← Book details Gobe Na Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 74 OF 136

Sashe 74

Gobe Na Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

“Eh mun gaisa da shi”

Na fada ina yin kasa da idona saboda jan da sukai.

“Halimatu ayi hakuri da rayuwa, mun san mun yi kuskure mun laifi amman a dubi girman Allah a yafe mana wallahi yanzu Aminu yayi nadama
......”

Kaina na daga na kalli Hajiyar Aminu wacce ke maganar murya kasa kasa kamar za tai kuka, sai na kalli Mama nace.

“A nan za ki kwana? Ko ni zan tsaya na kula da ita?”

Sai Hajiyar Aminu tai karaf tace.

“A a ni zan kwana nan kuje ku hutarwarku”

Jin hakan yasa na mike tsaye nai musu sallama na fice. A daren ranar kasa bachi nai saboda tunanin rayuwar da nai a gidan Aminu, tabbas na fuskanci kalubale wanda ba ko wace mace ce zata iya jurewa ba. Da asuba bayan na yi sallah na dora da karatun qur'ane, misalin shida da yan mintuna na sha ruwa na koma bachi, bayan begen Abdallah da zuciyata ta kwanta da shi har da mafarkinsa sai da nai a bachin nan nawa na safe. Kiran waya ne ya farkar da ni duk kuwa da kasancewar bakuwar number ce hakan be hana ni dauka ba. Tun da sallamar matar ta daki dodon kunnena na gane mahaifiyar Aminu ce, ita ta fara miko min gaisuwa ni kuma na amsa mata da ina gajiya. Ta fada min wai kar a dafa komai tasa an kawo musu daga gida, ni dai da to kawai na amsa mata na aje wayar.
Misalin tara na shirya na cikin bakar abaya kamar yadda na fi son sakata a duk tufafina na fita da zimmar idan na bar gidan Abdallah na je asibiti, so nake na tafi na bawa Abdallah hakuri kuma na fada masa labarin mutumen nan, and i got lucky na tarar ya shirya cikin kananan kaya na shirin zuwa office. And wani karin farincikin kuma shi ya bude min kofar da kansa yana rike da mug.

“Ina kwana?”

Na gaishe shi ina murmushi sai ya amsa min fuskarsa ba yaboba fallasa.

“Ya kai?”

“Zan iya shigowa magana nake son yin da kai.....”

Daga can bayansa na jiyo muryar Suwaiba tana da fada.

“To wannan abun ya wuce gona da iri, ya zama iskanci da cin fuska, kuma Wallahi ba zan dauka ba ke bakya ma jin munya bibiyar kanen tsohon mijinki... Kai tirr Halima kin yi abun kunya.... ”

Da muryar da na san zata iya jiiyoni na ke fada masa cewar.

“Ka ce tai hakuri na san babu dadi, amman babu abunda zai yanke alaka a tsakaninmu...”

“Muje waje mu yi maganar”

Shine abunda ya fito bakinsa, bakin nasa nake ta kallo kamin nai backwards na fita daga falon, wanda hakan ya bashi damar fitowa ya janyo kofar ya rufe.

“Ya kai....”

Yan yatsuna na fara murzawa sai hawaye.

“Daman na zo ne na baka hakuri akan abunda ya faru..... ”

“Ai na ce miki ya wuce ko? Ni ban rike ki da komai ba tun wacan karon na ce na yafe miki”

“Ba shi ba, akan duka abubuwa da nai maka”

“Na yafe miki Halimatu....”

Na kalleshi cike da kaunarsa wacce ta mamaye qalbina take taraiya da numfashina a yanzu, kai na gyada masa alamar gamzu.

“Kuma ina son ma fada maka wani abu....”

Sai yai hanzarin katseni.

“Bana son jin komai a yanzu pls”

Na sake gyada kan a karo na biyu ina hade yawuna.

“Amman magana ce mai muhimmanci akan maganar fyaden..... ”

“Oh Please haba dai bana son jin komai a yanzu”

“Shikenan, zan jira har zuwa lokacin da kake son ji, zan tafi amman dan Allah ka rika daukar wayata idan na kiraka kuma ka rika min reply idan ka ga sakona pls dan Allah”

Be ce min uffan ba har na juyo na fara tafiya, sai jin mutum nai a gafena yana takawa tare da ni.

“Dan Allah Halimatu ki cire komai a ranki, ki nemi aiki ko wata sana'a zaki iya tallafawa kanki ki rage damuwa kin ji? Ki cire kowa a ranki”

Tsayawa nai na kalleshi.

“Babu kowa a raina a yanzu, na cire komai na fahimci komai, babu wanda yake cikin raina Abdallah sai kai....”

Kallon mamaki yake min is like kamar be yarda da ni ba, juyawa yai ya kalli bayansa kamin ya nuna kansa. Ni kuwa na gyada masa kai cike da kuzari, can ya busar da iskar bakinsa.

“Ya rabb, wato baki daina shayeshayen nan da na ce ki daina ba ko?”

Na matso kusa da shi ina girgiza masa kai.

“Ban sha komai ba Wallahi a hayyacina nake”

“No Halima ba zata fadi haka a hayyacinta ba, ko dai damuwar nan ta dawo miki ko kuma kin koma ma shaye shayen”

“Wallahi ban sha komai ba”

Na fada ina masa magiya kamar zan fasa kuka.

“Shikenan ki tafi gida”

“Zan tafi duk abunda ka ce zan yi Abdallah”

Kamar umarninsa nake jira sai na juya da sauri na fice daga gidan.

AHMAD POV.

Glass cup ne a hannunsa yana kurba lemun a hankali, while idanuwansa suna watching plasma but his heart is one where else. Yana jin tsananin damuwa da kadaici a rashin Baby Namra da Matarsa da kuma mahaifinsa a rayuwarsa, sai dai his try be strong for him mother and his sister Siyama, domin su kadai suka rage masa a yanzu, he feels like da ace mahaifinsa yana raye da abubuwan sun masa sauki, kamar yadda da ace Baby Namra tana nan wata kila da be shiga damuwa haka ba damuwar da ke taba lafiyarsa ta taba rayuwarsa, he missed his wife his father his daughter. Be dawo daga duniyar tunanin Gobensa ba har sai da Hajiya ta soma magana da shi ayayinda take zaune saman sofa Siyama na kasa tana matsa mata kafafuwanta.

“Dazun Laraba ta kirani tace wai dan Allah a taimaka mata a dauki danta aiki a kamfaninku...”

A hankali ya juyo ya kalleta.

“Ai ba irin su muke dauka ba, yan boko, kuma kin san Attahiru ba wani boko yai mai zurfi ba, idan ma yayi ba zai wuce secondary school ba”

“To a duba masa dai haka nan tunda har ta roka sai a samu inda aka laba shi”

“Hajiya ki dai fada mata masu ilmi muke dauka saboda kamfanin a yanzu yana bukatar gogaggun.....”

Be marasa ba ya fara tari da sauri ya aje lemun hannunsa ya ciro handkerchief dinsa ya tari jinin da ya fito daga bakinsa. The white handkerchief din ya bawa Hajiya da Siyama damar ganin jinin da kyau, daga Hajiya har Siyama sai ka rasa wanene hankalinsa ya fi tashi...

“Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un... Mi zan gani haka?...”

Cewar Hajiya. Sai yai murmushi yana nuna mata cewar ba komai ba ne.

“Habo na ke yi, daji ne ya kamani da mura ba wani abu ba”

“Brother yaushe ka fara haka?”

Siyama ta tambaya hawaye na sauko mata, kallonta yai he know he can't hide anything from her domin karatun likita take kuma ta fi kowa sanin waye dan'uwanta.

“Can we talk private?”

Hajiya tai saurin amsawa tana girgiza kai tana kuka.

“No I'm your mother be kamata ka boye min komai ba, how do you expect your own mother to live after you death? How? Ku kadai kuka rage min daga kai sai wannan”

Ta nuna Siyama hannunta na rawa tana fashewa da kuka. Da sauri tashi yai ya koma gabata.

“Wallahi Hajiya ina shan magani kuma i believe zan ji sauki, duka duka ban hi sati da fara wannan tarin jinin ba, kuma na ga different doctors sun bani magani ina kan sha”

Siyama ce ta taso ta zo bayansa ta rumgume shi ta fashe da kuka.

“Please Brother we love you..... ”

He feel so hopeless, so emotional but a haka yake kokarin ganin ya zama very strong for them.
7/21/21, 10:46 PM - Buhainat: *GOBE NA...*

By Khadeeja Candy

3️⃣9️⃣

Tun daga lokacin da Hajiya ta lura da halin da danta yake ciki bata sake yarda ta barshi ya zauna shi kadai ba indai yana gidan to yana falo tare da ita ko kuma yana harabar gidan suna fira, a ganinta sakewarsa zai taimaka masa fiye da kadaicewar da zai yi shi kadai yana tunani da saka kansa a damuwa.
  Kamar yadda ta saba masa after dinner suna zaune dinning ta dauko masa zancen aure domin shi ne abunda ta fi son taga yayi a yanzu ko zai rage masa damuwa har ma ya kawo masa farincikin samun wata haihuwar.

“Tun kwanan baya na maka magana akan aure kace zaka yi tunani ba ka ce min komai ba”

Ya kurba ruwan da ke gabansa kadan yana dan murmushi.

“Hajiya bana son zancen aure a yanzu”

“Saboda me? If saboda ni ne zaka iya zama a wajen gidan nan da matarka, and ba zan cilasta maka auren Ikilima ba, sai ka dauko budurwa da kake so ka aura”

“No ba wai Budurwa ko bazarawa ba, a halin yanzu mace bata gabana, ni ban ki na mutu a haka ba”

“Saboda me? Ni bana son ganin jikanka ne? Ku kadai Allah ya bani ai zan so ku yi aure ku yi juri'a da yawa ba kamar ni ba”

“Kawai ina ganin kamar idan na sake haihuwa rasata zan yi, ni kuma bana son abunda zai sake kasani a damuwa yanzu”

Hajiya ta yi murmushi.

“Baka da karfi zuciya sai kace ba namiji ba”

“Hajiya ba zaki san abunda nake ji ba, babu wanda zai shiga a irin halin da nake ciki a yanzu ace be samu kansa a damuwa ba”

“Yes dole na ka damu an sani ai, amman ka rika sassautawa rayuwarka, ita daman rayuwa tana tafe da kalubale kala kala, wani mai sauki wani mai wahala, sai dai duk halin da zaka shiha ka rika tunawa akwai wadanda suka fika shigarsa, idan arziki ne akwai wadanda suka fika, idan talauci ne da damuwa akwai wadanda suka wankeka suka shanye, kai mata kawai ka rasa sai ya kuma uba, akwai wata macen da na gani na ita tana da uwar a raye uba a raye dukan ya'yanta suna nan, amman kalubalen rayuwar da ta shiga ko kan akaifarta baka shiga ba, tun daga lokacin da na ji labarin matar nan abun ya tsaya min a rai”
Chapter 74 · 0% Book details