← Book details Gobe Na Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 13 OF 136

Sashe 13

Gobe Na Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

“A'a Uncle Abdallah yace ya daina bari kina yin nisa da ni duk inda kika je na biki ko da gurin aiki ne idan ba haka ba Baba Sadi zai iya zuwa ya yanke ni saboda na fada”

Kamin nai wata magana Adnan ya nufo inda mike da sauri yan zaro ido.

“Baba Sadi ne zai yanke ki? Mi kika fada”

“Ba komai, zo muje”

Hannunta naja ban bari ta sake cewa komai ba. Na nufi kitchen din da ita.

“A cikin gidan nan wani be isa ya zo ya taba ki ba, ke ba a nan ba ko a wani wajen ne wani be isa ya taba ki ba, ki kwantar da hankalinki kinji yar kirki”

Na fada mata ina kokarin zuba mata abincin, sai ta fara motsa ido.

“Mama ina jin tsoro”

“Ai Baba Sadi be san kin fadi wannan maganar ba, kuma ba fada masa zan yi ba dan haka ki kwantar da hankalinki kinji?”

Ta gyada min kai, a plate na zuba mata abincin sannan na janyo hannunta muka fito falo, zaunar ita nai ina kokarin bata abincin sai ta ce.

“Momy ban wanke baki ba”

“To je ki wanke”

Bata min musu ba ta tashi zuwa cikin dakinsu, daman can Namra ba yarinya ce mai kiriniya da jan magana ba, ko abu yake cinta yana da wahala ta iya fada ga ladabi da hankali kamar ita ce yayar Adnan, duk abunda na saka ta sai ta yi ba musu idan nace daina zata daina, ga jinkai duk abunda ta samu ita dai Momy dai Momy dai. Rashin ji da kiriniya sai Adnan shi da yake babba da Aiman dakr binta sai kuma wannan yar berar nan Amal ita kam fitinar ta tafi ta kowa ga barna komai ta dauka sai ta lalata.
  Wayata ce dake kan dinning tai kara, sai na aje plate din a kasa na tashi na nufi inda wayar take, number Abdallah ce har na yi kamar ba zan dauka ba idan sai kuma wata zuciya tace min na dauka wata kila wata maganar ce aka Namra.

“Assalamu Alaikum”

Na masa sallama da sanyayyiyar muryar da ke fassara irin damuwar dake tare da ni, domin bana da wani sauran kuzari a yanzu. Sai da yai shiru for few seconds sannan na amsa min.

“Wa'alaikissalam Halima ya jikin Namra na san ta farka yanzu ko?”

Na gyada kain kamar yana gabana, shi kuma kamar ya san abunda nai sai ya ce.

“Good ki yi hakuri na fada miki magana marar dadi dazun, rai na ne ya bace shiyasa, kuma dan Allah Halima karki saka damuwa a ranki, karki kamar ba zaki iya ba, kina da yan'uwan da zasu iya goya miki baya ki yi komai, karki bar Baba Sadi ya ci bulus”

“Zan aje wayar”

“Okay ki kula da kanki”

Sauke wayar nai ina ta tunanin ranar da Abdallah zai canja, wannan wa'azin ma yana min shi ne saboda ya san idan har na ce zan kwace hakkin yata dole aurena zai mutu, shi kuma abunda ya dade yana jira kenan tun kamin na haifi Namra, ya kwallafa min rai kullum burinsa da addu'arsa aurena dai ya mutu shiyasa yake yawan fada min maganganu marasa dadin ji akan Aminu, ko da yaushe yana fada min be kamata na zauna da shi ba.
Ni kuma ina daukar hakan da son zuciya da kuma son kai irin na bahaushen mutum, taya zaka kwallafawa ranka son matar aure matar wani? Saboda kawai kana da alaka da yan'uwantaka, wani lokacin har haukarsa nake gani domin mutun mai hankali da tunani ba zai yi abunda yake ba.
  Ina cikin wannan tunanin na ji an buga kofar falon.

“Shigo”

Na fada domin na san kofar a bude take ban saka mata key ba. Hajara ce ta turo kofar falon ta shigo tana dauke da Amal sai dariya take bakina har kunne, rayuwarta na burni ne ita kan ta yi dacen aure ba kamar ni ba, abu mai wahala ka ganta a cikin damuwa duk wani abun da take bukata a take mijinta yake mata shi sai idan ba shi da hali.

“Ga yarki nan ta ishe ni da kuka daga kawai na taimaka na je da ita biki, sai ka ce na sato ta”

Na mika hannu na karbe ta sai ta ki zuwa sai ita fushi take tana turo baki.

“Yi hakuri Amal kyale Mama Hajara mun bata da ita har da tufafin Afrah aka saka miki iyeee yarinyata ta yi gayu”

Daker ta zo gareni shi ma da kuka, sai na rungume ta ina dariya. Sai dariyar da nake bata hana kawata kuma aminiyata fahimtar ina cikin damuwa ba.

“Halima kamar akwai damuwa ko?”

Dagowa nai na kalleta kamin na ce wani abun Namra ta fito daga dakinsu ta nufo inda nake.

“Momy ina abinci Maman su Salma ina wuni”

Hajara ta amsa mata ni kuma na fada mata inda tuwon yake.

“Ina cikin damuwa Hajara, damuwar da ta fi ta ko da yaushe kuma damuwar da zata dauwama a zuciyata har abada, ko da kuwa yan hukunta Sadi, ban taba jin na tsani Aminu ba sa yanzu, ban taba dana sanin auren Aminu ba sai yanzu, ban taba jin natsani rayuwa ba sai yanzu, ban taba mafarkin ko jin ina son mutuwa a kusa da ni ba kamar yau, Wallahi Hajara ji nake kamar na sha wani abu na mutu na huta, ina ma Allah be hallice ni ba da duk wannan rayuwar ban ganta ba, ita ba bata gan ni ba, da Aminu be aureni ba”

Da hawaye na ke maganar hawayen da ban yi zaton akwai sauransu ba. Cike da tashin hankali take kallona.

“Innalillahi wa'inna ilaihirraji'u, Halima me ya same ki haka?”

Ban boye mata komai ba, tun daga zubin farko na fada mata komai ina kuka, ita ma fashewa tai ya kuka ta saka hannunta biyu ta dafe kanta.

“Innalillahi wa'inna ilaihirraji'u, Allah ka tsayar mana wannan abun a nan”

Sannan ta dago ta kalleni.

“Ban taba ji uba kamar Aminu ba, taya za ayi ma yarka fyade kuma ka tsaya karyatawa, ai ko ubanka aka ce yayi ma yarka fyade ba zaka karyata ba saboda duniyar yanzu ta lalace, ammn ke yake dorawa laifin? Da ya tsaya ya kula da iyalinsa yadda ya kamata kuma ya tsare mutuncin kansa hakan zai faru ne? Ban taba goyon bayan ki yi ma Aminu komai ba ban taba goyon bayan ki kashe aurenki ba, a kullum ina cikin addu'ar Allah ya karkato miki da mijinki gareki, amman yau kam ba zan goyi bayan ki bar wannan maganar ba, gobe zan je nai magana da Mama zan fahimtar da su abunda kika kasa fahimta, kuma zan tsayawa Namra sai inda karfina ya kare saki ne dai ko? Aminu ya sake ki Abban Afrah zai aureki In-Sha-Allah, ko kin yi lalacewar da kika rasa mijin aure ba zaki rasa nawa ba”

Kallon yar'uwa nake mata ba kawa ko aminiya ba, na san a yadda Hajara ta dauke ni da kuma yadda yake jina zata iya min komai, ko da bana raye balle yanzu da take ganin idona. Sai dai na san abunda ta fada ta fada ne kawai a yanzu saboda ranta a bace yanke, domin ba wata macen da zata yarda mijinta ya auro mata kawarta da amincewarta. Hannuna na kai ya rika hannunta.

“Na gode Hajara kin karfafa min guiwa sosai”

“Wannan abun yayi yawa Halima Aminu yai miki yan'uwansa su rika ganin laifinki kina ganin kin maye komai na dan'uwansu sun dauki kiyayya sun dora miki, yanzu kuma abun ya wuce kanki ya koma har akan yaranki? Ace Kanen mijinki ya kai yana lalata da yaranki? Miyasa be yi da nasa ba sai na ki? Ko naki ne kawai yayan dan'uwansa, kai wannan tashin hankali da me nai kama? Kina cikin jarabawar aure kuma wani ya karo fado miki? Allah ya miki mafita Halima”

“Ameen”

Mun dade muna ta fira da ita tana ta kwantar min da hankali sannan ta tashi na rak har gurin gate ta wuce gidanta ni kuma na dawo cikin. Ina shigowa na shiga kitchen na debowa su Adnan na su tuwon na kawo musu sannan na dauko maganin Namra da ruwa na soma bata. Ina jin lokacin da mota ta tsaya da karfi har na daga labulen windows na leka waje sai na hango Hajiya tare da yayata mata uku wato mahaifiyar Aminu ce da kenensa. Ban ji komai a raina ba domin a yanzu zuciyata a dake kuma na san zuwan nata baya rasa nasaba da fadan da mukai da Aminu a waya dazun wata kila ya fada mata ne. Ashe kuwa na canka a dai dai domin ta shigo falon babu ko sallama tana shigowa cikin falon ta hau fadin.

“Halima mi kika fadawa Aminu a waya?”

Juyowa nai na kalleta na saba sauka na risina har masa na gaisheta idan ta zo gidan ko ni aje ko muka hadu da juna, sai dai yau bana jin zan iya yin haka.

“Hajiya sannu da zuwa”

“Ba sannu da zuwanki na ke so ba, wata magana na ji nake son ki sake maimaita min da bakinki”

“Indai har Aminu ya fada miki, to ba bukatar na sake maimaita miki, iya kar abunda ya kamata ki gane shine ba zan yi ma Sadi kazafi ba haka nan kawai”

“Kazafi ne mana, ai kin dade kina son raba kan gidan nan, kin rasa abunda za ki yi shine kika fake da wannan waya sani ko can gurin aikin naki kika kai yarinya aka lalata sai kuma ki zo ki fake da Sadi, wai ko baki san cewar ni na haifi Sadi ba? Kuma ni din mahaifiyar Aminu ce uba daya ya haife su nono daya suka sha”

“Ko tagwaye ne su Hajiya be dame ni ba, yayanki kike tsaye a nan kina karewa ni kuma na san zafin haihuwa kuma na san zafin keta haddi saboda ni ma mace ce”

Zakiya ta matso kusa da ni tana min tsawa.

“Halima karki ce zaki ma Hajiya rashin kunya Wallahi na ci mutuncin ki”

Ni kuma na mike tsaye ina nuna ga da yatsa a fusace.
Chapter 13 · 0% Book details