← Book details Gobe Na Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 100 OF 136

Sashe 100

Gobe Na Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Ba musu na karba na saka mata, sai da na mika mata wayar sannan ya ce.

“And ta girme ki ko ba komai she deserve some respect”

“Yeah Yeah Anty Halima....”

“Lim's”

Ya furta sannan ya juya muka cigaba da tafiya. Siyama har ta juya ta juyo tana kallonmu.

“Wowwwwwwww”

Juyowa nai na kalleta sai yace min.

“Share ta kanwar nan tawa da kike gani bata da hankali”

Murmushi kawai nai muka fice daga cikin gidan, mike titi mukai izuwa babban titi inda ababen hawa suka fi yawa.

“Akwai maganar da kike son min ne?”

Na kalleshi ban ce komai ba.

“Na lura da yanayinki, kin san yanzu na karance ki ina iya gane yanayin damuwarki ko far'a ko makamancin haka just say it”

Na yi murmushi ina saka duka hannayena na rike ledar da nake kyautata zaton turareka ne a ciki saboda irin kamshin da suke, sai na ji duk wata kimarsa da mutunsa sun kara karuwa a idona.

“Akan maganar Abraham ne?”

“Abraham dai? Why kike son magana akansa? Bakinsan bana son jin sunansa ba? Idan na tuna ya miki fyade sai na ji kamar na kashe shi na datsa namansa na soya shi sannan na watsa shi a cikin wuta ta kona shi”

Tsayawa nai ina kallonsa hasken dake unguwar yana haska min fuskarsa.

“It pain me”

Ya maimaita yana yamutsa fuska. Kasa nai da kaina.

“Saboda karka saka kanka a hatsari ne, and dazun ya zo min da wata magana ne wacce ta sanyaya min jiki, and ba zan jidadi ba idan wani abun ya same ka sanadina, yawancin mutanen da suka kusantata kaddarata ta kan shafe su”

Ban boye komai daga abunda ya faru tsakanina da Abraham ba na fada masa, sai kawai na ga yana dariya yana kallona dariya sosai fa kamar yana kallon wata yar wasan Comedy.

“Pls how old are you? Har yanzu akwai kurciya a tare da ke. And dan kawai an fada miki magana sai ki yarda? Kina saurin yarda gaskiya, and who told you idan Abraham ya aure ba ki haihu ba zai zauna da ke? How sure are you zai bayyana kansa ya daina duk abunda yake saboda ke?”

“Ba wai ina nufin na aure shi ba...?”

“Then me kike nufi? Pls karki sake min maganarsa ki bar masu bincike su bincika abunda suke so akansa, so that ki samu salama ni ma kuma hankalina na kwanta”

Na gyada masa kai. Sannan muka cigaba da tafiyar ya zuba hannayensa aljihu, da kansa ya tara min napep na shiga ya fada masa inda zai kai ni, sannan ya ciro kudin da nake kyautata zaton sun kai 3k ya bawa mai napep din.

“Na tabbatar ta shiga gida sannan ka dawo”

“To ranka ya dade na gode sosai”

Ya amsa cike da far'a sannan yaja Napep din muka nufo gida.

AHMAD POV.

tsaye yai a gurin har sai da ya daina hango napep dinsu sannan ya juyo ya dawo gida, duk abunda yai a gaban mahaifiyar Aminu yayi ne just to make her feel special, wani irin tausayi take ba shi ko kallonta yai sai yaji kamar zai zubar mata da hawaye.
  Part dinsa ya nufa a ranar kwana yai da tunani kala kala, sai sake sake yake a ransa. Misalin tara da wani abu ya shiga part din mahaifiyarsa, sai ya same ta a kitchen kamar kullum mai aikinsu kuma na jera abinci a dinning.

“Ina kwana Hajiya”

“An tashi lafiya?”

Ta amsa tana murmushi jinginawa yai jikin kofar kitchen din yana murmushi.

“Al-hamdulillah, Hajiya ba zaki daina wahalar da kanki akan girkin nan ba”

“Na san baka son abincin mai aiki shiyasa nake girka maka da kaina, amman idan kai aure zan huta”

Murmushi yai ya kai hannunsa a kirjinsa yana shafa farar shaddar dake jikinsa.

“Soon In-Sha-Allah”

Da sauri Hajiya ta juyo ta kalleshi.

“Da gaske?”

Ya gyada mata kai.

“Khadija dai?”

Sai ya bar jikin kofar ya nufo inda take yana murmushi.

“Wata ce dai wacce ta cancanci rayuwa mai kyau, wacce ta yanke kauna daga samun jindadi, wacce take bukatar tallafi ita da yayanta da yan'uwanta, wacce zuciyata ta cika da tausayinta”

“Halima ce?”

Hajiya ta tambaya tana murmushin jindadi. Sai ya rumgume ta ta baya ya dora kansa saman wuyanta.

“Hakan nan kawai nake jin kamar idan ba ni na aureta ba, zata iya auren wani ya ci amanarta kuma ta sha wahala, and idan ta auri wani ba ni ba, zai so yayanta? Zai iya taimakonta? Zai jin tausayinta kamar ni? Kin san me take fada min jiya? Wai tana tsoron kar kaddararta ta shafe ni, tsoro rabar mutane take, ina son na cire mata wannan tsoron i want to make her feel special, and duk wani kalami da mahaifiyar mutumen tai jiya da ni take, a tunaninta ina son Halima ne, Idan har ta amince min na aureta, zan aureta ne kawai saboda in tausayinta amman ba dan ina sonta ba”

Ya sake ta ya juyo gabanta ya tsaya.

“And ina son mace mai hakuri kamar ta, the way she talk, yadda take gudanar da rayuwarta da yadda take taka tsantsan everything is perfect i like her, and her name, ke ma kuma naga kamar ta ku zata zo daya”

“Duk macce da ta auri dana ta yi babban dace, and i believe matar na deserve a better life, ban kawo maka zancen ta bane saboda na san baka son bazawara, sai dai na lura jininku ya hadu hankalinku da tunaninku yana kokarin zama daya, zan fi kowa farinciki idan hakan ya tabbata saboda tana burgeni, daga ganinta kasan macece mai hakuri mai tarbiya mai hankali mai natsuwa da yadda da ko wace irin kaddara, irin matar nan duk namijin da ya aureta yayi sa'ar aure, abunda kake kudiri idan alheri a tsakaninku ina rokon Allah ya tabbatar”

“Amin Hajiya”

Ya amsa yana murmushi, har ga Allah shi dai kam ba son Halima yake ba, domin tuna tayi aure har biyu ga fyade yana bata masa rai, dukan wani abu da zai mata na tausayi ne kawai da kuma gudun halin da zata fada nan gaba, and the way ta Hajiya take son yai aure zai sake cika mata burinta na auren, sai dai yana jin inda har zai yi auren so Halima ce macen da tafi cancanta ya aura, ko ba komai ita kadai zata iya hakurin zaman da Hajiya, kuma a yadda ya lura da Hajiya tana son ta tan tausayinta ba zata cutar da ita kamar sauran matan ba.

AMINU POV.

Ko da suka isa har an fito da shi, sun zuba shi nan jikin wani siminti fuskarsa duk ta kumbura jikinsa ma kana gani kasan ya sha duka, da ido daya yake iya dagawa ya kalli mutane, jin muryar Hajiyarsa yasa shi jin sanyi, dacan kam ya dauka ko kashe shi za su yi. Hajiya da kuka da komai suka dauke shi suka saka shi a motarsa da direban Ahmad ya biyo su da ita, daga barak din suka wuce da shi asibiti, sai da suka kusa isa asibitin sannan Hajiya ta fara Allah ya isa dan can kan kasa daga ido tai ma ta kalli tarin sojijin, domin ba a bar su sun shiga ba sai da Direban ya kira Faruk din ya sanar masa sannan Faruk din ya bada umarnin a zo a tafi da da su ciki.

“Wannan ai zalunci ne, to shi Bazawarin nata soja ne daman”

Kanen mahaifinsa wanda shima sai a yanzu ya samu baki ya fada, babu dai wanda ya amsa shi duk jimamin abun kawai suke. Bama kamar Hajiya da take jin kamar ita aka daka.

“Wallahi duk inda zan shiga sai na shiga sai na ga inda za ayi auren nan, bakar azzalumar mata, da shegen bazawarin nata daman can ba son shi take da alheri ba, wannan bakin zalincin wallahi Allah ya saka muna”

Riri Hajiya take kuka tana jin kamar ace sun fi Ahmad arziki da iko da sai ta saka an wulakanta shi fiye da yadda yai ma danta amman ba dama, tun da sun fisu arziki da komai ma ciki har da sanin darajar dan'adam.
7/21/21, 10:48 PM - Buhainat: *GOBE NA...*

By Khadeeja Candy

5️⃣0️⃣

TWO MONTHS LATER.....

Alhamdulillah Thumma Al-hamdulillah.
  Godiya ce abunda ta cancanci fita daga bakina na yanzu, izuwa ga mahallincina ko da kuwa ina cikin tsananin rayuwa ballantana yanzu da rayuwar ta fara sauya min.
Abubuwa da yawa da ban zata ba daga Ahmad suna ta samu na, ni da shi a yanzu kusan mun zama abokai, yana sake min sosai yana fada min abubuwan da za su kwantar min da hankali, yana dora ni a kowace hanya ta jagoranci.
Ban tana sani haka yake da sakewa da son jama'a ba sai yanzu, a cikin abubuwan da yai minba kamar yadda ya dukufa a nemawa Kabir Lafiya, wanda farinciki ba ni kadai ya saka ba har da yan'uwansa domin na ga hakan a fuskarsu, asibiti aka maida shi suka masa duk wani gwaje gwaje daya kamata, sannan suka dora shi akan magani, duk wani abu da za a kashe masa ko aka kashe masa ta aljihun Ahmad yake fita.
   da abun ya ki yi a nan ne suka tura asibitin sokoto wato uduth, tare da yan'uwansa biyu aka je, da kuma matarsa.
  Bayan nemawa Kabir lafiya kuma yarana ya saka su a makarantarsa, school bus ke kaisu tana daukosu.
  Wani lokacin ina da na kalleshi sai na ji kamar na bude masa zuciyata yaga irin farincikin daya saka ni, idan kuma na tuna abubuwan da suka faru tsakaninmu sai nai dariya, farkon haduwarmu da kuma abubuwan da yai min na cin fuska kamin yanzu, da kuma yadda muke a yanzu sai wani abun ya bani dariya wani kuma ya bani mamaki.
Chapter 100 · 0% Book details