Sashe 126
Gobe Na Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
“Haka fa yake idan ya samu lafiya ba ma zaman lafiya ni da shi...”
Nikam kasa cewa komai nai sai dariya nake.
“Lims gulma ta take ko?”
“A a”
Ina amsa masa ya fito daga bandakin fuskarsa na ta haske irin ta sabon ango. A take ta dauki jakarta ta mike tsaye tana fadin.
“Ni dai na tafi Allah ya bada sauki”
Na amsa da amin ina binta da kallo shi kuma ya kabbatar sallah, hakan na bani damar tashi na shiga bandakin nai alwala na fito na jirashi har ya gama sannan na gabatar da tawa. Da kansa ya zuba mana abincin a plate daya spoon ma daya ya saka ya dora abincin gafena nikan sai kallonsa nake domin na lura tun jiya yana kokarin aikin da hannun.
“Hannun ba ya maka nauyi sosai ne?”
“Ba sosai yake min ba ina sai jin kamar jijiya ta rike ne”
Ya debo abincin da kansa ya kai mu a baki sannan shi ma ya ci. Shi yai feeding dina har na koshi sannan na karbi plate din na aje, sai kuma yaja ni jikinsa ya rumgume.
“Mata da miji idan suna zaune ba a zama nesa da juna ki koyi wannan yana kara soyayyar da shakuwa ko wani gurin muka je za mu rika tunani da kewar junanmu”
Yana gama fadar hakan ya saka hannunsa cikin hijabina yana kokarin kaiwa kirjina.
“Ba bari muji da akai wanka sun wanku”
Ya fada cikin rada sai nai saurin raba jikina da nashi.
“Baka da lafiya amman sai rashin ji kake....”
“Ahen ahen ahen please nahhhh”
Yayi maganar ta sigar shagwaba kamar wani dan 3 years sai marairaice min yake yana tabe baki irin yadda yara suke idan suna son abu. Nikam abun dariya ma ya bani wannan kuma ai ya zama ba jinya ba, duk yadda nai kokarin nisa da shi sai ya ce min ba haka ba. Sai da mutane suka fara shigowa sannan ya shafa min lafiya.
A yau kam na ga yan'uwan Ahmad sosai a asibitin wata kila saboda gobe zai bar kasar ne yasa suke ta zuwa kamar ana turowa idan wannan ya fita wata ko wani ne zai shigo, duk basa shigowa hannu sake masu kawo abinci ko siyayya wasu kuma idan za su fita sai su ba ni kudi, mun gaisa da wasu da yawa daga cikinsu ya gabatar da mu kuma ya gabatar ni a gurinsa kowa sa cewa yake sun ji abu daga sama wai ba sanarwa.
“Amaryar ce sai da haka shiyasa, sai da dabara”
“Ato ko dai kwace kai wa wani ne?”
Cewar wata tabashiyarsa tana dariya.
“To wannan tsaleliyar matar zan samu a banza, ai kinsan sai na yi da gaske, duk masu neman wasa suka tsaya ni kuma nai muku na shirwa”
Duk suka saka dariya har ni. Bayan sallah magariba na fara shirye shirye zuwa gida sai ya fara kallona kamar mai mamaki, nikam yau na rantse gida zan kwana ko da karbar sakon da Hajara tace min zata kawo idan an gama sallah isha'i.
“Ba dai gida za ki je ba ko”
“Gida mana, tun da gobe za mu tafi ai kara na ce gida tun yanzu sai na kwana can nai musu sallama”
“A a ni ba zan iya kwana babu ke ba”
“Can da da kake kwanan fa?”
“Can da ai ban rabi jikinki ba, yanzu kuma na saba kwana biyu nan ba zan iya ba gaskiya, haramun ne ma”
Ya fada yana riko hannuna.
“A a Mama tace na dawo gida na kwana so that nai sallama da su Namra”
Marairaice min yai.
“Tsoro nake ji, kuma ciwon zai iya tashi idan baki nan”
Yanayin yadda yai maganar yasa ban san lokacin da dariya ta subuce min ba. Shi kanshi dariya yai ya rumgume.
“i love you Babe, gaskiya ba zan jidadi ba idan baki kwana a nan ba, amman babu yadda na iya, dole nai hakuri”
“Yauwa na debi kala biyar na tafiya yayi? Kar na deba da yawa ya sama kauna”
Na fada daman ina son nai masa tambayar tun jiya.
“Ki kara”
“Za mu dade ne?”
“Ba sani ba tukuna, wata kila za mu dade wata kila ba za mu dade ba ya dangata daga yadda suka ba mu, amman kin san ko na ji sauki sai dai Hajiya ta dawo ta bar ku can ko?”
“Saboda me? Ba kai aka kai ba?”
“Kin san idan mutum ya dade yana jin kishin ruwa idan ya samu ruwan ba ya musu shan hankali”
Kallonsa nai da kyau ina mamakinsa a dacan idan aka ce min Ahmad zai yi haka wallahi zan karyata.
“Anya dai kai ne?”
“Ni ne fa, ai dan iskan cikin gida ne ni, Allah dai ya bani lafiya”
“Lafiya ai ta samu marar lafiya ba zai yi abunda kake ba”
“Ina ma kika sani hmmmm Allah dai ya kai damo ga harawa, ya nuna mana mu dan yi nisa da Hajiya akwai kara'i”
Ya karasa yana kwafa yana kokarin kyalkyalata, dariya nai sai yai kissing kumatuna yana shafa bayana, sai kuma ya dago fuskata ya soma tsosar bakina try to remove my Hijab, sai da nai da gaske sannan na raba jikina da shi.
“Komai abunki dai dole ki jira driver ya zo or else ki kwana nan dan ba zan bari ki hau Napep ba ana kalle min kaya”
A nan ma dariya nai ina ta jin kunyarsa sai dai na lura sam ya sauya kamar ba shi ba kunyar ma bata gabansa, hannunsa kuma baya zama kurum matukar muna zaune dakin daga ni sai shi. A dole nai jiran ya kira driver a waya ya iso, kamin na bar asibitin sai ya nemi na dora masa ruwa.
“Kin ja min wanka matar nan duk kin lalata ni”
Juyowa nai na kalleshi da mamaki ina kokarin fita, sai ya kanne min ido daya ya aiko kin da sakon kiss. Ni kam dariya nai na fice daga dakin.
Ko da na isa gida na tararda Hajara na jira na, tana ganina taja hannuna muka nufi dakina na kori su Namra da ke ciki muka zauna saman katifa ta, sai ta bude jakarta ta dauko abun ta bude tana mika min daya bayan daya.
“Wannan idan zaki kwanta bachi zaki shafa shi a kasan mararki, za ki ji sanyi kamar kankara, wannan kuma a kasa za ki tona ki zuba garshi a kasa sai ki saka wannan karamin a gabanki wannan kuma ki zuba a garwashin sai ki yi tsuguno za ki ji na cikin ya nairke kamar mai kuli karki taba ki barshi haka ya kwana a jikinki sai da safe ki wanke da ruwan dumi, wannan garin kuma da madara za ki sha, shi kuma wannan na kwayun ki hade shi duka da ruwa hmmmmmm to kwanta ki yi bachinki ba kya bukatar komai Hajiyata shi wannan hadin ma ba a bawa mai kishiya saboda gudun hada fada ko haddasa saki, sai dai idan kun dawo ki yi dilke da sauran gyaran jiki”
Rumgume ta nai ina murna idan ba kawar amana kawar arziki ba wa zai maka wannan?
“Na gode sosai Hajara”
“Babu komai Allah dai ya baku zaman lafiya”
“Amin ya rabbi”
Na rakata har gurin motar mijinta mu kai sallama na dawo cikin gida, shi da na sha tun cikin dare na sha da wanda tace na yi tsuguna duk nai.
Ni kaina sai da na soma tabbatarda lallai akwai alamun maganin mai kyau ne, domin tun a jikina na ga canji fitsari da nake ma ina yi ina jin zafi abunda ko da ina budurwa ban ji ba. Tun da farar safiya ya kirani muka gaisa yace na bawa Mama wayar ya gaisa da ita yai mata bakwana sannan na kaiwa Inna ita ma sukai bankwana sannan ya aje wayar bayan ya fada su Namra ba za su je ba yau wai zasu mana rakiya airport. Misalin tara ya aiko da mota, gaba daya sai naji wani iri kamar kar na tafi saboda kewa ko zuwa wata area ma ina jin kewa balle kuma tafiya ce ta kasa da kasa, kamin na shiga motar sai da nai ta kuka ina jin kamar idan na tafi ba zan dawo ba, ba su Namra kadai suka raka mu ba har da Aisha da Hafiza. Kai tsaye gidansu Ahmad din aka wuce da mu mun ga tarba ta musamman Hajiya kamar ta hade ni ita da sauran mutanen da suka zo musu bankwan, ban saka Ahmad a ido ba sai da zamu bar gida sannan ya shigo dakin Hajiya domin ni a dakinta ta aje ni su Namra suka tsaya falo. Ya shigo cikin shiga ta alfarma kamar ba shi ba ko kunyar Hajiya be ji ba ya zauna kusa da ni yana karbar rubutun data miko masa, sai da ya shaye tass sannan ta bashi wani ya shanye ta dauko masa ruwan addu'a a nan kam yai fir wai ba zai sha yawun wani ba, rubutun ma dan kar ya mata gardama ne.
“Ni naga ma abun da sauki sosai Allah ya kara lafiya”
Ta fada cike da jindadi sannan ta fice, shi kam kamar yana jira ya mika hannu ya riko ni.
“I miss you”
“Dakin Hajiya muke fa”
Na fada ina kallon kofa domin na san ba karamin kunya zan ji ba idan ta gan mu. Dariya yai ya saki hannuna nawa. Ba mu wani dade sosai ba muka fito daga cikin gidan har na nufi motar da muka shigo sai Siyama tace.
“A a ba ita zaki shiga ba ga motarmu can”
Nikam kasa cewa komai nai sai dariya nake.
“Lims gulma ta take ko?”
“A a”
Ina amsa masa ya fito daga bandakin fuskarsa na ta haske irin ta sabon ango. A take ta dauki jakarta ta mike tsaye tana fadin.
“Ni dai na tafi Allah ya bada sauki”
Na amsa da amin ina binta da kallo shi kuma ya kabbatar sallah, hakan na bani damar tashi na shiga bandakin nai alwala na fito na jirashi har ya gama sannan na gabatar da tawa. Da kansa ya zuba mana abincin a plate daya spoon ma daya ya saka ya dora abincin gafena nikan sai kallonsa nake domin na lura tun jiya yana kokarin aikin da hannun.
“Hannun ba ya maka nauyi sosai ne?”
“Ba sosai yake min ba ina sai jin kamar jijiya ta rike ne”
Ya debo abincin da kansa ya kai mu a baki sannan shi ma ya ci. Shi yai feeding dina har na koshi sannan na karbi plate din na aje, sai kuma yaja ni jikinsa ya rumgume.
“Mata da miji idan suna zaune ba a zama nesa da juna ki koyi wannan yana kara soyayyar da shakuwa ko wani gurin muka je za mu rika tunani da kewar junanmu”
Yana gama fadar hakan ya saka hannunsa cikin hijabina yana kokarin kaiwa kirjina.
“Ba bari muji da akai wanka sun wanku”
Ya fada cikin rada sai nai saurin raba jikina da nashi.
“Baka da lafiya amman sai rashin ji kake....”
“Ahen ahen ahen please nahhhh”
Yayi maganar ta sigar shagwaba kamar wani dan 3 years sai marairaice min yake yana tabe baki irin yadda yara suke idan suna son abu. Nikam abun dariya ma ya bani wannan kuma ai ya zama ba jinya ba, duk yadda nai kokarin nisa da shi sai ya ce min ba haka ba. Sai da mutane suka fara shigowa sannan ya shafa min lafiya.
A yau kam na ga yan'uwan Ahmad sosai a asibitin wata kila saboda gobe zai bar kasar ne yasa suke ta zuwa kamar ana turowa idan wannan ya fita wata ko wani ne zai shigo, duk basa shigowa hannu sake masu kawo abinci ko siyayya wasu kuma idan za su fita sai su ba ni kudi, mun gaisa da wasu da yawa daga cikinsu ya gabatar da mu kuma ya gabatar ni a gurinsa kowa sa cewa yake sun ji abu daga sama wai ba sanarwa.
“Amaryar ce sai da haka shiyasa, sai da dabara”
“Ato ko dai kwace kai wa wani ne?”
Cewar wata tabashiyarsa tana dariya.
“To wannan tsaleliyar matar zan samu a banza, ai kinsan sai na yi da gaske, duk masu neman wasa suka tsaya ni kuma nai muku na shirwa”
Duk suka saka dariya har ni. Bayan sallah magariba na fara shirye shirye zuwa gida sai ya fara kallona kamar mai mamaki, nikam yau na rantse gida zan kwana ko da karbar sakon da Hajara tace min zata kawo idan an gama sallah isha'i.
“Ba dai gida za ki je ba ko”
“Gida mana, tun da gobe za mu tafi ai kara na ce gida tun yanzu sai na kwana can nai musu sallama”
“A a ni ba zan iya kwana babu ke ba”
“Can da da kake kwanan fa?”
“Can da ai ban rabi jikinki ba, yanzu kuma na saba kwana biyu nan ba zan iya ba gaskiya, haramun ne ma”
Ya fada yana riko hannuna.
“A a Mama tace na dawo gida na kwana so that nai sallama da su Namra”
Marairaice min yai.
“Tsoro nake ji, kuma ciwon zai iya tashi idan baki nan”
Yanayin yadda yai maganar yasa ban san lokacin da dariya ta subuce min ba. Shi kanshi dariya yai ya rumgume.
“i love you Babe, gaskiya ba zan jidadi ba idan baki kwana a nan ba, amman babu yadda na iya, dole nai hakuri”
“Yauwa na debi kala biyar na tafiya yayi? Kar na deba da yawa ya sama kauna”
Na fada daman ina son nai masa tambayar tun jiya.
“Ki kara”
“Za mu dade ne?”
“Ba sani ba tukuna, wata kila za mu dade wata kila ba za mu dade ba ya dangata daga yadda suka ba mu, amman kin san ko na ji sauki sai dai Hajiya ta dawo ta bar ku can ko?”
“Saboda me? Ba kai aka kai ba?”
“Kin san idan mutum ya dade yana jin kishin ruwa idan ya samu ruwan ba ya musu shan hankali”
Kallonsa nai da kyau ina mamakinsa a dacan idan aka ce min Ahmad zai yi haka wallahi zan karyata.
“Anya dai kai ne?”
“Ni ne fa, ai dan iskan cikin gida ne ni, Allah dai ya bani lafiya”
“Lafiya ai ta samu marar lafiya ba zai yi abunda kake ba”
“Ina ma kika sani hmmmm Allah dai ya kai damo ga harawa, ya nuna mana mu dan yi nisa da Hajiya akwai kara'i”
Ya karasa yana kwafa yana kokarin kyalkyalata, dariya nai sai yai kissing kumatuna yana shafa bayana, sai kuma ya dago fuskata ya soma tsosar bakina try to remove my Hijab, sai da nai da gaske sannan na raba jikina da shi.
“Komai abunki dai dole ki jira driver ya zo or else ki kwana nan dan ba zan bari ki hau Napep ba ana kalle min kaya”
A nan ma dariya nai ina ta jin kunyarsa sai dai na lura sam ya sauya kamar ba shi ba kunyar ma bata gabansa, hannunsa kuma baya zama kurum matukar muna zaune dakin daga ni sai shi. A dole nai jiran ya kira driver a waya ya iso, kamin na bar asibitin sai ya nemi na dora masa ruwa.
“Kin ja min wanka matar nan duk kin lalata ni”
Juyowa nai na kalleshi da mamaki ina kokarin fita, sai ya kanne min ido daya ya aiko kin da sakon kiss. Ni kam dariya nai na fice daga dakin.
Ko da na isa gida na tararda Hajara na jira na, tana ganina taja hannuna muka nufi dakina na kori su Namra da ke ciki muka zauna saman katifa ta, sai ta bude jakarta ta dauko abun ta bude tana mika min daya bayan daya.
“Wannan idan zaki kwanta bachi zaki shafa shi a kasan mararki, za ki ji sanyi kamar kankara, wannan kuma a kasa za ki tona ki zuba garshi a kasa sai ki saka wannan karamin a gabanki wannan kuma ki zuba a garwashin sai ki yi tsuguno za ki ji na cikin ya nairke kamar mai kuli karki taba ki barshi haka ya kwana a jikinki sai da safe ki wanke da ruwan dumi, wannan garin kuma da madara za ki sha, shi kuma wannan na kwayun ki hade shi duka da ruwa hmmmmmm to kwanta ki yi bachinki ba kya bukatar komai Hajiyata shi wannan hadin ma ba a bawa mai kishiya saboda gudun hada fada ko haddasa saki, sai dai idan kun dawo ki yi dilke da sauran gyaran jiki”
Rumgume ta nai ina murna idan ba kawar amana kawar arziki ba wa zai maka wannan?
“Na gode sosai Hajara”
“Babu komai Allah dai ya baku zaman lafiya”
“Amin ya rabbi”
Na rakata har gurin motar mijinta mu kai sallama na dawo cikin gida, shi da na sha tun cikin dare na sha da wanda tace na yi tsuguna duk nai.
Ni kaina sai da na soma tabbatarda lallai akwai alamun maganin mai kyau ne, domin tun a jikina na ga canji fitsari da nake ma ina yi ina jin zafi abunda ko da ina budurwa ban ji ba. Tun da farar safiya ya kirani muka gaisa yace na bawa Mama wayar ya gaisa da ita yai mata bakwana sannan na kaiwa Inna ita ma sukai bankwana sannan ya aje wayar bayan ya fada su Namra ba za su je ba yau wai zasu mana rakiya airport. Misalin tara ya aiko da mota, gaba daya sai naji wani iri kamar kar na tafi saboda kewa ko zuwa wata area ma ina jin kewa balle kuma tafiya ce ta kasa da kasa, kamin na shiga motar sai da nai ta kuka ina jin kamar idan na tafi ba zan dawo ba, ba su Namra kadai suka raka mu ba har da Aisha da Hafiza. Kai tsaye gidansu Ahmad din aka wuce da mu mun ga tarba ta musamman Hajiya kamar ta hade ni ita da sauran mutanen da suka zo musu bankwan, ban saka Ahmad a ido ba sai da zamu bar gida sannan ya shigo dakin Hajiya domin ni a dakinta ta aje ni su Namra suka tsaya falo. Ya shigo cikin shiga ta alfarma kamar ba shi ba ko kunyar Hajiya be ji ba ya zauna kusa da ni yana karbar rubutun data miko masa, sai da ya shaye tass sannan ta bashi wani ya shanye ta dauko masa ruwan addu'a a nan kam yai fir wai ba zai sha yawun wani ba, rubutun ma dan kar ya mata gardama ne.
“Ni naga ma abun da sauki sosai Allah ya kara lafiya”
Ta fada cike da jindadi sannan ta fice, shi kam kamar yana jira ya mika hannu ya riko ni.
“I miss you”
“Dakin Hajiya muke fa”
Na fada ina kallon kofa domin na san ba karamin kunya zan ji ba idan ta gan mu. Dariya yai ya saki hannuna nawa. Ba mu wani dade sosai ba muka fito daga cikin gidan har na nufi motar da muka shigo sai Siyama tace.
“A a ba ita zaki shiga ba ga motarmu can”