Sashe 123
Gobe Na Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
For the first time a yau zan tunkari Abdallah da maganganu a cikin gidan Hajiya babu tsoro ko fargaba a tare da ni, sai dai ga dukan alamu shi din ya kasa natsuwa sai kiran wayata yake ni kuma na ki na dauka domin face to face nake son ganinsa ba ta waya ba, kamin mai napep din ya isa har na matsu, yana saukeni na biyashi kudinshi na buga gate din sai na ji shi a bude, hakan yasa na tura kofar na shiga babu kowa a harabar gidan sai motoci ina ganin motarsa na tabbatar da lallai yana gida kamar yadda ya fada min. Kai tsaye na nufi kofar falon nai knocked sai na ja na tsaya, after some seconds ma sake kwankwasawa. A hankali aka bude kofar Abdallah ne ya fito daga cikin falon ya janyo kofar ya rufe yana kallona da mamaki a fuskarsa.
“Halima lafiya?”
Ya tambaya a hankali kamar mai rarrashin yarinya. A yau da na kalleshi sai na ganshi kamar ba Abdallah ba, duk wata kima da matarta da mutunci da nake ganinsa da ita a yau sai na nemeta na rasa.
“Ina mamakin yadda zaka fada min abunda ba shine a ranka ba, ina mamakin yadda ka tozarta yardar da nai da kai ka watsar da amincin da nai maka”
Karara mamaki da al'ajab suka bayyana a fuskarsa.
“Halima are you okay?”
“No I'm not, me yasa zaka fada min abunda ba shine a ranka ba, akan me zaka ce kana son farincikina bayan ba haka ba ne a ranka?”
Matsowa yai kusa da ni ganin yadda nake daga murya, idanuwana kuma na nuna tsantsar bakin raina.
“Wace irin magana ce wannan? Me yake damunki?”
Ya fada murya kasakasa.
“Kaine damuwata Abdallah, kai ne matsalata”
“What happen?”
“Ka rantse min baka san abunda yake faruwa ba....!”
Murmushi yai ya lumshe ido ya bude.
“Wai wannan banza... Ai...”
“Shi ba banza ba ne mijina ne na sunna!”
Na fada cikin wani irin zafin rai da ban taba sanin ina da shi ba. Sai ya sake yin murmushi.
“Na sani ne ai, har na taya shi murna remember?”
“Yes a ranar ka cije shi a hannu”
“Maye ni ne ko aljani da zan masa wani abun?”
“No amman kai kana da kofi, kai ka yi wa Abdulhamid ya kasa aure, ka taba min ba sau daya ba ba sau biyu ba, Abdallah na sani zaka iya kullatar Ahmad a rai”
“Yes...”
Ya amsa min kai tsaye yana hade fuska kamar ba shi ba.
“Ya fada min zai nuna min matsayinsa a gurinki, kuma ya fada ya cika na sani yayi forcing din ki ya aure ki, he deceive you ba ki san waye shi ba, how could he? Ya aure ki by force and ya holding hannunki a gabana bayan ya san na fi kowa son ki? How dare he?”
“No how dare you....! Ahmad be aure ni ba sai da amincewa ta, abunda kai masa ya nuna baka son farincikina, domin yan'uwansa da danginsa ni zarsu zarga idan hakan ta faru ya kake tunanin zan kasance?”
“Amman Halima ba son shi kike ba, ta ya za ki auri mutumen da ya laka miki laifin kisan kai? Ko kin manta ne? Mutumen daya tashi sakawa a rufe ki gidan yari? Babu kalar maganar da be fada miki ba, Ina son ki Halima kin sani ina da kudurora akanki, i just want you to get a better life, kuma idan mu kai jira na wani lokaci wata kila Allah zai cika mana burinmu”
“Jiran shekara dubu nawa? Jiran ranar da Hajiya za ta so ni har ta amince na aure ka? Ko jiran ranar da Abdulhamid da bakinsa zai roki na aure ka? Ko jiran ranar da mutane za su ga dacewar haka su ba mu shawara aikatawa? Ba so na kake ba Abdallah kana son ka ne, a lokacin da na ke auren Aminu ka sani mijine uban yayana amman kullum sai ka fada min aibinsa, kullum sai ka fada min abunda zai bata min rai saboda na rabu da shi na aure ka, ka sani neman auren matar aure haramun ne Annabi ya hana amman ka nace kana ta min campaign kanka, babu abunda baka min dan na kashe aurena na aureka, wannan dalili ya hana ni auren shiyasa na zabi na aure dan'uwanka domin shi be taba min haka ba, duk kuwa da kasancewar shi ya fara so na kamin kowa, yana sane nai aure amman be taba ce min Halima ki kashe aurenki ki aure ni, Abdulhamid ya fika zuciya mai kyau, domin shi be taba cutar da ni ba, kawai ya kasa aminta da ni ne a lokacin da kaddara ta fada min, and now na sake auren wani ba kai ba, so kake na kashe auren na fito aure ka? Saboda ka cika son kanka kuma ka kasa yarda da kaddara, miye laifin Ahmad idan na aure shi kuma zan samu farinciki a gidansa? Ashe ba farinciki kake min fatar samu ba?”
Na karasa a tsawace hawaye na sauko min.
“Halima kamar ba ke ba”
“Ni ce dai, na zo na gargade ka ne, idan wani abu ya samu mijina...! Ba zan taba yafe maka ba, kuma hakan ba zai saka ya sake ni ba ba zan taba rabuwa da shi ba har a abada...! Domin ni na yarda da abunda ka kasa yarda da shi KADDDARA”
Na kare ina nuna shi da yatsa, sai ya girgiza min kai ya kara matsowa kusa da ni
“Haba Halima kina da raunin tunani, ta yadda idan wani ya kisa miki wata maganar sai ki hau ki zauna akanta, ki rika kokarin samawa wasu farinciki ba kanki ba, yanzu duniya ta wuce wannan kowa kansa ya sani, kamar kin manta waye Ahmad? Miya zai kitsa miki abubuwa a kaina kuma yardar da mutumen da kika gani a jiya sama da ni?”
“So kake GOBE NA ta lalace, so kake mutane su fara guduna suna ganina kamar wata annoba? So kullum nai ta dauwama a bakinciki da damuwa? Na gaji i deserve happiness”
“Shi nake kokarin ba ki, i promise you za ki samu farinciki a tare da ni, dukannin mafarkina da burina akanki ne, Halima ina miki son da wani da'namiji be taba miki shi ba....”
Yana karasa Hajiya ta bude kofar falon ta fito, a yanayin yadda na ganta da kuma yadda fuskarta ya nuna ta ji komai. A gabansa ta tsaya yana kallonsa shi ma kallonta yai sai yai kasa da idonsa.
“Da gaske kai ne silar ciwon Hassan?”
Ta masa tambayar tana masa wani irin mugun kallo, sai yai shiru ya kasa amsawa kuma ya kasa daga ido ya kalleta.
“Ka amsa min? Eh ko a a?”
Ta daka matsa tsawa jikinta har bari yake.
“Eh....”
Tasss ta wanke masa fuska da mari kamar daman jiran take ya amsa mata da eh din, hakan kuma be wadatar da ita ba har sai da ta sake marin dayan baren fuskar.
“Amman baka da tausayi baka da imani Husaini.... Allah ya wadaranka....”
Cikin kuka take mishi wannan maganar, shi kuma har lokacin be motsa daga inda yake ba. Sai kuma ta juyo ta kalleni tana hawaye.
“Fita ki bar min gida, ba ke ba yaya har abada, ko bana raye ka auri Halima ban yafe maka ba.....!”
Ta karasa tana nuna shi da yatsa, a rikice Abdallah ya kalleta ya kalleni sai ya fadi kasa ya rike kafafuwanta ya fashe da kuka kamar ba shi ba.
“Noooooooo Hajiya dan Allah..... Hajiya dan Allah, Hajiya dan Allah.... Hajiya dan Allah.... Hajiya dan Allah...”
Ya maimaita hakan ya fi a kirga yana rike da kafafuwanta yana kallona kuka yake sosai kamar ba namiji ba, sai kuma ya mike tsaye ya rike hannayenta.
“Hajiya ina son Halima Wallahi baki san kudurina ba dan Allah karki shiga tsakaninmu haka....”
A take ta fisge hannunta ta sake wanka masa kyakkyawan mari. A lokacin ne yai shiru ya runtse ido.
“Ka gani ko? Dan Allah ka kyale min mijina.... Ina son abuna”
Na fada ina hade hannayena nima hawaye nake kamar shi, sai ya bude ido ya kalleni kamin ya juya yana kallon mutanen da suka fito daga falon suna tambayar ba'asi, Hajiyar kuma ya koma cikin falon tana kuka. Ni kuma na juyo kamar kazar da kwai ya fashewa na fara tafiya ina jin wani abu marar dadi. Sai da na kai gate din sannan na juyo na kalleshi har lokacin yana tsaye a inda yake yana kallona, juyawa nai na bude gate din na fita. Sai da nai tafiya mai nisa sannan na samu napep na shiga ta mayardar da ni asibitin ko da na isa ana kiran sallah magariba, kai tsaye na nufi ward din da Ahmad yake ina isa na tura kofar dakin na shiga, sai na samu Mama da Inna zaune a dakin ga Hajiyarsa da Kanwarsa Siyama da wata wasu mata hudu da ban wayance su ba, sai dai ina kyautata zaton yan'uwan Ahmad din ne, shi kuma yana zaune saman gadon wani kallo kawai yake aiko min wanda ke nuna ba lafiya ba. A sanyaye na shiga muka gaisa da mahaifiyarsa sai ta gabatar da ni a gurin matan, sannan tace min.
“Kin gwangwanin Gwarzo nan”
Hakan yasa na sake mika musu gaisuwa sannan na tsaya a kusa da Inna sai dai a duk lokacin da na kalli Ahmad sai ya dan harare ni kasa kasa, sannan ya sauko saman gadon ya shiga bandaki yai alwala ya fito, Hajiyarsa ta umarce ni da na shimfida masa carpet su kuma suka tashi suka fita tare da bakin. Inna da Mama suka mike tsaye Inna na ce min.
“To mu kan mun tafi Halimatu sai kin dawo Allah ya kara sauki”
“Amin inna sai na zo”
Sai da suka juya sannan ya kawo kunnensa kusa da nawa ya rada min.
“Ki ce musu nan za ki kwana”
“Halima lafiya?”
Ya tambaya a hankali kamar mai rarrashin yarinya. A yau da na kalleshi sai na ganshi kamar ba Abdallah ba, duk wata kima da matarta da mutunci da nake ganinsa da ita a yau sai na nemeta na rasa.
“Ina mamakin yadda zaka fada min abunda ba shine a ranka ba, ina mamakin yadda ka tozarta yardar da nai da kai ka watsar da amincin da nai maka”
Karara mamaki da al'ajab suka bayyana a fuskarsa.
“Halima are you okay?”
“No I'm not, me yasa zaka fada min abunda ba shine a ranka ba, akan me zaka ce kana son farincikina bayan ba haka ba ne a ranka?”
Matsowa yai kusa da ni ganin yadda nake daga murya, idanuwana kuma na nuna tsantsar bakin raina.
“Wace irin magana ce wannan? Me yake damunki?”
Ya fada murya kasakasa.
“Kaine damuwata Abdallah, kai ne matsalata”
“What happen?”
“Ka rantse min baka san abunda yake faruwa ba....!”
Murmushi yai ya lumshe ido ya bude.
“Wai wannan banza... Ai...”
“Shi ba banza ba ne mijina ne na sunna!”
Na fada cikin wani irin zafin rai da ban taba sanin ina da shi ba. Sai ya sake yin murmushi.
“Na sani ne ai, har na taya shi murna remember?”
“Yes a ranar ka cije shi a hannu”
“Maye ni ne ko aljani da zan masa wani abun?”
“No amman kai kana da kofi, kai ka yi wa Abdulhamid ya kasa aure, ka taba min ba sau daya ba ba sau biyu ba, Abdallah na sani zaka iya kullatar Ahmad a rai”
“Yes...”
Ya amsa min kai tsaye yana hade fuska kamar ba shi ba.
“Ya fada min zai nuna min matsayinsa a gurinki, kuma ya fada ya cika na sani yayi forcing din ki ya aure ki, he deceive you ba ki san waye shi ba, how could he? Ya aure ki by force and ya holding hannunki a gabana bayan ya san na fi kowa son ki? How dare he?”
“No how dare you....! Ahmad be aure ni ba sai da amincewa ta, abunda kai masa ya nuna baka son farincikina, domin yan'uwansa da danginsa ni zarsu zarga idan hakan ta faru ya kake tunanin zan kasance?”
“Amman Halima ba son shi kike ba, ta ya za ki auri mutumen da ya laka miki laifin kisan kai? Ko kin manta ne? Mutumen daya tashi sakawa a rufe ki gidan yari? Babu kalar maganar da be fada miki ba, Ina son ki Halima kin sani ina da kudurora akanki, i just want you to get a better life, kuma idan mu kai jira na wani lokaci wata kila Allah zai cika mana burinmu”
“Jiran shekara dubu nawa? Jiran ranar da Hajiya za ta so ni har ta amince na aure ka? Ko jiran ranar da Abdulhamid da bakinsa zai roki na aure ka? Ko jiran ranar da mutane za su ga dacewar haka su ba mu shawara aikatawa? Ba so na kake ba Abdallah kana son ka ne, a lokacin da na ke auren Aminu ka sani mijine uban yayana amman kullum sai ka fada min aibinsa, kullum sai ka fada min abunda zai bata min rai saboda na rabu da shi na aure ka, ka sani neman auren matar aure haramun ne Annabi ya hana amman ka nace kana ta min campaign kanka, babu abunda baka min dan na kashe aurena na aureka, wannan dalili ya hana ni auren shiyasa na zabi na aure dan'uwanka domin shi be taba min haka ba, duk kuwa da kasancewar shi ya fara so na kamin kowa, yana sane nai aure amman be taba ce min Halima ki kashe aurenki ki aure ni, Abdulhamid ya fika zuciya mai kyau, domin shi be taba cutar da ni ba, kawai ya kasa aminta da ni ne a lokacin da kaddara ta fada min, and now na sake auren wani ba kai ba, so kake na kashe auren na fito aure ka? Saboda ka cika son kanka kuma ka kasa yarda da kaddara, miye laifin Ahmad idan na aure shi kuma zan samu farinciki a gidansa? Ashe ba farinciki kake min fatar samu ba?”
Na karasa a tsawace hawaye na sauko min.
“Halima kamar ba ke ba”
“Ni ce dai, na zo na gargade ka ne, idan wani abu ya samu mijina...! Ba zan taba yafe maka ba, kuma hakan ba zai saka ya sake ni ba ba zan taba rabuwa da shi ba har a abada...! Domin ni na yarda da abunda ka kasa yarda da shi KADDDARA”
Na kare ina nuna shi da yatsa, sai ya girgiza min kai ya kara matsowa kusa da ni
“Haba Halima kina da raunin tunani, ta yadda idan wani ya kisa miki wata maganar sai ki hau ki zauna akanta, ki rika kokarin samawa wasu farinciki ba kanki ba, yanzu duniya ta wuce wannan kowa kansa ya sani, kamar kin manta waye Ahmad? Miya zai kitsa miki abubuwa a kaina kuma yardar da mutumen da kika gani a jiya sama da ni?”
“So kake GOBE NA ta lalace, so kake mutane su fara guduna suna ganina kamar wata annoba? So kullum nai ta dauwama a bakinciki da damuwa? Na gaji i deserve happiness”
“Shi nake kokarin ba ki, i promise you za ki samu farinciki a tare da ni, dukannin mafarkina da burina akanki ne, Halima ina miki son da wani da'namiji be taba miki shi ba....”
Yana karasa Hajiya ta bude kofar falon ta fito, a yanayin yadda na ganta da kuma yadda fuskarta ya nuna ta ji komai. A gabansa ta tsaya yana kallonsa shi ma kallonta yai sai yai kasa da idonsa.
“Da gaske kai ne silar ciwon Hassan?”
Ta masa tambayar tana masa wani irin mugun kallo, sai yai shiru ya kasa amsawa kuma ya kasa daga ido ya kalleta.
“Ka amsa min? Eh ko a a?”
Ta daka matsa tsawa jikinta har bari yake.
“Eh....”
Tasss ta wanke masa fuska da mari kamar daman jiran take ya amsa mata da eh din, hakan kuma be wadatar da ita ba har sai da ta sake marin dayan baren fuskar.
“Amman baka da tausayi baka da imani Husaini.... Allah ya wadaranka....”
Cikin kuka take mishi wannan maganar, shi kuma har lokacin be motsa daga inda yake ba. Sai kuma ta juyo ta kalleni tana hawaye.
“Fita ki bar min gida, ba ke ba yaya har abada, ko bana raye ka auri Halima ban yafe maka ba.....!”
Ta karasa tana nuna shi da yatsa, a rikice Abdallah ya kalleta ya kalleni sai ya fadi kasa ya rike kafafuwanta ya fashe da kuka kamar ba shi ba.
“Noooooooo Hajiya dan Allah..... Hajiya dan Allah, Hajiya dan Allah.... Hajiya dan Allah.... Hajiya dan Allah...”
Ya maimaita hakan ya fi a kirga yana rike da kafafuwanta yana kallona kuka yake sosai kamar ba namiji ba, sai kuma ya mike tsaye ya rike hannayenta.
“Hajiya ina son Halima Wallahi baki san kudurina ba dan Allah karki shiga tsakaninmu haka....”
A take ta fisge hannunta ta sake wanka masa kyakkyawan mari. A lokacin ne yai shiru ya runtse ido.
“Ka gani ko? Dan Allah ka kyale min mijina.... Ina son abuna”
Na fada ina hade hannayena nima hawaye nake kamar shi, sai ya bude ido ya kalleni kamin ya juya yana kallon mutanen da suka fito daga falon suna tambayar ba'asi, Hajiyar kuma ya koma cikin falon tana kuka. Ni kuma na juyo kamar kazar da kwai ya fashewa na fara tafiya ina jin wani abu marar dadi. Sai da na kai gate din sannan na juyo na kalleshi har lokacin yana tsaye a inda yake yana kallona, juyawa nai na bude gate din na fita. Sai da nai tafiya mai nisa sannan na samu napep na shiga ta mayardar da ni asibitin ko da na isa ana kiran sallah magariba, kai tsaye na nufi ward din da Ahmad yake ina isa na tura kofar dakin na shiga, sai na samu Mama da Inna zaune a dakin ga Hajiyarsa da Kanwarsa Siyama da wata wasu mata hudu da ban wayance su ba, sai dai ina kyautata zaton yan'uwan Ahmad din ne, shi kuma yana zaune saman gadon wani kallo kawai yake aiko min wanda ke nuna ba lafiya ba. A sanyaye na shiga muka gaisa da mahaifiyarsa sai ta gabatar da ni a gurin matan, sannan tace min.
“Kin gwangwanin Gwarzo nan”
Hakan yasa na sake mika musu gaisuwa sannan na tsaya a kusa da Inna sai dai a duk lokacin da na kalli Ahmad sai ya dan harare ni kasa kasa, sannan ya sauko saman gadon ya shiga bandaki yai alwala ya fito, Hajiyarsa ta umarce ni da na shimfida masa carpet su kuma suka tashi suka fita tare da bakin. Inna da Mama suka mike tsaye Inna na ce min.
“To mu kan mun tafi Halimatu sai kin dawo Allah ya kara sauki”
“Amin inna sai na zo”
Sai da suka juya sannan ya kawo kunnensa kusa da nawa ya rada min.
“Ki ce musu nan za ki kwana”