Sashe 21
Gobe Na Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Har na yi kamar ba zan juyo ba sai kuma na juyo na kalleshi. Bude motarsa yai ya dauko wata ledar ya miko min.
“Ga wannan inji kawarki tace a gaishe ki”
“Ka maida maita ka fada mata bana son gaisuwarta kuma ka fada mata karta sake aiko ka a kofar gidanmu da sunan gaisuwa”
Dariya yai yana gyara tsayuwar agogon hannunsa.
“Halimatu kenan, ba zuwa Hajara ne kawai ba, ni kana na ga akwai bukatar na kawo gaisuwa kuma na jajanta miki akan abunda ya faru”
“Da alama baka fahimci da wane yare nake maka magana ba, amman idan ita idan ka isar mata zata fassara maka”
Ina fada masa hakan ta juya na koma cikin cike da mamakin karfin hali irin na Hajara, shi ma kansa Isma'il din mamaki ya bani domin na lura ba shi da kunya irin yadda na ke da Hajara ai ko ni na tallata masa kaina a tunani be kamata ya amsa min ba.
Bayan na koma cikin gidan na shirya, na fito da zimmar zuwa gurin aikina ba, abun mamaki sai na kasa samun abun hawa kamar dai wacan karon, ganin haka yasa na canja shawara daga zuwa gurin aiki na nufi Hauwa International School, wato makarantar su Namra kamar da wasa na tari wani mai napep ya tsaya hakan ba karamin dadi yai min ba ban ko tsaya fada masa inda zanje ba na shiga ciki da murna yadda kasa wance bata saba shiga Napep ba, ina cikin fada masa inda zai kai ni wayata tai ringing, sai da Hajara ta jera min kira hudu sannan na daga rai a bace.
“Minene?”
“Haba Halimatu ai ko dan ya kamata ki mutunta Mijina”
“Naga alamar ke da mijin na ki kamar ba ku da hankali Hajara, na gargade shi ke ma kuma na gargade ki karki sake yi min wannan wasa”
“Ni dai van kora dan wani gargadin ki ba, na kira ne kawai na fada miki ban fada masa abunda ya fito dake daga gidan mijinki ba, kuma ban fada masa abunda ya samu Namra ba, kuma ni mijina ba zuwa yai ya fada miki cewar yana son ki ba, cewa ina son ki abu ne mai tsada a gurin mijina ya fara gadaki ne ya ga ruwanki...”
Ta karasa tana dariya sannan ta kashe wayar ba tare da jiran irin amsar da zan bata ba. Kadan ya rage mamaki ya kashe ni anya Hajara na cikin hankalinta kuwa kuma ta san abunda take kokarin aikatawa? Wai daman da gaske take da take zancen mijinta ya aureni? Ko kuwa dai gwadani take? Idan gaskoya ne ko karya ni ba zan iya auren mijin kawata ba, yar'uwata ma zance domin Hajara ta fi karfin kawa a gurina. Har na isa makarantar nai abunda zan yi na gama na kama hanyar aikina ban daina mamaki ba da kuma jinjina karfi hali irin yana anya irin matan nan suna nan kuwa? Ni sam na kasa yarda da gaske take ma.
*BAYAN WATA DAYA.*
Babu makarantar da ban leka ba nai yawo da takardun transfer su Adnan ba amman aka ki karbarsu a ko'ina, daga private school har na gobnati abun har tsoro ya soma ba ni, a duk makarantar da na kai su sai su kamar za su karba sai kuma su bullo da wani abun, wata makaranta ma ko kallona ba sa yi yadda kasan wacce akai wa wani magani haka nai ta shimlalo a gari neman makarantar da zata dauki su Adnan da Namra amman ina!
Hakan yasa n watsar da zancen karatunsu na maida hankalina gurin aikina duk kuwa da kasancewar bana jindadin aiki a yanzu saboda rashin Kabir ba kuma dan na shaku da shi ba sai dan tuna abunda ya same ni yana ni walwala a cikin office din, musamman da aka kawo wani da zai maye gurbinsa, ko da wasa ban sake gwada zuwa duba shi asibiti ba, sai dai na kan gwada kiran wayarsa kuma bana samu, ta hanyar wani abokinsa da ke aiki a inda nake na samu labarin cewar an kai shi kano a asibitin kwakwalwa saboda abun ya taba hankalinsa, na tauyasa masa ba kadan ba na kuma tausayawa matarsa da duka danginsa musamman da na samu labarin cewar iyayensa duka biyu basa raye, ta wani bangaren kuma ina tausayin kaina domin ban san me gobena ta tanadar min ba ban san abunda zan tarar nan gaba ba.
*Lahadi*
Kasancewar yau ranar hutu ce kamar dai jiya sa ta kasance asabar, dukan mu muna zaune gida har kanena ana ta zancen duniya, yawancin firar da muke ta rashin tsaro da ke addabar al'ummar mu ne da kuma tsadar rayuwa da muke ciki, ina zaune Abdallah ya shigo ya gaishe da Mama da Inna kanena kuma suka gaishe shi ya amsa musu amman bakina be hadu da na shi ba, ba baki kadai ba idona ma ban daga na kalleshi ba balle har na mika masa gaisuwa. Tashi nai ya nufi daki yana rike da hannu Namra waccena lura tana sakewa da shi sosai a duk lokacin da ya leko mu, Mama ta tashi ta bi bayansa suka shiga falon tare, ina nan waje zaune amman hankalina yana can inda suke duk na bi na tsargu sai kace wacce tai wani abun gulma.
Bayan yan mintuna Namra ta fito hannunta rike da chocolate.
“Momy wai ki zo inji Mama”
Na tashi cikin kuzari na bi bayanta, ina shigowa idonsa na kaina kamar daman can rayuwarsa ta takaita akan kallona ne kawai.
“Miya hanaki saka su makaranta”
“Na kai su ba a karba ne”
Na fada ina dan turo baki a shagwabe abunda ban saba ba, kuma ban san dalilin zuwansa a yanzu ba.
“Daman ai ba za akarbe su ba tunda kika bata min rai”
Ya fada yaa ta kallona da idonsa kamar maye, sai a yanzu na fahimci inda zance ya dosa, kar dai kwahi yai min aka ki karbar su a makaranta saboda shi twins ne shi da Abdulhamid.
“Kwahi kai min kenan? Ai ni kwahin ka ba zai kama ni ba”
“Kwarai shiyasa ranar ai kika samu Napep ta kawo ki har gida”
Har yanzu kallona yake yi irin kallon nan kamar ni din tv sa ce.
“To wani abun kika masa kenan?”
Cewar Mama tana murmushi, ni kuma na maida hankali gurin kiran wayata da ke shigowa.
Abdulhamid ne rubuce a screen din wayar, hakan ya saka gabana faduwa ba dan komai na sai dan Abdallah na zaune a falon, kusan tun lokacin da na fito nai bari Abdulhamid be taba kirana da sunan yi min jaye ko sannu ba, ba zan ce dan be ji ba, domin ko last time da Hajiya ta zo ta fada min cewar Abdulhamid ya kawo ta amman be shigo cikin gida ba.
“Hello....”
“Haima”
Gabana ne ya yanke ya fadi jin ya kira ni da sunan da na manta when last ya kirani da sunan.
“Na'am... ”
Na amsa kamar mai koyon magana.
“Kina lafiya?”
“Lafiya Kalau”
“Ina fatar kina gida, gani nan zuwa amman ba zan shigo cikin gida ba magana kawai zan yi da ke na koma”
“To... ”
Ina amsawa ya kashe wayar, idon Abdallah na kaina tana ta min kallon tuhuma, ni kuma na gagara tsayuwa na gagara zama sai yawo na ke da ido kamar marar gaskiya, ba dan komai ba sai dan bana son Abdulhamid ya zo ya tarar da Abdallah, duk kuwa da ban san abunda zai kawo shi ba na san dole daya daga cikinsu ya zargi wani abu. Musamman Abdallah da ya fiye shiga hanci da saka min ido.
#TeamAbdulhamind
#TeamAbdallah
#TeamAminu 😜
#TeamHalimatu
7/20/21, 8:30 AM - Buhainat: *GOBE NA...*
_My Tomorrow_
By Khadeeja Candy
1️⃣3️⃣
“Kamar baki da gaskiya Halimatu...”
Sai da na kalli Mama sannan na kalleshi.
“Bana da gaskiya kamar ya? Wannan wace irin magana ce Abdallah?”
Ya dan tabe baki yana ta wasa da hannun Amal kamar ba shi yai maganar ba. Kamar an daki hannuna sai na yi yai min majiyar, ban san lokacin da na saki wayar hannuna ta subuce ta fadi kasa, a take ta watse a saman tedar da ke falon kamar abar da aka taka da mota ko aka sakawa dutse aka daddaka. Subhanallahi Mama ta furta ni kuma na risina a gurin ina kallon wayar ina jin kamar na fasa kuka tuni idona suka cika da kwalla, har ga Allah na tsani na rasa wani abun da na ke matukar so ko yake da muhimmancin sosai a rayuwata, na san phone ce amman ina jin babu dadi domin samun irinta a yanzu ba abu mai sauki a gareni a lokacin da na ke gidanmu dawainiya ta zata min yawa yanzu fiye da, ga kuma zuwan da Abdulhamid zai yi ban san abunda zai kawo shi ba wata kila ma baya son kowa ya san da zuwansa.
“Ya akai wayar ta fadi?”
Mama ta tambaya sai an amsa mata muryata na gargada alamar ina daf da fashe da kuka.
“Ban sani ba Mama a hannu ta zame ta fadi”
“Laa shikenan wayar Momy ta fashe bamu da wayar game”
Namra ta fada tana wani bude baki, Abdallah kam ko dago kai be yi ya kalleni ba sai wasa yake da yatsun Amal kamar be san abunda ya faru ba.
“Momy yanzu da wace wayar za mu rika game...?”
Wani bakin haushi na ji ban san lokacin da na dakawa Namra wacce tai maganar tsawa ba.
“Da wayar ubanki... ”
Sai a lokaci Abdallah ya dago ya kalleni sai kuma ya kalli inda wayar take ba ce min komai ba sai dai fuskarsa ta nuna alamar bachin rai, mikewa yai tsaye yana saa dayan hannunsa a aljihu.
“Mama ni zan tafi, kuma yaran nan a yi kokarin saka su makaranta domin barin su hakan nan ba zai yiyu ba ya kamata a san abun yi lokaci na ta tafiya”
“Ga wannan inji kawarki tace a gaishe ki”
“Ka maida maita ka fada mata bana son gaisuwarta kuma ka fada mata karta sake aiko ka a kofar gidanmu da sunan gaisuwa”
Dariya yai yana gyara tsayuwar agogon hannunsa.
“Halimatu kenan, ba zuwa Hajara ne kawai ba, ni kana na ga akwai bukatar na kawo gaisuwa kuma na jajanta miki akan abunda ya faru”
“Da alama baka fahimci da wane yare nake maka magana ba, amman idan ita idan ka isar mata zata fassara maka”
Ina fada masa hakan ta juya na koma cikin cike da mamakin karfin hali irin na Hajara, shi ma kansa Isma'il din mamaki ya bani domin na lura ba shi da kunya irin yadda na ke da Hajara ai ko ni na tallata masa kaina a tunani be kamata ya amsa min ba.
Bayan na koma cikin gidan na shirya, na fito da zimmar zuwa gurin aikina ba, abun mamaki sai na kasa samun abun hawa kamar dai wacan karon, ganin haka yasa na canja shawara daga zuwa gurin aiki na nufi Hauwa International School, wato makarantar su Namra kamar da wasa na tari wani mai napep ya tsaya hakan ba karamin dadi yai min ba ban ko tsaya fada masa inda zanje ba na shiga ciki da murna yadda kasa wance bata saba shiga Napep ba, ina cikin fada masa inda zai kai ni wayata tai ringing, sai da Hajara ta jera min kira hudu sannan na daga rai a bace.
“Minene?”
“Haba Halimatu ai ko dan ya kamata ki mutunta Mijina”
“Naga alamar ke da mijin na ki kamar ba ku da hankali Hajara, na gargade shi ke ma kuma na gargade ki karki sake yi min wannan wasa”
“Ni dai van kora dan wani gargadin ki ba, na kira ne kawai na fada miki ban fada masa abunda ya fito dake daga gidan mijinki ba, kuma ban fada masa abunda ya samu Namra ba, kuma ni mijina ba zuwa yai ya fada miki cewar yana son ki ba, cewa ina son ki abu ne mai tsada a gurin mijina ya fara gadaki ne ya ga ruwanki...”
Ta karasa tana dariya sannan ta kashe wayar ba tare da jiran irin amsar da zan bata ba. Kadan ya rage mamaki ya kashe ni anya Hajara na cikin hankalinta kuwa kuma ta san abunda take kokarin aikatawa? Wai daman da gaske take da take zancen mijinta ya aureni? Ko kuwa dai gwadani take? Idan gaskoya ne ko karya ni ba zan iya auren mijin kawata ba, yar'uwata ma zance domin Hajara ta fi karfin kawa a gurina. Har na isa makarantar nai abunda zan yi na gama na kama hanyar aikina ban daina mamaki ba da kuma jinjina karfi hali irin yana anya irin matan nan suna nan kuwa? Ni sam na kasa yarda da gaske take ma.
*BAYAN WATA DAYA.*
Babu makarantar da ban leka ba nai yawo da takardun transfer su Adnan ba amman aka ki karbarsu a ko'ina, daga private school har na gobnati abun har tsoro ya soma ba ni, a duk makarantar da na kai su sai su kamar za su karba sai kuma su bullo da wani abun, wata makaranta ma ko kallona ba sa yi yadda kasan wacce akai wa wani magani haka nai ta shimlalo a gari neman makarantar da zata dauki su Adnan da Namra amman ina!
Hakan yasa n watsar da zancen karatunsu na maida hankalina gurin aikina duk kuwa da kasancewar bana jindadin aiki a yanzu saboda rashin Kabir ba kuma dan na shaku da shi ba sai dan tuna abunda ya same ni yana ni walwala a cikin office din, musamman da aka kawo wani da zai maye gurbinsa, ko da wasa ban sake gwada zuwa duba shi asibiti ba, sai dai na kan gwada kiran wayarsa kuma bana samu, ta hanyar wani abokinsa da ke aiki a inda nake na samu labarin cewar an kai shi kano a asibitin kwakwalwa saboda abun ya taba hankalinsa, na tauyasa masa ba kadan ba na kuma tausayawa matarsa da duka danginsa musamman da na samu labarin cewar iyayensa duka biyu basa raye, ta wani bangaren kuma ina tausayin kaina domin ban san me gobena ta tanadar min ba ban san abunda zan tarar nan gaba ba.
*Lahadi*
Kasancewar yau ranar hutu ce kamar dai jiya sa ta kasance asabar, dukan mu muna zaune gida har kanena ana ta zancen duniya, yawancin firar da muke ta rashin tsaro da ke addabar al'ummar mu ne da kuma tsadar rayuwa da muke ciki, ina zaune Abdallah ya shigo ya gaishe da Mama da Inna kanena kuma suka gaishe shi ya amsa musu amman bakina be hadu da na shi ba, ba baki kadai ba idona ma ban daga na kalleshi ba balle har na mika masa gaisuwa. Tashi nai ya nufi daki yana rike da hannu Namra waccena lura tana sakewa da shi sosai a duk lokacin da ya leko mu, Mama ta tashi ta bi bayansa suka shiga falon tare, ina nan waje zaune amman hankalina yana can inda suke duk na bi na tsargu sai kace wacce tai wani abun gulma.
Bayan yan mintuna Namra ta fito hannunta rike da chocolate.
“Momy wai ki zo inji Mama”
Na tashi cikin kuzari na bi bayanta, ina shigowa idonsa na kaina kamar daman can rayuwarsa ta takaita akan kallona ne kawai.
“Miya hanaki saka su makaranta”
“Na kai su ba a karba ne”
Na fada ina dan turo baki a shagwabe abunda ban saba ba, kuma ban san dalilin zuwansa a yanzu ba.
“Daman ai ba za akarbe su ba tunda kika bata min rai”
Ya fada yaa ta kallona da idonsa kamar maye, sai a yanzu na fahimci inda zance ya dosa, kar dai kwahi yai min aka ki karbar su a makaranta saboda shi twins ne shi da Abdulhamid.
“Kwahi kai min kenan? Ai ni kwahin ka ba zai kama ni ba”
“Kwarai shiyasa ranar ai kika samu Napep ta kawo ki har gida”
Har yanzu kallona yake yi irin kallon nan kamar ni din tv sa ce.
“To wani abun kika masa kenan?”
Cewar Mama tana murmushi, ni kuma na maida hankali gurin kiran wayata da ke shigowa.
Abdulhamid ne rubuce a screen din wayar, hakan ya saka gabana faduwa ba dan komai na sai dan Abdallah na zaune a falon, kusan tun lokacin da na fito nai bari Abdulhamid be taba kirana da sunan yi min jaye ko sannu ba, ba zan ce dan be ji ba, domin ko last time da Hajiya ta zo ta fada min cewar Abdulhamid ya kawo ta amman be shigo cikin gida ba.
“Hello....”
“Haima”
Gabana ne ya yanke ya fadi jin ya kira ni da sunan da na manta when last ya kirani da sunan.
“Na'am... ”
Na amsa kamar mai koyon magana.
“Kina lafiya?”
“Lafiya Kalau”
“Ina fatar kina gida, gani nan zuwa amman ba zan shigo cikin gida ba magana kawai zan yi da ke na koma”
“To... ”
Ina amsawa ya kashe wayar, idon Abdallah na kaina tana ta min kallon tuhuma, ni kuma na gagara tsayuwa na gagara zama sai yawo na ke da ido kamar marar gaskiya, ba dan komai ba sai dan bana son Abdulhamid ya zo ya tarar da Abdallah, duk kuwa da ban san abunda zai kawo shi ba na san dole daya daga cikinsu ya zargi wani abu. Musamman Abdallah da ya fiye shiga hanci da saka min ido.
#TeamAbdulhamind
#TeamAbdallah
#TeamAminu 😜
#TeamHalimatu
7/20/21, 8:30 AM - Buhainat: *GOBE NA...*
_My Tomorrow_
By Khadeeja Candy
1️⃣3️⃣
“Kamar baki da gaskiya Halimatu...”
Sai da na kalli Mama sannan na kalleshi.
“Bana da gaskiya kamar ya? Wannan wace irin magana ce Abdallah?”
Ya dan tabe baki yana ta wasa da hannun Amal kamar ba shi yai maganar ba. Kamar an daki hannuna sai na yi yai min majiyar, ban san lokacin da na saki wayar hannuna ta subuce ta fadi kasa, a take ta watse a saman tedar da ke falon kamar abar da aka taka da mota ko aka sakawa dutse aka daddaka. Subhanallahi Mama ta furta ni kuma na risina a gurin ina kallon wayar ina jin kamar na fasa kuka tuni idona suka cika da kwalla, har ga Allah na tsani na rasa wani abun da na ke matukar so ko yake da muhimmancin sosai a rayuwata, na san phone ce amman ina jin babu dadi domin samun irinta a yanzu ba abu mai sauki a gareni a lokacin da na ke gidanmu dawainiya ta zata min yawa yanzu fiye da, ga kuma zuwan da Abdulhamid zai yi ban san abunda zai kawo shi ba wata kila ma baya son kowa ya san da zuwansa.
“Ya akai wayar ta fadi?”
Mama ta tambaya sai an amsa mata muryata na gargada alamar ina daf da fashe da kuka.
“Ban sani ba Mama a hannu ta zame ta fadi”
“Laa shikenan wayar Momy ta fashe bamu da wayar game”
Namra ta fada tana wani bude baki, Abdallah kam ko dago kai be yi ya kalleni ba sai wasa yake da yatsun Amal kamar be san abunda ya faru ba.
“Momy yanzu da wace wayar za mu rika game...?”
Wani bakin haushi na ji ban san lokacin da na dakawa Namra wacce tai maganar tsawa ba.
“Da wayar ubanki... ”
Sai a lokaci Abdallah ya dago ya kalleni sai kuma ya kalli inda wayar take ba ce min komai ba sai dai fuskarsa ta nuna alamar bachin rai, mikewa yai tsaye yana saa dayan hannunsa a aljihu.
“Mama ni zan tafi, kuma yaran nan a yi kokarin saka su makaranta domin barin su hakan nan ba zai yiyu ba ya kamata a san abun yi lokaci na ta tafiya”