Sashe 23
Gobe Na Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Yarinyar ta fada yana nuna inda Mug din yake sai a lokacin na lura da mug din, da alama yarinyar irin yaran nan masu shegen kodin tsiya da tsiwa, domin har wani juya ido take tana motsa baki kamar wata babba. Babbar kuma wacce ta fi tsananin kama da shi ta hau baya tana dago min hannu.
“Bye..... ”
Ikon Allah su kuma haka suke? Sun buge ni ko sannu babu? Ko ma miya tsayar da ni kallonsu oho, daman can da ganinsu ai ba gidan mutunci suka fito ba. Ni kadai nake ta mita ta a cikin raina har muka iso gida, sannan na karbe chocolate din da Amal ta dauka na yarinyar na jefar, babu irin kukan da ba tai ba na ki na kulata har ta gaji tai bachi.
Washe gari bayan mun gama karyawa na fara shirin zuwa aikina, kanwata Husna ta shigo wai na zo falon Mama ana kirana, ta gwarin guiwata na nufi falon Mama ance karka ji tsoron kira ka ji tsoron laifin da ka aikata, na shiga falon da rabon ido dan ganin mai kirana sai naga Mama ce kadai a falon hannunta rike da farar leda mai rubutu da zanen wayoyi a jiki.
“Mama ke kike kirana?”
“Aa Abdulhamid ne yana waje saka hijabinki ki masa godiya waya ya kawo yace a baki”
Ta amsa min cikin rashin jindadi da walwala. Dakinta na shiga na dauko hijabi na nufi kofar gidan. Sai na same shi cikin farar motarsa zaune yana danna wayarsa, farin gilashin motar na kwankwasa da zimmar ya bude min na gaishe shi kuma nai masa godiya sai na ga ya miko hannunsa daga can cikin motar ya bude min motar da alama so yake na shiga ciki na zauna. Haka kuwa akai na shiga uncomfortable na zauna sannan na mika masa gaisuwa be amsa min ba kuma be kalleshi ba har lokacin taba wayarsa yake.
“Yau ba zaki je aiki ba ne?”
“Zanje ina cikin ne aka ce kana kirana”
Sai a lokacin ya dago ya kalleshi a natse. To je ki karasa shirinki sai na kai ki. Kallonsa nai har na bude baki na ce masa a a sai kuma na tuna da abunda ya faru da ni a lokacin da nai gardama da Abdallah ban sani ba shi ma ko yana da kohin kar ya min na kasa samun abun hawa.
“To by the way na ga waya na gode sosai”
“No no no never mind je ki shirya kawai”
Ya fada yana dauke idonsa daga barin kallona, ni kuma na fita daga motar na shiga cikin gidan na karasa shirina sannan na shiga falon Mama dan mata sallama kuma n karbi wayar da har yanzu bana jin murnar siya min ita da yai. Wani kallo tuhuma Mama tai min sai duk na ji babu dadi a take shikan shikan rashin natsuwa suka bayyana a jikina da kuma fuskata.
“Ina kyautata zaton Abdulhamid be san Abdallah na zuwa gidan nan ba, kamar yadda yau din ma nake kyautata zaton Abdallah be san Abdulhamid ya zo ba, sai dai ke kin sani kuma ina tunanin kin san daidai da rashinsa, na dade da fahimtar cewar Abdallah yana son ki ko dan saboda kulawar da yake nunawa yaran nan, sai dai abunda ban sani ba kuma nake son sani a yanzu shi ma Abdulhamid son ki yake yi?”
I find it so difficult na amsa mata, ni kaina a yanzu ban sani ba iyakar abunda na sani Abdallah na so ko be fada min ba ya nuna min balle kuma ya fada min tun a lokacin da igiyar auren Aminu take kaina, ba zan iya shaidar abunda ya kawo Abdulhamid a yau ba, domin bana da tabbaci yana so na har yanzu kamar yadda zuciyata ya kasa goge shi a raina, ko kuwa dai tausayine kawai a tsakaninmu.
“Dukansu yan'uwna junane Halimatu kin sani, bayan yan'uwanta ta jini ma su tagwaye ni a ciki daya suka fito a rana daya kuma a mahaifa daya, mace daya ta raine su uba daya ya haife su, karki aikata abunda zai zame mana matsala ni da mahaifinki domin uwar data haifi mahaifinki ita ce ta haifi mahaifin Abdallah, mahaifin Abdallah da mahaifinki uwa daya uba daya suke karki lalata alaka Halimatu”
“Ban kira Abdallah na ce ya zo nan, zuwan Abdulhamid a yau ma bana da masaniya sai da na ganshi”
“Ba shi nake kokarin fahimtar da ke ba, ki sallami daya daga cikinsu saboda gudun abunda zai iya faruwa a gobenki, idan kuma dukansu ba ki ra'ayinsu to ki sallame su duka shi ya fi alheri Allah ya tsare a dawo lafiya”
Ya miko min ledar sannan ta mike tsaye ta fice ta bar a falon tsaye, ji nai kamar a san saka gatari an sare duk wata gaba ta kuzari da ke jikina. Kamar wata marar lakka haka na fito daga cikin gidan na nufi inda motarsa take na bude na shiga shi kuma ya tashi motar muka hau hanya.
“Ban jajanta miki kan abunda ya faru ba, na yi hakan ne saboda na baki lokaci ki huce bacin ranki, kuma bana son wata magana ta shiga tsakanina da ke a lokacin da kike idda, ko da ko gaisuwa ce, amman yanzu ina jin I'm free to name what ever i want daga gareki saboda kina da yanci”
Ban ce masa komai ba ina ta kokarin maida hankalina gurin titi amman na kasa, magaganun Mama sun tsaya min a kai.
“Ban jidadin abunda ya faru ba, Aminu kuma be yi miki hallaci ba amman mai hakuri yana tare da nasara, kuma kansa yai ma na san wata rana zai yi nadama ya gane cewar yayi kuskure a lokacin da ke din kin masa nisa”
Still ban ce masa kuma ba, hakan kuma be hana shi cigaba da magana ba.
“Jarabawa ce ta rayuwa, you know wani lokacin Allah yana jarraba bayinsa da abubuwa daban dabam, kamar yadda ya jarrabe ki da miji kamar Aminu ni kuma ya jarabe ni da cutar da na kasa samun maganinta har yanzu, wanda hakan yasa har bana son kawo tunanin aure a rayuwata....”
Juyowa nai na kalleshi a take zuciyata ta cika da tausayinsa.
“A da na sadakar na cire rai daga samun lafiya, kuma na aje duk wani abu na neman magani, amman daga lokacin da na ji cewar Aminu ya sake ki sai na nemi duk wannan abun na rasa, na ji cewar a yanzu ya dace na nemi magani kuma na nemi aurenki ko da ba za ki so ni ba, ba dan komai ba sai dan na faranta miki kuma na cika burina a kanki, ban sani ba ko akwai soyayyar Abdulhamid a zuciyar Halimatu ko a a, idan ma babu zan yi kokarin samawa idan kuma akwai sai na kafafata na ingantata”
Ya karasa daidai lokacin da ya faka motarsa a ma'aikatarmu sai ya zauna daidai yana dubana da fuskarsa ta tausayi.
“Na san za ki mamaki jin irin wannan maganar daga bakina kai tsaye kuma a karon farko da na ziyarce ki, daman abunda na ke son mu tattauna kenan a jiya, saboda ina son nai mata sha daya ne idan ma hadiye zuciya zan yi na mutu na san makomata idan kuma dama za ki ba ni nan ma na san makomata, ni dai har gobe ina son ki Halimatu kuma ina alakanta abunda Aminu yai miki da rashin aurenki da nai ta hanyar kin yarda da shawararki ta cewar na aureki na cigaba da neman magani za ki yi hakuri da ni a haka, ko kuma ki jira ni na nemi magani amman duka na ki yarda, na san da cewar Allah ta rubuto hakan zai faru amman komai yana da sila....”
Jimmm nai na dan wasu mintuna sannan na ya cigaba.
“Wata kila zuciyarki ta raya miki cewar na cika son kai a yanzu ko? Kina da gaskiya ba ko wace mace ce zata auri namiji irina ba, shiyasa ban gwada neman kowa ba sai ke ban taba saka son wata mace a raina ba sai ke kuma har gobe ke ce a raina Halimatu, zan iya baki damar yin shawara matukar kika ji za ki iya aurena a haka, ko kuma ki jira har na samu lafiya zan fi kowa farinciki, idan kuma kika ji ba za ki iya ba nan ma ba zan zarge ki ba.... ”
“Zan shiga office na gode”
Shine kawai abunda na fada na share hawayen da suka fara min zuba tun a lokacin daya fara maganar.......
Anya Halimatu zata iya zabe tsakanin dan'uwa da dan'uwa?
Anya zata iya zaba tsakanin mutuwa da rayuwa? Domin auren namiji irin Abdulhamid mutuwa da rayuwa ne.
A ganinku waya dace ta zaba?
Ina labarin Aminu ne?
Ko ya Kabir yake?
Shi kuma Abdallah haka yake da an bata masa rai sai kohi 🤣🤔
#TeamAminu
#TeamAbdulhami
#TeamAbdallah
#TeamHalimatu
#ZawarcinHalimatu
#Gobena
7/20/21, 8:30 AM - Buhainat: *GOBE NA...*
_My Tomorrow_
By Khadeeja Candy
1️⃣4️⃣
“Bye..... ”
Ikon Allah su kuma haka suke? Sun buge ni ko sannu babu? Ko ma miya tsayar da ni kallonsu oho, daman can da ganinsu ai ba gidan mutunci suka fito ba. Ni kadai nake ta mita ta a cikin raina har muka iso gida, sannan na karbe chocolate din da Amal ta dauka na yarinyar na jefar, babu irin kukan da ba tai ba na ki na kulata har ta gaji tai bachi.
Washe gari bayan mun gama karyawa na fara shirin zuwa aikina, kanwata Husna ta shigo wai na zo falon Mama ana kirana, ta gwarin guiwata na nufi falon Mama ance karka ji tsoron kira ka ji tsoron laifin da ka aikata, na shiga falon da rabon ido dan ganin mai kirana sai naga Mama ce kadai a falon hannunta rike da farar leda mai rubutu da zanen wayoyi a jiki.
“Mama ke kike kirana?”
“Aa Abdulhamid ne yana waje saka hijabinki ki masa godiya waya ya kawo yace a baki”
Ta amsa min cikin rashin jindadi da walwala. Dakinta na shiga na dauko hijabi na nufi kofar gidan. Sai na same shi cikin farar motarsa zaune yana danna wayarsa, farin gilashin motar na kwankwasa da zimmar ya bude min na gaishe shi kuma nai masa godiya sai na ga ya miko hannunsa daga can cikin motar ya bude min motar da alama so yake na shiga ciki na zauna. Haka kuwa akai na shiga uncomfortable na zauna sannan na mika masa gaisuwa be amsa min ba kuma be kalleshi ba har lokacin taba wayarsa yake.
“Yau ba zaki je aiki ba ne?”
“Zanje ina cikin ne aka ce kana kirana”
Sai a lokacin ya dago ya kalleshi a natse. To je ki karasa shirinki sai na kai ki. Kallonsa nai har na bude baki na ce masa a a sai kuma na tuna da abunda ya faru da ni a lokacin da nai gardama da Abdallah ban sani ba shi ma ko yana da kohin kar ya min na kasa samun abun hawa.
“To by the way na ga waya na gode sosai”
“No no no never mind je ki shirya kawai”
Ya fada yana dauke idonsa daga barin kallona, ni kuma na fita daga motar na shiga cikin gidan na karasa shirina sannan na shiga falon Mama dan mata sallama kuma n karbi wayar da har yanzu bana jin murnar siya min ita da yai. Wani kallo tuhuma Mama tai min sai duk na ji babu dadi a take shikan shikan rashin natsuwa suka bayyana a jikina da kuma fuskata.
“Ina kyautata zaton Abdulhamid be san Abdallah na zuwa gidan nan ba, kamar yadda yau din ma nake kyautata zaton Abdallah be san Abdulhamid ya zo ba, sai dai ke kin sani kuma ina tunanin kin san daidai da rashinsa, na dade da fahimtar cewar Abdallah yana son ki ko dan saboda kulawar da yake nunawa yaran nan, sai dai abunda ban sani ba kuma nake son sani a yanzu shi ma Abdulhamid son ki yake yi?”
I find it so difficult na amsa mata, ni kaina a yanzu ban sani ba iyakar abunda na sani Abdallah na so ko be fada min ba ya nuna min balle kuma ya fada min tun a lokacin da igiyar auren Aminu take kaina, ba zan iya shaidar abunda ya kawo Abdulhamid a yau ba, domin bana da tabbaci yana so na har yanzu kamar yadda zuciyata ya kasa goge shi a raina, ko kuwa dai tausayine kawai a tsakaninmu.
“Dukansu yan'uwna junane Halimatu kin sani, bayan yan'uwanta ta jini ma su tagwaye ni a ciki daya suka fito a rana daya kuma a mahaifa daya, mace daya ta raine su uba daya ya haife su, karki aikata abunda zai zame mana matsala ni da mahaifinki domin uwar data haifi mahaifinki ita ce ta haifi mahaifin Abdallah, mahaifin Abdallah da mahaifinki uwa daya uba daya suke karki lalata alaka Halimatu”
“Ban kira Abdallah na ce ya zo nan, zuwan Abdulhamid a yau ma bana da masaniya sai da na ganshi”
“Ba shi nake kokarin fahimtar da ke ba, ki sallami daya daga cikinsu saboda gudun abunda zai iya faruwa a gobenki, idan kuma dukansu ba ki ra'ayinsu to ki sallame su duka shi ya fi alheri Allah ya tsare a dawo lafiya”
Ya miko min ledar sannan ta mike tsaye ta fice ta bar a falon tsaye, ji nai kamar a san saka gatari an sare duk wata gaba ta kuzari da ke jikina. Kamar wata marar lakka haka na fito daga cikin gidan na nufi inda motarsa take na bude na shiga shi kuma ya tashi motar muka hau hanya.
“Ban jajanta miki kan abunda ya faru ba, na yi hakan ne saboda na baki lokaci ki huce bacin ranki, kuma bana son wata magana ta shiga tsakanina da ke a lokacin da kike idda, ko da ko gaisuwa ce, amman yanzu ina jin I'm free to name what ever i want daga gareki saboda kina da yanci”
Ban ce masa komai ba ina ta kokarin maida hankalina gurin titi amman na kasa, magaganun Mama sun tsaya min a kai.
“Ban jidadin abunda ya faru ba, Aminu kuma be yi miki hallaci ba amman mai hakuri yana tare da nasara, kuma kansa yai ma na san wata rana zai yi nadama ya gane cewar yayi kuskure a lokacin da ke din kin masa nisa”
Still ban ce masa kuma ba, hakan kuma be hana shi cigaba da magana ba.
“Jarabawa ce ta rayuwa, you know wani lokacin Allah yana jarraba bayinsa da abubuwa daban dabam, kamar yadda ya jarrabe ki da miji kamar Aminu ni kuma ya jarabe ni da cutar da na kasa samun maganinta har yanzu, wanda hakan yasa har bana son kawo tunanin aure a rayuwata....”
Juyowa nai na kalleshi a take zuciyata ta cika da tausayinsa.
“A da na sadakar na cire rai daga samun lafiya, kuma na aje duk wani abu na neman magani, amman daga lokacin da na ji cewar Aminu ya sake ki sai na nemi duk wannan abun na rasa, na ji cewar a yanzu ya dace na nemi magani kuma na nemi aurenki ko da ba za ki so ni ba, ba dan komai ba sai dan na faranta miki kuma na cika burina a kanki, ban sani ba ko akwai soyayyar Abdulhamid a zuciyar Halimatu ko a a, idan ma babu zan yi kokarin samawa idan kuma akwai sai na kafafata na ingantata”
Ya karasa daidai lokacin da ya faka motarsa a ma'aikatarmu sai ya zauna daidai yana dubana da fuskarsa ta tausayi.
“Na san za ki mamaki jin irin wannan maganar daga bakina kai tsaye kuma a karon farko da na ziyarce ki, daman abunda na ke son mu tattauna kenan a jiya, saboda ina son nai mata sha daya ne idan ma hadiye zuciya zan yi na mutu na san makomata idan kuma dama za ki ba ni nan ma na san makomata, ni dai har gobe ina son ki Halimatu kuma ina alakanta abunda Aminu yai miki da rashin aurenki da nai ta hanyar kin yarda da shawararki ta cewar na aureki na cigaba da neman magani za ki yi hakuri da ni a haka, ko kuma ki jira ni na nemi magani amman duka na ki yarda, na san da cewar Allah ta rubuto hakan zai faru amman komai yana da sila....”
Jimmm nai na dan wasu mintuna sannan na ya cigaba.
“Wata kila zuciyarki ta raya miki cewar na cika son kai a yanzu ko? Kina da gaskiya ba ko wace mace ce zata auri namiji irina ba, shiyasa ban gwada neman kowa ba sai ke ban taba saka son wata mace a raina ba sai ke kuma har gobe ke ce a raina Halimatu, zan iya baki damar yin shawara matukar kika ji za ki iya aurena a haka, ko kuma ki jira har na samu lafiya zan fi kowa farinciki, idan kuma kika ji ba za ki iya ba nan ma ba zan zarge ki ba.... ”
“Zan shiga office na gode”
Shine kawai abunda na fada na share hawayen da suka fara min zuba tun a lokacin daya fara maganar.......
Anya Halimatu zata iya zabe tsakanin dan'uwa da dan'uwa?
Anya zata iya zaba tsakanin mutuwa da rayuwa? Domin auren namiji irin Abdulhamid mutuwa da rayuwa ne.
A ganinku waya dace ta zaba?
Ina labarin Aminu ne?
Ko ya Kabir yake?
Shi kuma Abdallah haka yake da an bata masa rai sai kohi 🤣🤔
#TeamAminu
#TeamAbdulhami
#TeamAbdallah
#TeamHalimatu
#ZawarcinHalimatu
#Gobena
7/20/21, 8:30 AM - Buhainat: *GOBE NA...*
_My Tomorrow_
By Khadeeja Candy
1️⃣4️⃣