Sashe 102
Gobe Na Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ya amsa sannan ya juya ya fice, yadda Ahmad yake masa maganar kai ka rantse da Allah be san Yunus din ba aiki ne kawai ya hada su, domin yana masa magana ne ta sigar yaro da ubangidansa babu alamar murmushi ko wasa a duka Maganarsa, bayan kuma shi Yunus din ya fada min cewar Ahmad din childhood friend dinsa ne kuma kaf a kamfanin ba shi da aboki irinsa, saboda ya yarda da shi 100%
Haka Ahmad ya zaunar da ni a office din for more than 3 hours, ba dan na masa aikin komai ba, after every 30 minutes sai yaje gurin windows dinsa ya leko sannan ya dawo ya zauna wata kila Yunus din yana can yana aikin ne tun da ya riga ya fara.
Ban san abunda ya zo masa a rai ba sai ganin nai yana kallona yana murmushi.
“I know zaki ce ni din ai ba muharraminki ba ne ko? Yes amman ni ina da karfin jini the way da zan iya controlling kaina akan wasu maganganu ko aikata wani abun ba, ba kowa zai iya haka ba, and ita mace komai shekarunta komai girmanta sai ana controlling dinta saboda karamar kwakwalwa ne da su, more especially Lims”
Ya fada still smile, ni dai ban da idon da na sakar masa babu abunda na ce, har na fara tunanin to ko dai Yunus din dan iska ne?
“Dauko lemu ki sha”
Ya fada yana dora duka kafafuwansa saman katon tebur din, tare da kai yatsansa jikin dogon hancinsa.
“No Na gode”
Sai ya dan tabe baki.
“Kamar kin ji haushi ko? Ke ana tausayinki kin gagara ganewa, by the way likitocin da suke uduth sun bada shawarar a fitar da Kabir india saboda a can ne za a iya masa aiki mai kyau a kwashe jinin daya kwanta a cikin kwakwalwarsa, sun ce bashi magani zai dauki lokaci mai tsawo kamin ya samu lafiya kuma za a kashe kudi sosai, amman idan an masa aikin kuma aka yi a sa'a zai iya samun sauki cikin kankanen lokaci”
“Ba za a iya yi masa a nan ba? Zuwa india ai za a kashe kudi da yawa”
“To ke zaki kashe kudin ne? Ko kudin a aljihunki za su fito? Ko kuma kudin na ki ne? Are you the money or the money is yours? Ke kin fiye son shiga uku”
Ya fada yana mikewa tsaye ya nufi fridge din ya bude ya dauko lemun ya nufo inda nake.
“Already na fada musu su shirya komai daya kamata, kawai dai na fada miki ne just to let you know”
Ya miko min lemun, karba nai da mamaki a fuskata haka yake wani lokacin, daga abun arziki ina tausayin kudin da zai kashe sai ya ce min wai ba ni ce kudin ba, and look at him now kamar ba shi ne ya gama hade fuska dazun ba, sometimes yana abu kamar wani mai aljanu.
“Kamar mai aljannu ko?”
Jin ya fadi haka yana murmushi yasa nai saurin mikewa tsaye ina girgiza kai, a zatona a fili nai maganar har ya ji.
“No mai Al.... Jifai nake nufi....”
Na fada da sauri sai yai dariyar da ta bayyana hakoransa.
“Ashe na canka daidai yadda naga kin rike lemun daman na san gulma kike a zuciyarki ki ce wannan mutume kamar mai aljanu”
Nima dariyar nai sosai har idona ya cika da kwala ashe ma ba a fili nai maganar ba, canka yai ni kuma garin kare kaina sai na fallasa kaina. Murmushi yake yana kallon yadda nake dariya kamar ba ni ba.
“Cute you, dariya na miki kyau”
Daidaita natsuwata nai, na koma na zauna na rike lemun.
“Tashi muje mu ci abinci”
“No ana kawo min abinci a office everyday”
“Ba zaki koma office din nan ba sai gobe that's final”
Hannunsa ya kai ya dauki keys din dake saman tebur din.
“Amman handbag dina tana office din”
Sai ya miko min keys din.
“Je ki jirani a mota”
Ba musu na karba keys din na juya na fice daga office din, na san inda yake aje motarsa dan haka na nufi gurin kai tsaye na tsaya a gurin ina jiransa, be jima ba ya fito tare da wata mata wacce rike da jakata ta kawo min jakar shi kuma ya karbi keys din ya bude motar ni ma na bude na shiga front seat. Tun da ya kama hanyar restaurant din be ce min uffan ba sai dai lokaci zuwa lokaci yana kallon inda nake, ni ma kuma ban ce masa komai ba, zuciyata nata raya min abubuwa da dama har muka isa gurin.
Motar na tsayawa na bude na fito shi ma ya fito yai gaba ina binsa a baya, restaurant din da Abdulhamid ya taba cewa na tsaya a ciki na jira shi ce, wacce na shiga ciki na zauna a kujerar da Ahmad din ya rufeni da masifa saboda na zaunarna kujerar da ban san ta wacece ba a gurinsa.
A yau ciki muka shiga har vip din inda set din yake, da kansa yaja min kujerar, sai na kasa zama kuma na gagara cewa komai and na kasa dauke idona akansa, gabana sai bugawa yake da sauri kamar zai fito.
“Zauna mana”
Ya fada so calmly yana min wani irin kallo da na kasa natsuwa. Na zauna kamar yadda ya umarce ni amman kamar wata karago haka na zama, idan zan juya gaba daya zan juya idan zan juyo gaba daya zan juyo, kana kallo kasan bana cikin natsuwa ba kuma natsuwa irin ta wanda yake cikin tashin hankali ko zullumi ba ko fargaba ba, no natsuwa dai irin ta Wanda yake ganin wani abu kamar a mafarki.
“Me za a kawo miki?”
“Just water”
Na fada ina kallon waiter din.
“Kawo mana Jalof plate biyu da lemu”
Ya fada masa sannan ya kalli.
“Is hardly na ci abinci a public place like this, bana cin abinci a awaje yawanci Hajiya ta ke girka min, sai dai ina yawan zuwa gurin nan tare da mahaifiyar Baby lokacin da take raye just to make her happy, saboda ta saba zuwa gurin tun tana budurwa, a yau ma na san sai Hajiya tace min miyasa ban ci abinci a gida ba, kuma saboda ke ne, na zamu so nan ace me zaki ci ki ce ruwa ba, you must eat with me”
Magana yake min a hankali kamar mai kokarin fahimtar da ni. Wani abu nake hangowa a idonsa wanda nake kokarin karyata kaina kansa. Ba shiri na mike tsaye ya dauki jakata na rataya.
“I don't think i deserve this, ya kamata ka cigaba da mutunta kujerar matarka”
Ina fadar hakan ban tsaya komai na na nufi hanyar sauka daga gurin har ina sauri kamar zan fadi. Ina fitowa gurin na tari napep na shiga, hawaye suka fara sauko min, tsoro nake ji kamar Ahmad ya bijiro min da abunda Aminu, Abdulhamid, Abdallah, Abraham suka bijiro min da shi, idan ya tambayi so a gurina na amsa masa da a a ban kyauta ba, sai dai ni ban shirya ba, na gaji da halin maza, ba zan sake aikata kurskuren auren mutunen da zan yi kuka a karkashin igiyar aurensa ba.
Idan na tuna Aminu da Abdulhamid duk haka suka min kamin daga baya su saka ni dakin kuka su juya min baya, babu muhallin kowa a zuciyata a yanzu, idan har akwai wanda ya cancance ni a yanzu Abdallah ne, ba kowa ba, ba zan yarda Ahmad ya yaudare ni na fada soyayyarsa, a yanayin gidansu da irin girman da suke da shi, ba lallai ne idan ya aure ni ya ga kima ta ba, domin mu talakawa ne masu rufin asiri ba masu arziki ba, idan har mahaifiyar Aminu zata raina talaucin mu ya zama silar da ya saka ta kara wulakanta ni tana cewa ina kwashe arzikin danta ina kaiwa gidanmu ina ga mahaifiyar Ahmad?
Secondly idan Abdulhamid be iya hakuri da ni ya zauna da ni a gidansa da aka min fyade ba taya wani zan ji labarina da rana tsaya kuma yace zai hadiye ƙashi ya zauna da ni babu kyama? Shin idan ma na yarda wata kadarar ta sake samun a gidansa zai iya zama da ni ko kuwa shi ma juya min baya zai yi? No I'm not just ready.
Mai napep na isa kofar gidanmu sakon kar ta kwana na shigowa wayata daga number Ahmad.
“Miyasa kika ce baki cancanci haka ba? Miyasa kika tafi kika barni? Why kike jin tsoro? Mi zuciyarki ta raya miki a kaina?”
“Nothing, you're just my friend”
Ita ce amsa da na bashi bayan na karanta sakon, sannan na share hawayena na fita daga napep din.
“No I'm not just your friend”
“I'm not”
Ita ce amsar da ya maido min a take. Sai kawai na goge sakon, na sallame mai napep na shige gida, kallo daya Mama tai min ta fahimci damuwa, tai ta min tambayoyi a gurin aikinki ne ko a Abraham din ne domin na dade da labarta mata komai akansa, sai kawai na ce mata babu komai.
Misalin tara da wani abu na dare, Aminu ya kira wayata, rabon da na ga kiransa a wayata har na manta, kusan tun da Ahmad ya saka aka mai masa duka be sake zuwa ba ko kirana ko da da sunan duba yaransa ne. Ba tare da tunanin komai ba na dauki kiran, sai ya sanar min yana kofar gida dan Allah na fito magana zai yi da ni.
Tashi nai na jari hijabina na saka na fadawa Inna wacce nake zaune a dakinta sannan na fita wajen, kusa da kofar gida na same shi zaune a cikin motarsa da ke fake. Tsaye nai jikin motar na ce.
“Gani”
“Ki shigo ciki dan Allah”
“Duk abunda zaka fada ka fada a nan”
“Maganar da zan yi tana da muhimmanci dan Allah ki taimaka ki shigo”
Haka Ahmad ya zaunar da ni a office din for more than 3 hours, ba dan na masa aikin komai ba, after every 30 minutes sai yaje gurin windows dinsa ya leko sannan ya dawo ya zauna wata kila Yunus din yana can yana aikin ne tun da ya riga ya fara.
Ban san abunda ya zo masa a rai ba sai ganin nai yana kallona yana murmushi.
“I know zaki ce ni din ai ba muharraminki ba ne ko? Yes amman ni ina da karfin jini the way da zan iya controlling kaina akan wasu maganganu ko aikata wani abun ba, ba kowa zai iya haka ba, and ita mace komai shekarunta komai girmanta sai ana controlling dinta saboda karamar kwakwalwa ne da su, more especially Lims”
Ya fada still smile, ni dai ban da idon da na sakar masa babu abunda na ce, har na fara tunanin to ko dai Yunus din dan iska ne?
“Dauko lemu ki sha”
Ya fada yana dora duka kafafuwansa saman katon tebur din, tare da kai yatsansa jikin dogon hancinsa.
“No Na gode”
Sai ya dan tabe baki.
“Kamar kin ji haushi ko? Ke ana tausayinki kin gagara ganewa, by the way likitocin da suke uduth sun bada shawarar a fitar da Kabir india saboda a can ne za a iya masa aiki mai kyau a kwashe jinin daya kwanta a cikin kwakwalwarsa, sun ce bashi magani zai dauki lokaci mai tsawo kamin ya samu lafiya kuma za a kashe kudi sosai, amman idan an masa aikin kuma aka yi a sa'a zai iya samun sauki cikin kankanen lokaci”
“Ba za a iya yi masa a nan ba? Zuwa india ai za a kashe kudi da yawa”
“To ke zaki kashe kudin ne? Ko kudin a aljihunki za su fito? Ko kuma kudin na ki ne? Are you the money or the money is yours? Ke kin fiye son shiga uku”
Ya fada yana mikewa tsaye ya nufi fridge din ya bude ya dauko lemun ya nufo inda nake.
“Already na fada musu su shirya komai daya kamata, kawai dai na fada miki ne just to let you know”
Ya miko min lemun, karba nai da mamaki a fuskata haka yake wani lokacin, daga abun arziki ina tausayin kudin da zai kashe sai ya ce min wai ba ni ce kudin ba, and look at him now kamar ba shi ne ya gama hade fuska dazun ba, sometimes yana abu kamar wani mai aljanu.
“Kamar mai aljannu ko?”
Jin ya fadi haka yana murmushi yasa nai saurin mikewa tsaye ina girgiza kai, a zatona a fili nai maganar har ya ji.
“No mai Al.... Jifai nake nufi....”
Na fada da sauri sai yai dariyar da ta bayyana hakoransa.
“Ashe na canka daidai yadda naga kin rike lemun daman na san gulma kike a zuciyarki ki ce wannan mutume kamar mai aljanu”
Nima dariyar nai sosai har idona ya cika da kwala ashe ma ba a fili nai maganar ba, canka yai ni kuma garin kare kaina sai na fallasa kaina. Murmushi yake yana kallon yadda nake dariya kamar ba ni ba.
“Cute you, dariya na miki kyau”
Daidaita natsuwata nai, na koma na zauna na rike lemun.
“Tashi muje mu ci abinci”
“No ana kawo min abinci a office everyday”
“Ba zaki koma office din nan ba sai gobe that's final”
Hannunsa ya kai ya dauki keys din dake saman tebur din.
“Amman handbag dina tana office din”
Sai ya miko min keys din.
“Je ki jirani a mota”
Ba musu na karba keys din na juya na fice daga office din, na san inda yake aje motarsa dan haka na nufi gurin kai tsaye na tsaya a gurin ina jiransa, be jima ba ya fito tare da wata mata wacce rike da jakata ta kawo min jakar shi kuma ya karbi keys din ya bude motar ni ma na bude na shiga front seat. Tun da ya kama hanyar restaurant din be ce min uffan ba sai dai lokaci zuwa lokaci yana kallon inda nake, ni ma kuma ban ce masa komai ba, zuciyata nata raya min abubuwa da dama har muka isa gurin.
Motar na tsayawa na bude na fito shi ma ya fito yai gaba ina binsa a baya, restaurant din da Abdulhamid ya taba cewa na tsaya a ciki na jira shi ce, wacce na shiga ciki na zauna a kujerar da Ahmad din ya rufeni da masifa saboda na zaunarna kujerar da ban san ta wacece ba a gurinsa.
A yau ciki muka shiga har vip din inda set din yake, da kansa yaja min kujerar, sai na kasa zama kuma na gagara cewa komai and na kasa dauke idona akansa, gabana sai bugawa yake da sauri kamar zai fito.
“Zauna mana”
Ya fada so calmly yana min wani irin kallo da na kasa natsuwa. Na zauna kamar yadda ya umarce ni amman kamar wata karago haka na zama, idan zan juya gaba daya zan juya idan zan juyo gaba daya zan juyo, kana kallo kasan bana cikin natsuwa ba kuma natsuwa irin ta wanda yake cikin tashin hankali ko zullumi ba ko fargaba ba, no natsuwa dai irin ta Wanda yake ganin wani abu kamar a mafarki.
“Me za a kawo miki?”
“Just water”
Na fada ina kallon waiter din.
“Kawo mana Jalof plate biyu da lemu”
Ya fada masa sannan ya kalli.
“Is hardly na ci abinci a public place like this, bana cin abinci a awaje yawanci Hajiya ta ke girka min, sai dai ina yawan zuwa gurin nan tare da mahaifiyar Baby lokacin da take raye just to make her happy, saboda ta saba zuwa gurin tun tana budurwa, a yau ma na san sai Hajiya tace min miyasa ban ci abinci a gida ba, kuma saboda ke ne, na zamu so nan ace me zaki ci ki ce ruwa ba, you must eat with me”
Magana yake min a hankali kamar mai kokarin fahimtar da ni. Wani abu nake hangowa a idonsa wanda nake kokarin karyata kaina kansa. Ba shiri na mike tsaye ya dauki jakata na rataya.
“I don't think i deserve this, ya kamata ka cigaba da mutunta kujerar matarka”
Ina fadar hakan ban tsaya komai na na nufi hanyar sauka daga gurin har ina sauri kamar zan fadi. Ina fitowa gurin na tari napep na shiga, hawaye suka fara sauko min, tsoro nake ji kamar Ahmad ya bijiro min da abunda Aminu, Abdulhamid, Abdallah, Abraham suka bijiro min da shi, idan ya tambayi so a gurina na amsa masa da a a ban kyauta ba, sai dai ni ban shirya ba, na gaji da halin maza, ba zan sake aikata kurskuren auren mutunen da zan yi kuka a karkashin igiyar aurensa ba.
Idan na tuna Aminu da Abdulhamid duk haka suka min kamin daga baya su saka ni dakin kuka su juya min baya, babu muhallin kowa a zuciyata a yanzu, idan har akwai wanda ya cancance ni a yanzu Abdallah ne, ba kowa ba, ba zan yarda Ahmad ya yaudare ni na fada soyayyarsa, a yanayin gidansu da irin girman da suke da shi, ba lallai ne idan ya aure ni ya ga kima ta ba, domin mu talakawa ne masu rufin asiri ba masu arziki ba, idan har mahaifiyar Aminu zata raina talaucin mu ya zama silar da ya saka ta kara wulakanta ni tana cewa ina kwashe arzikin danta ina kaiwa gidanmu ina ga mahaifiyar Ahmad?
Secondly idan Abdulhamid be iya hakuri da ni ya zauna da ni a gidansa da aka min fyade ba taya wani zan ji labarina da rana tsaya kuma yace zai hadiye ƙashi ya zauna da ni babu kyama? Shin idan ma na yarda wata kadarar ta sake samun a gidansa zai iya zama da ni ko kuwa shi ma juya min baya zai yi? No I'm not just ready.
Mai napep na isa kofar gidanmu sakon kar ta kwana na shigowa wayata daga number Ahmad.
“Miyasa kika ce baki cancanci haka ba? Miyasa kika tafi kika barni? Why kike jin tsoro? Mi zuciyarki ta raya miki a kaina?”
“Nothing, you're just my friend”
Ita ce amsa da na bashi bayan na karanta sakon, sannan na share hawayena na fita daga napep din.
“No I'm not just your friend”
“I'm not”
Ita ce amsar da ya maido min a take. Sai kawai na goge sakon, na sallame mai napep na shige gida, kallo daya Mama tai min ta fahimci damuwa, tai ta min tambayoyi a gurin aikinki ne ko a Abraham din ne domin na dade da labarta mata komai akansa, sai kawai na ce mata babu komai.
Misalin tara da wani abu na dare, Aminu ya kira wayata, rabon da na ga kiransa a wayata har na manta, kusan tun da Ahmad ya saka aka mai masa duka be sake zuwa ba ko kirana ko da da sunan duba yaransa ne. Ba tare da tunanin komai ba na dauki kiran, sai ya sanar min yana kofar gida dan Allah na fito magana zai yi da ni.
Tashi nai na jari hijabina na saka na fadawa Inna wacce nake zaune a dakinta sannan na fita wajen, kusa da kofar gida na same shi zaune a cikin motarsa da ke fake. Tsaye nai jikin motar na ce.
“Gani”
“Ki shigo ciki dan Allah”
“Duk abunda zaka fada ka fada a nan”
“Maganar da zan yi tana da muhimmanci dan Allah ki taimaka ki shigo”