Sashe 45
Bakar Shuka Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Wani abu dake neman huda k'irjinta ta danne tace " kayi hak'uri Yaya, na jefa rayuwarmu cikin matsala, na mayar da gidan mu tamkar gidan zaman makoki, na gurb'ata kyakkyawar alak'ar dake tsakanin mu, na wargaza farin cikinmu, na lalata komai, kana da matarka ta aure ta sunna na mayar dakai tamkar gwauro duk da nasan kana da yawan buk'atar mace amma saboda san zuciya ta na rufe idona, nak'i tausaya maka, na danne maka duk wani hakk'inka dake kaina, na tauye maka damarka da Allah ya baka a kaina, amma duk da haka kayi hak'uri dani, ka jure duk wata musgunawa ta, na jefa rayuwar mu cikin bak'in bala'in da babu me fitar damu sai Allah, ka yafe min dan Allah, ta k'arasa maganar cikin matsanancin kukan dake huda zuciyarshi."Kiyi addu'a in sha Allah komai zaizo mana da sauk'i, da yardar Allah komai zai gyaru.
"Kayya kayya Yaya, adayyi shiru kawai amma har abada babu abinda zai gyaru.
"Subhanallahi haba sai kace ba musulma ba, sai kin yiwa kanki bak'in bakin da zai biki, babu abinda zai gagari Allah kedai kiyi addu'a.
Murmushi ya sake yi mata ya mik'e yaja mata bargo ya rufe ta yana fad'in " ki kwanta sai da safe.
Tana san tace ya tsaya ya taya ta kwana amma tana jin kunyar fad'ar hakan, tana ji tana gani ya fice bayan ya kashe mata fitilar d'akin, ta sauke nannauyan numfashi had'i da rufe idonta tunaninka kala-kala na zuwa kanta, har bacci yayi awon gaba da ita.
*************************************
" Ajlaal wai meke damunka ne?
"Duk kabi kayi wani zuru-zuru dakai kamar mahaukaci saban kamo, Abbanshi ya fad'a yana kallan shi.
A fili Mama ta sauke ajiyar zuciya had'i da cewa " jibi yadda ya lalace ya rame ya jeme, ka fad'a mana abinda ke damunka matuk'ar baifi k'arfin mu ba zamuyi maka maganinshi da izinin Allah.
"Ina santa! Itace rayuwata, ita kad'ai ce macen da nake so, dan ita numfashi na ke fita, dan ita zuciya ta ke bugawa idan na sake rasata a karo na biyu bazan iya jurewa ba, mutuwa zanyi, dan Allah ku taimaka min ina santa da duka zuciya ta.
Kallan juna Mama da Abbah sukayi cikin mamakin dake bayyane saman fuskarsu k'arara, mayar da kallanshi Abbah yayi kan Ajlaal yace " bamu fahimce ka ba?
"Kayi mana k'arin bayanin inda kalamanka suka dosa wacece kake son?
A wahalce muryarshi na rawa yace " Deeyanah! Abbah Deeyanah ce ina matuk'ar santa akanta zan iya aikata komai, please ku taimaka min karku rasa ni.
Sake kallan juna Mama da Abba sukayi a karo na biyu sai dai wannan karon ba mamaki bane bayyane saman fuskarsu ba, tsoro ne, tsoron kodai tilon d'ansu ya haukace ne, dan su a iya saninsu Deeyanah ta dad'e dayin aure, bama zasu iya tuna adadin shekarun ba, a k'iyasi dai sun san yanzu tayi yara hud'u, amma ita yake magana yanzu?
"Meyasa kake magana akan matar wani?
"Meyasa kake magana akan Deeyanah bayan kafi kowa sanin tana da aure harda yara?
"Meyasa bazaka hak'ura da ita ka nemi wata ka aura ba?
"Ita dai Abbah, Deeyanah daka sani ita.
"Kodai ka fara shaye-shaye ne Ajlaal bamu sani ba?
Abbah yayi maganar yana kallan Ajlaal d'in cikin tashin hankali.
"Ban fara ba amma ina gaf da farawa a kowanne lokaci.
"Wata k'ila ma ta dad'e da mantawa dakai a rayuwarta tana can tana rayuwarta cikin farin ciki ka tsaya kana azabtar da kanka a banza, please ka sawa ranka hak'uri da salama ka dangana ba komai muke so muke samu ba a rayuwa, sau da yawa zaka ga abinda muka so bashi ne yake zama rabon mu ba, haka ba shine alkhairin mu ba.
" Rasa wanda muke so nuni ne na cewa raban mu yana ta can wani wajen yana neman mu, dan mun fad'i a soyayyar wani ba yana nufin mun rasa soyayya ta har abada bane, ba asara bane danka rasa wanda kake so, asara shine ka rasa kanka wajen k'aunar wanda kai a wajenshi ba komai bane, sauk'i yana tare da tsanani, mai hak'uri yana cimma dad'i, mai kyauta baya tab'a rasawa, duk wanda yaji tsoron Allah Ubangiji zayyi mishi mafita, manta da damuwa ka fuskanci rayuwa, kowa ka gani a duniya da akwai abinda ya dame shi.
" Fadadawa rayuwa ce, tsukakewa mutuwa ce, rayuwa itace yiwa kowa fatan alkhairi, san wawashe komai wa kanka ba komai cikinsa face halaka, a kowacce mu'amula ka zama mai gaskiya da rik'on amana saboda baka san yaushe ne, a wanne lokaci a ina ne cutar dakai zata farauci rayuwarka, duniyarka da farin cikinka ba........
" Kai dalla can dakata shashasha sauna asararran banza kawai ba wa'azi yazo yace kayi mishi ba ka cika mutane da surutun banza duk kabi ka tofe mu da yawu, haka ka tsaya shirme a wancan lokacin na baya har ya rasata, Mama ta fad'a cikin masifa tana galla mishi harara kamar idanuwanta zasu fad'o k'asa, lakwas Abbah yayi duk da yana san ya sake yin magana amma tsoronta dake danne shi ya hana.
Kallanta ta mayar ga Ajlaal tana huci kamar wacce tayi tseren gudu tace " kaima kai ka tsaya kana b'atawa kanka lokaci wannan gantallen daka d'auka a matsayin uba wacce uwar zai iya yi maka?
"Ka fita kaje ka nemi soyayyarka ta kowanne hali, kada ka sake ka dawo min gida batare da suruka ta abar k'aunarka Deeyanah ba, kayi koma meye danka mallake ta.
Cikin sanyi cike da fargaba Abbah yace " koma meye kika ce f..... kallan data watsa mishi yasashi had'iye sauran maganar dole.
*********************************
Tana zaune saman sallaya ta d'aga hannayenta tana tsiyayar da hawaye me k'una da take jinsu tamkar soyayyan mai, addu'a take yi sosai ta neman yafiya.
"Ya Ubangijin al'arshe ya Ubangijin sammai da k'assai, kaji k'aina ka yafe min zunubaina, Kai mai rahama ne, mai tausayi ne, mai yafiya da afuwa ne, ya Allah na sani ni mai tarin zunubai da manyan laifuka ne wad'anda suke rinjaya ta, ya Allah ka.......
Banko k'ofar da akayi yasata saurin d'agowa ta kalli k'ofar, ya fad'o d'akin tamkar an jeho shi, yayi tsaye k'erere kanta, daga k'amshin turaren jikinshi ta gane shine batare data d'ago kanta ta kalle shi ba.
A galabaice ya kira sunanta " Deeyanah!.
Yadda kasan ba sunanta ya kira ba ta cigaba da addu'arta.
"Ina sanki Deeyanah dan Allah karki barni, karki juya min baya a sanda nafi buk'atarki, wallahi nafi Deen sanki, ki yarda dani, kizo mu gudu muyi ta can wani b'angaren duniya, muyi rayuwa daga ni saike sai yaranmu.
Addu'ar ta shafa kana ta mik'e ta ninke sallayar ta aje, ta nufi gado ta kwanta yadda kasan bata san da mutum ba, jikinshi na wata irin rawa kamar mazari ya isa gareta yasa hannu ya d'ago ta ya mannata da k'irjinshi, a fili ya sauke ajiyar zuciya yana fad'in " a wajenki kad'ai nake samun irin wannan nutsuwar dan Allah karki guje ni.....
A zuciye ta fisge jikinta daga nashi tana jin turirin azabar da fatar jikinta ke fitarwa tamkar ya watsa mata wuta, cikin matsanancin b'acin rai ta yarfa mishi mari a saman kuncin shi, zayyi magana ta dakatar dashi da hannunta tace.
"Kamar ban tab'a fad'a maka bana bana san kana tab'a min jikina ba?
"Sau nawa kake san na sanar dakai illa da bak'ar masifar dake tattare da hakan?
"Sanki ne ke neman haukata ni.
"K'arya kake baka so na Ajlaal, wallahi da kana so na daka so min kyakkyawan k'arshe da gamawa da duniya lafiya, da kayi min sha'awar rayuwa mai kyau, daka yi min fatan kusanci da Allah da samun rabauta duniya da lahira, da kayi min addu'ar shiga Aljanna, da kayi min addu'ar neman tsari da wuta, da kayi min fatan rahamar Allah,
amma kai da kake ikirarin kafi kowa so na, kaine zaka kama hannuna ka shigar dani wuta.
"Kana tak'amar kana so na d'inne zaka nisanta ni da mahaliccina?
"Kana so na zaka nisanta ni da samun rahamar Ubangiji?
"Kana so na zaka rabani da dukkanin farin ciki na?
"Kana so..... " Dakata Deeyanah!
Ya fad'a yanayinshi yana canjawa!
" Wallahi idan duniya zata tashi, babu mahaluk'in daya isa ya rabani dake koda kuwa keda kanki ne, koda hakan yana nufin kawo yak'in duniya na k'arshe, ban damu da adadin mutanen da zasu rasa rayukansu ba, dan haka ki dawo cikin hayyacinki, a baya na baki zab'i biyu kink'i d'aukar ko d'aya, to yanzu ma zan sake baki wani zab'in imma ki dawo mu d'ora daga inda muka tsaya ko kuma ki kashe aurenki kizo muyi aure ko kuma in turawa mijinki video dan yana nan a wayata har yanzu, kinga ai dole ya sake ki ki dawo min.
Ta bud'e baki zatayi magana ya d'ora yatsanshi saman lips d'inta yana zagaya bakinta had'e da cije lips d'inshi ya lumshe idanuwanshi yana shafa k'irjinshi yace " ina san bakin nan naki, yana da dad'in tsotsa, ya k'arashe maganar had'e da rankwafowa zai sha bakinta, ta hannayenta ta hankad'ashi baya da iya k'arfinta gami da nunashi da yatsa tace " Allah yayi min tsari dakai la'ananne mai mugun nufi, yayi dariya yana cewa " karki manta lissafin kwanakin fa sati d'aya yana nufin kwanaki bakwai, bai jira tayi magana ba ya fice, rasa abinda zatayi ne yasata durk'ushewa a k'asa ta fasa rikitaccen kuka.
Anan k'asa tana kuka bacci yayi awon gaba da ita, sha biyu dai-dai na dare ringing d'in wayarta ya cika dak'in ta farka firgigit cikin rashin nutsuwa, da sauri ta kaiwa wayar raruma hannunta ya danna wajen amsa kira batare data sani ba, "irin wannan bacci haka kamar ina kusa dake, yayi maganar sautin dariyarshi na ratsa cikin kanta, " tik tok tik tok lokacinki yana tafiya fa yau saura kwanaki shida, batayi mishi magana ba ta datse kiran had'i da kashe wayar tayi jefa da ita gefe.
"Kayya kayya Yaya, adayyi shiru kawai amma har abada babu abinda zai gyaru.
"Subhanallahi haba sai kace ba musulma ba, sai kin yiwa kanki bak'in bakin da zai biki, babu abinda zai gagari Allah kedai kiyi addu'a.
Murmushi ya sake yi mata ya mik'e yaja mata bargo ya rufe ta yana fad'in " ki kwanta sai da safe.
Tana san tace ya tsaya ya taya ta kwana amma tana jin kunyar fad'ar hakan, tana ji tana gani ya fice bayan ya kashe mata fitilar d'akin, ta sauke nannauyan numfashi had'i da rufe idonta tunaninka kala-kala na zuwa kanta, har bacci yayi awon gaba da ita.
*************************************
" Ajlaal wai meke damunka ne?
"Duk kabi kayi wani zuru-zuru dakai kamar mahaukaci saban kamo, Abbanshi ya fad'a yana kallan shi.
A fili Mama ta sauke ajiyar zuciya had'i da cewa " jibi yadda ya lalace ya rame ya jeme, ka fad'a mana abinda ke damunka matuk'ar baifi k'arfin mu ba zamuyi maka maganinshi da izinin Allah.
"Ina santa! Itace rayuwata, ita kad'ai ce macen da nake so, dan ita numfashi na ke fita, dan ita zuciya ta ke bugawa idan na sake rasata a karo na biyu bazan iya jurewa ba, mutuwa zanyi, dan Allah ku taimaka min ina santa da duka zuciya ta.
Kallan juna Mama da Abbah sukayi cikin mamakin dake bayyane saman fuskarsu k'arara, mayar da kallanshi Abbah yayi kan Ajlaal yace " bamu fahimce ka ba?
"Kayi mana k'arin bayanin inda kalamanka suka dosa wacece kake son?
A wahalce muryarshi na rawa yace " Deeyanah! Abbah Deeyanah ce ina matuk'ar santa akanta zan iya aikata komai, please ku taimaka min karku rasa ni.
Sake kallan juna Mama da Abba sukayi a karo na biyu sai dai wannan karon ba mamaki bane bayyane saman fuskarsu ba, tsoro ne, tsoron kodai tilon d'ansu ya haukace ne, dan su a iya saninsu Deeyanah ta dad'e dayin aure, bama zasu iya tuna adadin shekarun ba, a k'iyasi dai sun san yanzu tayi yara hud'u, amma ita yake magana yanzu?
"Meyasa kake magana akan matar wani?
"Meyasa kake magana akan Deeyanah bayan kafi kowa sanin tana da aure harda yara?
"Meyasa bazaka hak'ura da ita ka nemi wata ka aura ba?
"Ita dai Abbah, Deeyanah daka sani ita.
"Kodai ka fara shaye-shaye ne Ajlaal bamu sani ba?
Abbah yayi maganar yana kallan Ajlaal d'in cikin tashin hankali.
"Ban fara ba amma ina gaf da farawa a kowanne lokaci.
"Wata k'ila ma ta dad'e da mantawa dakai a rayuwarta tana can tana rayuwarta cikin farin ciki ka tsaya kana azabtar da kanka a banza, please ka sawa ranka hak'uri da salama ka dangana ba komai muke so muke samu ba a rayuwa, sau da yawa zaka ga abinda muka so bashi ne yake zama rabon mu ba, haka ba shine alkhairin mu ba.
" Rasa wanda muke so nuni ne na cewa raban mu yana ta can wani wajen yana neman mu, dan mun fad'i a soyayyar wani ba yana nufin mun rasa soyayya ta har abada bane, ba asara bane danka rasa wanda kake so, asara shine ka rasa kanka wajen k'aunar wanda kai a wajenshi ba komai bane, sauk'i yana tare da tsanani, mai hak'uri yana cimma dad'i, mai kyauta baya tab'a rasawa, duk wanda yaji tsoron Allah Ubangiji zayyi mishi mafita, manta da damuwa ka fuskanci rayuwa, kowa ka gani a duniya da akwai abinda ya dame shi.
" Fadadawa rayuwa ce, tsukakewa mutuwa ce, rayuwa itace yiwa kowa fatan alkhairi, san wawashe komai wa kanka ba komai cikinsa face halaka, a kowacce mu'amula ka zama mai gaskiya da rik'on amana saboda baka san yaushe ne, a wanne lokaci a ina ne cutar dakai zata farauci rayuwarka, duniyarka da farin cikinka ba........
" Kai dalla can dakata shashasha sauna asararran banza kawai ba wa'azi yazo yace kayi mishi ba ka cika mutane da surutun banza duk kabi ka tofe mu da yawu, haka ka tsaya shirme a wancan lokacin na baya har ya rasata, Mama ta fad'a cikin masifa tana galla mishi harara kamar idanuwanta zasu fad'o k'asa, lakwas Abbah yayi duk da yana san ya sake yin magana amma tsoronta dake danne shi ya hana.
Kallanta ta mayar ga Ajlaal tana huci kamar wacce tayi tseren gudu tace " kaima kai ka tsaya kana b'atawa kanka lokaci wannan gantallen daka d'auka a matsayin uba wacce uwar zai iya yi maka?
"Ka fita kaje ka nemi soyayyarka ta kowanne hali, kada ka sake ka dawo min gida batare da suruka ta abar k'aunarka Deeyanah ba, kayi koma meye danka mallake ta.
Cikin sanyi cike da fargaba Abbah yace " koma meye kika ce f..... kallan data watsa mishi yasashi had'iye sauran maganar dole.
*********************************
Tana zaune saman sallaya ta d'aga hannayenta tana tsiyayar da hawaye me k'una da take jinsu tamkar soyayyan mai, addu'a take yi sosai ta neman yafiya.
"Ya Ubangijin al'arshe ya Ubangijin sammai da k'assai, kaji k'aina ka yafe min zunubaina, Kai mai rahama ne, mai tausayi ne, mai yafiya da afuwa ne, ya Allah na sani ni mai tarin zunubai da manyan laifuka ne wad'anda suke rinjaya ta, ya Allah ka.......
Banko k'ofar da akayi yasata saurin d'agowa ta kalli k'ofar, ya fad'o d'akin tamkar an jeho shi, yayi tsaye k'erere kanta, daga k'amshin turaren jikinshi ta gane shine batare data d'ago kanta ta kalle shi ba.
A galabaice ya kira sunanta " Deeyanah!.
Yadda kasan ba sunanta ya kira ba ta cigaba da addu'arta.
"Ina sanki Deeyanah dan Allah karki barni, karki juya min baya a sanda nafi buk'atarki, wallahi nafi Deen sanki, ki yarda dani, kizo mu gudu muyi ta can wani b'angaren duniya, muyi rayuwa daga ni saike sai yaranmu.
Addu'ar ta shafa kana ta mik'e ta ninke sallayar ta aje, ta nufi gado ta kwanta yadda kasan bata san da mutum ba, jikinshi na wata irin rawa kamar mazari ya isa gareta yasa hannu ya d'ago ta ya mannata da k'irjinshi, a fili ya sauke ajiyar zuciya yana fad'in " a wajenki kad'ai nake samun irin wannan nutsuwar dan Allah karki guje ni.....
A zuciye ta fisge jikinta daga nashi tana jin turirin azabar da fatar jikinta ke fitarwa tamkar ya watsa mata wuta, cikin matsanancin b'acin rai ta yarfa mishi mari a saman kuncin shi, zayyi magana ta dakatar dashi da hannunta tace.
"Kamar ban tab'a fad'a maka bana bana san kana tab'a min jikina ba?
"Sau nawa kake san na sanar dakai illa da bak'ar masifar dake tattare da hakan?
"Sanki ne ke neman haukata ni.
"K'arya kake baka so na Ajlaal, wallahi da kana so na daka so min kyakkyawan k'arshe da gamawa da duniya lafiya, da kayi min sha'awar rayuwa mai kyau, daka yi min fatan kusanci da Allah da samun rabauta duniya da lahira, da kayi min addu'ar shiga Aljanna, da kayi min addu'ar neman tsari da wuta, da kayi min fatan rahamar Allah,
amma kai da kake ikirarin kafi kowa so na, kaine zaka kama hannuna ka shigar dani wuta.
"Kana tak'amar kana so na d'inne zaka nisanta ni da mahaliccina?
"Kana so na zaka nisanta ni da samun rahamar Ubangiji?
"Kana so na zaka rabani da dukkanin farin ciki na?
"Kana so..... " Dakata Deeyanah!
Ya fad'a yanayinshi yana canjawa!
" Wallahi idan duniya zata tashi, babu mahaluk'in daya isa ya rabani dake koda kuwa keda kanki ne, koda hakan yana nufin kawo yak'in duniya na k'arshe, ban damu da adadin mutanen da zasu rasa rayukansu ba, dan haka ki dawo cikin hayyacinki, a baya na baki zab'i biyu kink'i d'aukar ko d'aya, to yanzu ma zan sake baki wani zab'in imma ki dawo mu d'ora daga inda muka tsaya ko kuma ki kashe aurenki kizo muyi aure ko kuma in turawa mijinki video dan yana nan a wayata har yanzu, kinga ai dole ya sake ki ki dawo min.
Ta bud'e baki zatayi magana ya d'ora yatsanshi saman lips d'inta yana zagaya bakinta had'e da cije lips d'inshi ya lumshe idanuwanshi yana shafa k'irjinshi yace " ina san bakin nan naki, yana da dad'in tsotsa, ya k'arashe maganar had'e da rankwafowa zai sha bakinta, ta hannayenta ta hankad'ashi baya da iya k'arfinta gami da nunashi da yatsa tace " Allah yayi min tsari dakai la'ananne mai mugun nufi, yayi dariya yana cewa " karki manta lissafin kwanakin fa sati d'aya yana nufin kwanaki bakwai, bai jira tayi magana ba ya fice, rasa abinda zatayi ne yasata durk'ushewa a k'asa ta fasa rikitaccen kuka.
Anan k'asa tana kuka bacci yayi awon gaba da ita, sha biyu dai-dai na dare ringing d'in wayarta ya cika dak'in ta farka firgigit cikin rashin nutsuwa, da sauri ta kaiwa wayar raruma hannunta ya danna wajen amsa kira batare data sani ba, "irin wannan bacci haka kamar ina kusa dake, yayi maganar sautin dariyarshi na ratsa cikin kanta, " tik tok tik tok lokacinki yana tafiya fa yau saura kwanaki shida, batayi mishi magana ba ta datse kiran had'i da kashe wayar tayi jefa da ita gefe.