Ina wayarki?”
“Tana cikin jaka”
“Mu gani”
Ya zuro min farin hannunsa.
“Na kashe ta fa”
Ganin be janye hannun ba kuma be dauke idonsa daga kaina ba yasa na saka hannu a jakar na dauko wayar na mika masa, a zato na dubawa kawai zai yi ya bani sai na ga ya zura ta aljihu, kamar nai magana sai kuma wata zuciyar ta hana ni.
Ba mu yi nisa sosai da hotel din na ga direban ya faka motar gafe ya fita ya zaga bayan motar ya dauki abubuwan da ya dauko a gurin taron sannan ya rufe, Ahmad kuma ya fita daga motar ya shiga mazaunin direba yaja motar, ni kam ina zaune baya abuna sai dai sanyin ac yayi min yawa har na fara jin kamar ciwon kai na son kamani.
A nesa da masallacin gada biyu ya faka motarsa ya bude ya fita sannan ya zagayo inda nake ya bude min.
“Zanje nai sallah ki dawo gaba”
“Ban iya tukin mota ba”
“Ban ce ki tuka ba, a front seat zaki zauna”
Na fito na bar kayan a baya sannan na rufe motar na bude gidan gaba na zauna ina ta mamakin karbe min waya da yai, can kuma na tuna da abunda yai min jiya, wata kila dan kar ayi ta kirana ne muna tare kuma baya son hayaniyar kiran, amman ai sai ya bar min wayata yace kar na kunna.
Ni dai ina zaune a motar har aka sauko daga sallah juma'a mutane suna ta wuce, sannan ya bude motar ya shigo yai mata key muka hau titi, a hankali yake tukun kusan ko wace mota ta zo sai ta wuce mu, kusan da mu da masu tafiya kasa duk daya idan ma akwai tazara kadan ne.
“Kin na rasa yata ko?”
Na juyo na kalleshi sai na ga ba ni yake kallo ba, amman tabbas na san da ni yake domin daga ni sai shi ne a motar.
“Eh”
“Na rasa mahaifina ma, na rasa Matata mahaifiyar Baby”
Ya sake fada still be kalleni ba.
“Allah ya musu rahama”
Be amsa da amin ba, sai yai wata maganar ta dabam.
“You got lucky baki tana rasa kowa ba, the pain of losing someone is unforgettable, mahaifina na fara rasawa, mahaifina yana da ciwon suga, a lokacin da abun ya taso masa an fitar da shi waje, a cairo ya rasu a lokacin na shiga tashin hankali sosai, kin san saboda me?”
Na girgiza kai.
“Saboda Hajiyata, ya mace zata ji idan ta rasa mijinta? Ya da zai ji idan ya rasa mahaifinsa? Ya yar'uwa zata ji idan ta rasa mahaifinta? A lokacin nauyin Hajiya da Siyama da nawa ni kaina sai taro duk a kaina, tausayin kaina tausayin Hajiya tausayin Siyama, mu biyu kawai Allah ya bashi, daga ni sai Siyama, Hajiya tana son yayana sosai, sai dai duk haihuwarta yaranta rasuwa suke daga ni sai Siyama muka tsaya, shiyasa take son Siyama sosai wani lokacin tana kiranta da autarta, kamar yadda nima take so na sosai har take kishina, tana ganin kamar wata macen zata karbe mata ni, lokacin da muka rasa mahaifi komai na mu ya tsaya cak, ciki har da rayuwarmu domin mahaifinmu shine komai na mu, kullum Hajiya tana cikin damuwa Siyama ma haka”
Yayi shiru ya kai hannunsa ya dauki gorar ruwan da ke cikin motar ya bude ya kurba sannan ya aje.
“Daga lokacin na fara tunanin gina rayuwata, da ta mahaifiyata da kuma ta kanwata, a lokacin ne na fara neman aure har akai nasara na auri wata yarinya, she's my first wife but not my first love, domin na aureta ne ba wai dan na san miye soyayya ba a lokacin, a gida daban muka tare, daga lokacin da nai aure sai rayuwa ta ta canja daga matashi wanda yake zaune a gidan mahaifinsa zuwa mai mata da yake zaune a gidansa, na aje aikin da nake na soja a lokacin na cigaba da kula da kamfanin mahaifina na zinari, a cikin na bude makaranta wa Hajiyata duk wani abu na makaranta a hannun Hajiya yake zuwa, a da kullun tare da Hajiya muke karyawa komai kusan tare muke amman da nai aure sai abubuwa suka sauya, daga lokacin sai Hajiya ta fara ganin kamar matar da na aura tana kokarin mallake ni ne, sai ta cilasta min dole sai na dawo a cikin gidan mahaifina na kama part daya na zauna da ita, ita kuma tace ba zata zauna da Hajiya ba, daker na samu kanta ta amince muka zauna tare, sai kuma ta hanani cin abincinta tana cewa zata saka min magani a ciki, ta fara takura mata ta saka abubuwan da ya kamata ace mai aiki ce zatai, da ta kasa jurewa sai ta nemi fita Hajiya tace na sake ta, a haka nai aure har uku yana mutuwa saboda takurar Hajiya, ban zamu wacce ta dade ba sai mai sunanki, mace mai hakuri kamar ke, mai kawaici da sanin ya kamata, ita ta haifa min Baby Namra, a cikinta na biyu ne ta rasu, a ranar da ya rasu ni kaina bana iya gane kaina, domin rasa abokin rayuwa yana nufin rasa wani bangare na jikinka...”
Ya karasa muryarsa na rawa, hannuna na kai na dauki daya daga cikin tissue da ke cikin tissue ibox na mika masa sai ya karba.
“Thank you”
Ya tare gefen idonsa sannan ya sake kurba ruwan, ya bude gilashin motar iska ya shigo wata kila sanyin ac baya wadatar da shi.
“Sai ta bar ni da Baby, after that na sake aure biyu ya mutu, dayan saboda Hajiya dayan kuma saboda matar bata son Baby sai ta rika kishin yata tana ganin kamar ina nuna mata so da yawa ne, daga lokacin sai an gimgine maganar aure a gafe, na cigaba da rayuwata da yau da kullum, sai gashi na samu kaina cikin farinciki a haka muke rayuwa da kanwata da mahaifiyata da yata sai kuma sauran dangi na yan'uwa, amman dai a familyn mu mu kadai muka rage yayan Abbah, so the day I lost Baby, ba zan iya fada miki abunda naji ba, at first ban ji komai ba sai daga baya, kuma na kasa blaming kowa sai ke saboda a gurinta ta rasu, and she always talking about her friend i mean your daughter, tace na baki hakuri be kamata nai fada da mahaifiyar abokiyarta ba, so the day that i decided zan baki hakuri....”
A nan din m shiru yai sai hawaye ya gangaro ta gefen idonsa.
“Ina son yata sosai....”
Ya fada yana rumtse idonsa na wani lokaci kamin ya bude.
“Tana da sakewa, tana da kyauta duk da kasancewar ta karama, ga ta da wayo, ga son mutane bata da abokin shawara sai ni bata da abokin wasa daga ni sai Siyama wacce ta zame mata kamar kawa, sai kuma Hajiya wacce ta zame mata mahaifiya, Baby bata da kawa ko daya sai yarki da ta samu daga baya, that's why take yawan damun kanta kullum sai ta ganta.... ”
Ya lumshe idonsa yana sauke ajiyar zuciya da karfi.
“Abubuwa da yawa suna faruwa saboda ni, kai ma idan kana tare da ni wani abun zai iya samunka Dan Allah ka sauke ni a nan”
Na fada ina kawarda fuskata wasu hawaye masu zafi da radadi suna sauko min, a yau kan na manta da damuwata labarin Ahmad ya ban tausayi, domin rasa uba, ya, mata, abubuwa ne da basa fassaruwa da ko wane kalar yare. Murmushi yai ya miko min tissue da na bashi
“Take your tissue back”
Na karba na share hawayen, sannan ya miko min ruwa na karba na kurba sai na rike gorar, ina jin kamar wani hawayen zai sauko min.
“Can I imagine your life without your parents?”
Dam dam dam na ji gabana ya yanke ya fadi, kallonsa nai kamin na kalli gorar ruwan dake hannuna.