Sashe 132
Gobe Na Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
“Na sani ni dai ki saka mu a addu'a, kin ga Inna da Mama da yan unguwa ai ba su san wannan ba, yan mata hudu a gida, Yaya nata aure tana barinsu ina lafiya, yan kanennan na mu ma sai taso suke za su cin mana a tsawo”
Ban yi mamaki na san indai Hafiza ce zata fadi fiye da haka ma, da dai ace Aisha ce ko Husna take maganar da ce ina kunyarsu amman Hafiza sai gyaran Allah ba kunya ba tsoro kuma bata jiran sai an mata.
Ko ba a fada na ni an san wasu dan gulma da neman ganin gidan da za a kaini yasa sun bin motocin daukar amarya tun da a budurwa nake ba balle ace dole sai kowa yaje, amman Al-hamdulillah shi ma farinciki ne kuma na san ba za su je su tarardar wani abin tsegumi ba, sai dai kowa ya bawa idonsa abinci.
Ni kaina da na already na ga gidan kamin a kawo ni amman hakan be hana ni zama bakauya ba a birnin, wata kila kuma dan yana dare ne sai ko'ina da gidan ya dauki haske ga shuke shuken da suka kara kawata gidan gwanin sha'awa.
Bangaren mahaifiyarsa aka fara shiga da ni Gwaggota na rike da hannuna kaina na cikin gyale jikina sanye da shadda lace mai ruwa kwai, sai kamshin turare nake kamar yadda muka shiga muka tarardar falon Hajiya ma yana kamshin turaren wuta. Muna shiga matan dake cikin falon suka fara guda kamar an aurowa dansu burduwa, sai saka min albarka suke yan matan na daukata hoto, har cikin dakin Hajiya aka shiga da ni tai min nasiha sannan na taso tare da mutanen da muke tare aka nufi bangare na da ni.
Mutane da yawa sun yaba da yadda aka samu part dina so Ma-sha-Allah, ciki har da masu fadin mai hakuri mawadaci, basu dade ba suka fita har su Hafiza aka bar ni kadai a dakin ta cikin a nan na yaye gyalena ina kara kallon yadda kalle da aka min ja yake ta haiba.
Few people ne suka raso Ahnad zuwa dakina, a yadda suke zolayarsa yai musu shiru yana murmushi sai ka rantse da Allah ba shi ba ne, sai wani sun sun yake da kai kamar mai kunyar gaske.
Suma sun mana nasiha irin tasu sannan sukai mana addu'a, sai da ya raka su ya dawo, sai ya zauna kusa da ni ya cire min mayafin yana murmushi kamar yadda nima nake tsakanin fuskata da tasa sai na rasa wacce ta fi wata annuri, hannuna ya kama ta sumbata sannan yaja ni jikinsa ya rumgume.
“Al-hamdulillah, a yau Allah ya tabbatar mana da abunda ba mu taba mafarki ba, abunda ba mu taba kawowa a rai cewar zai faru ba a tsarim rayuwarmu, nesa ta zame mana kusa kunci da bakinciki ya zame mana farinciki da nishadi, ina rokon Allah yasa mutuwa ce zata raba mu kuma ya bamu zuri'ar mai kyau mai albarka, kuma ya bamu ikon kula da su da dauke sauke nauyinsu da yake kan mu”
“Amin”
Na fada ina wasa da zanen shaddar dake jikinsa, ji yai kamar rumgumar da yai min ba tai ba sai ya kara matseni sosai ya kirjinsa.
“Wallahi gani nake kamar ba gaske ne ba, Al-hamdulillah Allah”
Ya sake fada cike da nishadin, sallah godiya ga Ubangijince farkon abunda muka fara gabatarwa sannan neman tsarin Allah da kuma ni'imarsa ya biyo baya, muka ci daga abunda ya shigo min da shi, kana ya zuba min madara na sha sannan muka sake dabbaka wata sunnar.
Washe gari tun kamin mu tashi bachi Siyama da kwankwaso mana kofa, ina jin lokacin da ya daga ni a hankali saman kirjinsa ya kwantar da ni, ya gyara min duvet din sannan ya sumbace ni ya tashi ya fita. Be dade ba ya dawo ya sake jana kirjinsa ya rungume ba mu tashi ba sai kusan tara har da wani abu, shi ma dan Hafiza ta kira ni ta fada min cewar akwai yan'uwan Inna da za su zo yanzu.
A lokacin ne na tashi nai wanka na fito na tafi gaban madubi na shirya ina kokarin mikewa tsaye na hango shi ta cikin madubin yana kallon jikinsa ba riga sai tawul din daya daura shima iya kwankwasonsa. Murmushi nai na juyo ina kallonsa.
“Kawai gani nake kamar ba gaske ba ne”
Na sake yin murmushin sannan na nufi wardrobe a zatona kayan da nace Hafiza ta dauko min yana ciki sai nai arba da wasu tufafin dabam a ciki juyowa nai na kalleshi.
“Nawa ne?”
“Eh mana, daman ai ba zan kai miki gida ki yi kwalliya wani ya gani ba, ni da na siya ni za ayi wa kwalliya da su”
Bayan ya fadi haka ya karaso kusa da ni ya dafa ni yana min inda aka jera takalmin, akwai kayan da ba a dinke ba sai dai dikaken yafi yawa kuma kowane kaya da kalar hijabinsa babu gyale ko daya, gyale kan sai na abayar da aka saka a ciki amman bayan shi ban san wani mayafi mai suna veil a cikin kayan ba. Ko ba a fada min ba ni kaina a fahimci Ahmad mutum ne mai kishi hijabin kuma zai taimaka min na kara kare martabata da kuma mutuncin aure da kuma abunda Ahmad yake cewa na boye masa wai na sa shi kadai.
Sati daya Hajiya ta dauka tana mana girki na safe na rana na dare bata taba gajiyawa ba, sai da akai satin daya sannan ta sa aka kirani ita da kanta ta zaunar da ni falonta ta fada min cewar daga gobe zan fara girkawa mijina abinci da kaina.
“A ka'ida kwana uku ake, amman saboda ki huta yasa na dauki sati daya ina miki, yawancin duk abunda kika ga ina girka muku shine favorite din mijinki, dan haka sai ki haddace wani abun kuma za ki iya karawa dan kanki ko kuma ki saffara masa wani abun irin naku na yan zamani”
“In-Sha-Allah Hajiya na gode sosai Allah ya saka da alheri ya kara miki lafiya”
“Amin Allah ya muku albarka ku ma”
A nan na amsa da Amin, sannan na tashi na dawo part dina raina fes. Zaunawa nai saman kujerar da yake zaune sai ya dago ya kalleni sannan yasa hannunsa ya zagaye mazaunena.
“Hajiya tace zan fara maka girki daga gobe”
Na fada ina jan hancinsa dayan hannuna kuma a kunnensa ina wasa da shi. Lumshe ido yai ya bude yana tsutsar lips dinsa.
“Kin iya?”
Na dan yi fuskar shagwaba.
“Haba shi girkin?”
“Eh mana wasu yara irinki ba a koya musu girki a gida saboda son jiki”
Dariya nai sai ya kamo kaina ya hade goshinsa da nawa, ya sumbanci hancina yana isar min da numfashinsa.
“Idan baka kiya ba zan iya saka ki catering school ki koya mana”
“No ni din eh to ban hana ko dan koyan wadansu abubuwan ba na zamani amman indan girki ne irin na mu na hausa ai na saba yi na iya daidai gwargwado”
Mikewa tai tsaye ya ja hannuna muka nufi kitchen, gaban gas ya fara tsayar da ni sai ya koma bayana ya rumgume ni, da dayan hannuna ya rika nuna min yadda zan yi amfani da gas din.
“Na fa iya”
Bakinsa ya kai saitin kunnen yana cizona a hankali yace.
“Ki dauka baki taba aure ba sai yanzu, ki dauka wannan auren shi ne aurenki na fari, ki dauka komai sai a yanzu ne za ki koya sai a yanzu zaki iya, ki dauka Ahmad ne mijinki na farko kuma na karshe har abada”
Na gyada kai a hankali ina dan matse fuska domin maganar yake yana cizon kunne a hankali kamshin turarensa duk ya cika ni sai tayar min da zuciya yake.
“Okay”
“That's my Lims”
A dolen dole na biye masa ya rika nuna komai na kitchen din da yadda ake amfani da shi, wani abu kan ban san shi ba sai da ya fada min sauran kam duk na sansu kuma na saba amfani da su, domin ko a gidan Aminu da gas nake aiki balle kuma Abdulhamid.
Bayan mun gama muka fito daga kitchen din sai ya sake ni ya shiga ciki yai alwala, ina zaune ya fito yana sake hannayen rigarsa dake nade.
“Tashi ki yi alwala zanje masallaci”
Ya fada yana kissing dina, a kokarin yi masa addu'ar Allah ya tsare na ji lemun da na sha dazun ya dawo min a baki, saurin mikewa nai tsaye sai ya rike ni.
“Lafiya?”
Karnin turarensa yasa na fara sheka amai a gurin kamar wacce ta fi wani abu, sakina yai sai yai baya baya yana kallona baki sake kamar mai mamaki sai kuma ya rugo a guje yazo ya rumgume yana murmushi sai kuma ya sake ni.
“No wait....”
Sai kuma ya sake rumgume ni ya sake sakin ya sake rumgume ni yayi min haka yafi a kirga sai dariya yake. Can ya cire hular kansa ya jefar ya fara zagaya falon yana kallona kamar mai mafarki, sai kuma ya nufo ni ya daga fuskata yana kallona
“I can't believe this”
Ya fada kamin ya sake ni ya fadi a gurin yana ma Allah Sujada. Ni kan a raina nace daga ganin na yi amai idan kuma ya kasance malaria ce fa? Domin ni ban saba ciki da amai tun yana yaro ba sai ya fara girma hasalima ko irin laulayin nan na masu yaron ciki ban saba yi a ba sai ya fara fitowa na ke cin wuya har sai na raina kaina.
7/28/21, 8:33 PM - Buhainat: *GOBE NA...*
By Khadeeja Candy
6️⃣4️⃣
Ban yi mamaki na san indai Hafiza ce zata fadi fiye da haka ma, da dai ace Aisha ce ko Husna take maganar da ce ina kunyarsu amman Hafiza sai gyaran Allah ba kunya ba tsoro kuma bata jiran sai an mata.
Ko ba a fada na ni an san wasu dan gulma da neman ganin gidan da za a kaini yasa sun bin motocin daukar amarya tun da a budurwa nake ba balle ace dole sai kowa yaje, amman Al-hamdulillah shi ma farinciki ne kuma na san ba za su je su tarardar wani abin tsegumi ba, sai dai kowa ya bawa idonsa abinci.
Ni kaina da na already na ga gidan kamin a kawo ni amman hakan be hana ni zama bakauya ba a birnin, wata kila kuma dan yana dare ne sai ko'ina da gidan ya dauki haske ga shuke shuken da suka kara kawata gidan gwanin sha'awa.
Bangaren mahaifiyarsa aka fara shiga da ni Gwaggota na rike da hannuna kaina na cikin gyale jikina sanye da shadda lace mai ruwa kwai, sai kamshin turare nake kamar yadda muka shiga muka tarardar falon Hajiya ma yana kamshin turaren wuta. Muna shiga matan dake cikin falon suka fara guda kamar an aurowa dansu burduwa, sai saka min albarka suke yan matan na daukata hoto, har cikin dakin Hajiya aka shiga da ni tai min nasiha sannan na taso tare da mutanen da muke tare aka nufi bangare na da ni.
Mutane da yawa sun yaba da yadda aka samu part dina so Ma-sha-Allah, ciki har da masu fadin mai hakuri mawadaci, basu dade ba suka fita har su Hafiza aka bar ni kadai a dakin ta cikin a nan na yaye gyalena ina kara kallon yadda kalle da aka min ja yake ta haiba.
Few people ne suka raso Ahnad zuwa dakina, a yadda suke zolayarsa yai musu shiru yana murmushi sai ka rantse da Allah ba shi ba ne, sai wani sun sun yake da kai kamar mai kunyar gaske.
Suma sun mana nasiha irin tasu sannan sukai mana addu'a, sai da ya raka su ya dawo, sai ya zauna kusa da ni ya cire min mayafin yana murmushi kamar yadda nima nake tsakanin fuskata da tasa sai na rasa wacce ta fi wata annuri, hannuna ya kama ta sumbata sannan yaja ni jikinsa ya rumgume.
“Al-hamdulillah, a yau Allah ya tabbatar mana da abunda ba mu taba mafarki ba, abunda ba mu taba kawowa a rai cewar zai faru ba a tsarim rayuwarmu, nesa ta zame mana kusa kunci da bakinciki ya zame mana farinciki da nishadi, ina rokon Allah yasa mutuwa ce zata raba mu kuma ya bamu zuri'ar mai kyau mai albarka, kuma ya bamu ikon kula da su da dauke sauke nauyinsu da yake kan mu”
“Amin”
Na fada ina wasa da zanen shaddar dake jikinsa, ji yai kamar rumgumar da yai min ba tai ba sai ya kara matseni sosai ya kirjinsa.
“Wallahi gani nake kamar ba gaske ne ba, Al-hamdulillah Allah”
Ya sake fada cike da nishadin, sallah godiya ga Ubangijince farkon abunda muka fara gabatarwa sannan neman tsarin Allah da kuma ni'imarsa ya biyo baya, muka ci daga abunda ya shigo min da shi, kana ya zuba min madara na sha sannan muka sake dabbaka wata sunnar.
Washe gari tun kamin mu tashi bachi Siyama da kwankwaso mana kofa, ina jin lokacin da ya daga ni a hankali saman kirjinsa ya kwantar da ni, ya gyara min duvet din sannan ya sumbace ni ya tashi ya fita. Be dade ba ya dawo ya sake jana kirjinsa ya rungume ba mu tashi ba sai kusan tara har da wani abu, shi ma dan Hafiza ta kira ni ta fada min cewar akwai yan'uwan Inna da za su zo yanzu.
A lokacin ne na tashi nai wanka na fito na tafi gaban madubi na shirya ina kokarin mikewa tsaye na hango shi ta cikin madubin yana kallon jikinsa ba riga sai tawul din daya daura shima iya kwankwasonsa. Murmushi nai na juyo ina kallonsa.
“Kawai gani nake kamar ba gaske ba ne”
Na sake yin murmushin sannan na nufi wardrobe a zatona kayan da nace Hafiza ta dauko min yana ciki sai nai arba da wasu tufafin dabam a ciki juyowa nai na kalleshi.
“Nawa ne?”
“Eh mana, daman ai ba zan kai miki gida ki yi kwalliya wani ya gani ba, ni da na siya ni za ayi wa kwalliya da su”
Bayan ya fadi haka ya karaso kusa da ni ya dafa ni yana min inda aka jera takalmin, akwai kayan da ba a dinke ba sai dai dikaken yafi yawa kuma kowane kaya da kalar hijabinsa babu gyale ko daya, gyale kan sai na abayar da aka saka a ciki amman bayan shi ban san wani mayafi mai suna veil a cikin kayan ba. Ko ba a fada min ba ni kaina a fahimci Ahmad mutum ne mai kishi hijabin kuma zai taimaka min na kara kare martabata da kuma mutuncin aure da kuma abunda Ahmad yake cewa na boye masa wai na sa shi kadai.
Sati daya Hajiya ta dauka tana mana girki na safe na rana na dare bata taba gajiyawa ba, sai da akai satin daya sannan ta sa aka kirani ita da kanta ta zaunar da ni falonta ta fada min cewar daga gobe zan fara girkawa mijina abinci da kaina.
“A ka'ida kwana uku ake, amman saboda ki huta yasa na dauki sati daya ina miki, yawancin duk abunda kika ga ina girka muku shine favorite din mijinki, dan haka sai ki haddace wani abun kuma za ki iya karawa dan kanki ko kuma ki saffara masa wani abun irin naku na yan zamani”
“In-Sha-Allah Hajiya na gode sosai Allah ya saka da alheri ya kara miki lafiya”
“Amin Allah ya muku albarka ku ma”
A nan na amsa da Amin, sannan na tashi na dawo part dina raina fes. Zaunawa nai saman kujerar da yake zaune sai ya dago ya kalleni sannan yasa hannunsa ya zagaye mazaunena.
“Hajiya tace zan fara maka girki daga gobe”
Na fada ina jan hancinsa dayan hannuna kuma a kunnensa ina wasa da shi. Lumshe ido yai ya bude yana tsutsar lips dinsa.
“Kin iya?”
Na dan yi fuskar shagwaba.
“Haba shi girkin?”
“Eh mana wasu yara irinki ba a koya musu girki a gida saboda son jiki”
Dariya nai sai ya kamo kaina ya hade goshinsa da nawa, ya sumbanci hancina yana isar min da numfashinsa.
“Idan baka kiya ba zan iya saka ki catering school ki koya mana”
“No ni din eh to ban hana ko dan koyan wadansu abubuwan ba na zamani amman indan girki ne irin na mu na hausa ai na saba yi na iya daidai gwargwado”
Mikewa tai tsaye ya ja hannuna muka nufi kitchen, gaban gas ya fara tsayar da ni sai ya koma bayana ya rumgume ni, da dayan hannuna ya rika nuna min yadda zan yi amfani da gas din.
“Na fa iya”
Bakinsa ya kai saitin kunnen yana cizona a hankali yace.
“Ki dauka baki taba aure ba sai yanzu, ki dauka wannan auren shi ne aurenki na fari, ki dauka komai sai a yanzu ne za ki koya sai a yanzu zaki iya, ki dauka Ahmad ne mijinki na farko kuma na karshe har abada”
Na gyada kai a hankali ina dan matse fuska domin maganar yake yana cizon kunne a hankali kamshin turarensa duk ya cika ni sai tayar min da zuciya yake.
“Okay”
“That's my Lims”
A dolen dole na biye masa ya rika nuna komai na kitchen din da yadda ake amfani da shi, wani abu kan ban san shi ba sai da ya fada min sauran kam duk na sansu kuma na saba amfani da su, domin ko a gidan Aminu da gas nake aiki balle kuma Abdulhamid.
Bayan mun gama muka fito daga kitchen din sai ya sake ni ya shiga ciki yai alwala, ina zaune ya fito yana sake hannayen rigarsa dake nade.
“Tashi ki yi alwala zanje masallaci”
Ya fada yana kissing dina, a kokarin yi masa addu'ar Allah ya tsare na ji lemun da na sha dazun ya dawo min a baki, saurin mikewa nai tsaye sai ya rike ni.
“Lafiya?”
Karnin turarensa yasa na fara sheka amai a gurin kamar wacce ta fi wani abu, sakina yai sai yai baya baya yana kallona baki sake kamar mai mamaki sai kuma ya rugo a guje yazo ya rumgume yana murmushi sai kuma ya sake ni.
“No wait....”
Sai kuma ya sake rumgume ni ya sake sakin ya sake rumgume ni yayi min haka yafi a kirga sai dariya yake. Can ya cire hular kansa ya jefar ya fara zagaya falon yana kallona kamar mai mafarki, sai kuma ya nufo ni ya daga fuskata yana kallona
“I can't believe this”
Ya fada kamin ya sake ni ya fadi a gurin yana ma Allah Sujada. Ni kan a raina nace daga ganin na yi amai idan kuma ya kasance malaria ce fa? Domin ni ban saba ciki da amai tun yana yaro ba sai ya fara girma hasalima ko irin laulayin nan na masu yaron ciki ban saba yi a ba sai ya fara fitowa na ke cin wuya har sai na raina kaina.
7/28/21, 8:33 PM - Buhainat: *GOBE NA...*
By Khadeeja Candy
6️⃣4️⃣