← Book details Bakar Shuka Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 31 OF 56

Sashe 31

Bakar Shuka Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Bata tsaya ba tana cigaba da tafiya tace " sallah zanyi na dawo na cigaba da d'iba, bayyi magana ba ya mik'e bai bita d'akinta ba ya wuce d'akinshi da hanzari ya k'arasa alwalar ya fita dan yaji har liman ya shiga, tana jin fitarshi ta sauke ajiyar zuciya zuciya had'i da fad'awa kan gado ta saki kuka, tana jin wayarta na motsi amma tayi banza da wayar danta san ko waye, sai da tayi me isarta kana ta mik'e ta shiga ban d'aki ta d'auro alwala ta fito ta tada, bata tashi daga kan sallayar ba tana lazimi har aka kira sallar ishaa, ta mik'e tayi sallar bata tsaya yin addu'a ba tayi saurin ficewa daga part d'in su dan kar dawo ya same ta, part d'in Ammi ta shige ta iske ta zaune kan sallah tana jan carbi, ganin Deeyanah yasata tak'aita addu'ar, suna hira har tara sai ga Deen ya shigo, tana ganinshi ta soma gyangyad'in k'arya, zama shima yayi suka d'an tab'a hirar da Ammi har goma tayi, ganin irin kallan da yake yiwa Deeyanah suna hirar amma gaba d'aya hankalinshi na kanta, sai zungurinta yake yi ta k'asa da k'afa yasa Ammi cewa " tashi kuje sai da safe.

Dole badan taso ba ta mik'e yayi saurin ficewa tabi bayanshi, Ammi tabi bayansu da kallo tana murmushi, tsayawa yayi wajen Azrah daya gani tsaye, tayi saurin shigewa gidan tayi amfani da wannan damar tana zuwa ta baje saman bed, kafin yazo ta hau baccin k'arya, daya dawo yayi mata tashin duniya amma tak'i tashi wai ita tayi bacci, "yanzu fa kika shiga ko minti biyar ba'ayi ba amma har kinyi nisa a bacci kuma a sanin danayi miki ai baki da nauyin bacci haka?

Ganin bata da niyyar tashi yasa shi d'ago ta yana fad'in " haba kusan shekara biyu bamuyi sex ba amma bakya ko d'okina?

"Ke in zaki iya jurewa ni nakai k'arshen mak'ura ya fad'a yana had'e bakinsu, da iya k'arfinta ta rufe bakin tak'i bashi damar da zai sha bakinta, murmushi yayi had'i da kwantar da ita batare daya sake yin yunk'urin wani abu ba ya fice daga d'akin, dakyar ya iya kai kanshi d'akin shi saboda wata irin muguwar sha'awa dake cinshi, yana shiga bedroom d'inshi ya wuce bathroom had'i da sakarwa kanshi shower ya dad'e ruwan na sauka kanshi kafin ya samu wutar dake ruruwa a jikinshi ta mutu, dakyar ya rarrafa ya cire kayanshi ya zube saman bed.

Ita ko yana fita ta mik'e zata dannawa k'ofar key Ajlaal ya turo k'ofar ya shigo rolling idanuwanta tayi had'i da cewa " me kazo yi kuma?

"Raya sunna, ya rad'a mata a kunnenta yana dariya, dariyar itama tayi ta juya ta koma kan gadon, ya bita yana cewa " ah irin wannan kwalliya haka da akayi mishi?

Dariya tayi sosai gami da cewa " sarkin kishi, ya zauna kusa da ita had'i da sanya hannu ya d'ago hab'arta ya zuba mata ido yana kallan kwayar idonta, sun d'auki lokaci a haka sannan ya had'e bakinsu suka soma aikawa juna deep kiss had'i da tsotsar lips d'in junansu, cikin salon gwarewa da iya sarrafa mace ya zame rigar jikinta k'asa ya soma sarrafa ta yana rud'a mata jikinta da sak'unanshi masu wuyar mantawa, a rikice ta soma mayar mishi da martani ta fara rikita mishi lissafi had'i da mantar dashi zahirin duniyar da yake, cikin k'ank'anin lokaci suka gama rikita junansu, suka birkita komai dake kan gadon duk wani pillow sai da aka wullo shi k'asa abu ya d'auki zafi iya zafi kana komai ya wakana basu sararawa juna ba sai wajen asuba, suka zube saman gadon suna mayar da numfashi, shi kam Deen kwana yayi cur bai runtsa ba yana ta faman murk'ususu yana juyi saboda sha'awa, ya mik'e zaije d'akinta yafi sau goma amma bai san meke hanashi zuwan ba, sai wajejen asuba wahalallan bacci yayi awon gaba dana shi.

Bai farka ba sai wajejen sha d'aya na safe wani masifaffen ciwon ciki ya farkar dashi a daddafe ya fito daga d'akin daga shi sai bedsheet d'in daya rufa ya jawo ya d'aura ya fito dashi, tana tsaye daga ita sai rigar bacci iya gwiwa ko d'an kwalli babu akanta ta tufke gashin kanta da ribon, tana jera abinci a dinning Deedee na zaune yana ta faman zuba mata surutu Deen ya fito, bai ma kula da Deedee ba, bai san yadda akayi ba sai ganinshi yayi kusa da ita, tun da take dashi a iya tsayin rayuwar da sukayi tare bata tab'a ganinshi cikin irin wannan yanayin ba, wani irin mugun tsoro ne ya kamata ta saki kofin glass d'in hannunta, kafin tayi wani yunk'uri ya damk'eta ya had'e bakinsu, wani irin kiss yake yi mata da k'arfi har zafi-zafi take ji, bazai iya tsayawa long romance ba, dan haka ya sab'ule hannun rigar jikinta ta fad'i k'asa, dakyar ta iya had'a kalmomin bakinta tace " Deedee..!, ido ya soma rabawa yana duba inda yaron yake, zaune ya ganshi kan kujera ya saki baki yana kallan ikon Allah.

A tsawace cikin hargowa Deen ya daka mishi tsawa " tashi ka fita, jikin yaran na rawa ya mik'e ya fice saboda tsoratar da yayi a bud'e yabar k'ofar da gudu ya shiga part d'in Ammu, tare da Ammi ya same su tsaye a kitchen suna aiki, " Ammi ga Daddy can yana cirewa Momy kaya, shima ya cire kayan jikinshi shine ya koro ni, kallan juna sukayi ita da Ammi, Ammu taja tsaki tana fad'in " yaran yanzu sai a barsu, koma wanne uzurin ne ya kamasu su kasa hak'uri a gaban d'ansu fisabilillahi?

Ammi tayi murmushi tare da durk'usawa ga Deedee tace " laifi tayi mishi shine zai zane ta, kaima idan ka sake ka fad'awa wani abinda ya faru irin abinda yayiwa Momynka shi zayyi maka, a tsorace ya girgiza kanshi yana cewa " babu wanda zan gayawa, " yauwa good boy, Ammi ta fad'a tana shafa kanshi, Ammu ta sake jan dogon tsaki a karo na biyu cikin jin haushi tayi kwafa batare data ce komai ba, Ammi tayi dariya tana fad'in " ke karki matsawa yara na, barsu suyi lokacinsu ne, ke meye bakuyi ba a lokacinku, Ammu tayi dariya batare datace komai ba.

Deedee na fita ya sake had'e bakinsu har wani sake danno kanta yake yi ta baya da hannunshi, ya zagayo da hannunshi kan boobs d'inta ya soma mammatsa su, cak ya d'auke ta ya rabata da k'asa ya dawo cikin falo da ita ya jefa ta saman sofa 3 sitter ya bita ya danne, a gaggauce ya cigaba da romancing d'inta, ita kam in banda bugu babu abinda k'irjinta keyi, a hankali ta soma k'ok'arin janye jikinta daga nashi, ai yadda kasan zata rabashi da ranshi, ya sanya k'irjinshi ya danne ta sosai ta yadda ko kwakkwaran motsi bazata iya ba, tayi-tayi ta kwace kanta amma ta kasa, idonta ta runtse da k'arfi had'i da tattaro daga d'aya k'arfinta ta tura shi, tayi saurin tashi zaune tare da kifa kanta kan tafin hannayenta tana mayar da numfashi.

Da sauri ya tashi ya kuma nufarta tayi saurin mik'ewa had'i da dakatar dashi ta hanyar d'aga mishi hannu tana hakki tace " ba....ba...bana... sallah, ina period ne, d'an dakawa yayi gami da tsare ta da shanyayyun idanuwanshi da suka rikid'e suka koma kamar na mashaya, sai da ya furzar da iska daga bakinshi kana yace " da idan kina period haka kike yi min idan ina cikin mood?

"Naga kin san duk hanyar da zaki bi ki saka ni na samu nutsuwa, yayi magana yana tsareta da ido yayinda acan k'asan zuciyarshi kokawa yake da zuciyar dan karta sak'a mishi mugun abun da take san sak'a mishi akanta, leb'enta na k'asa ta d'an lasa gami da sanya hannu ta mayar da gashin kanta daya bazo mata, tana san tayi magana amma idonshi dake kanta ya hanata bata damar yin maganar.

Cikin suyar k'irji yace " haka kika yi tayi min wan can karon har na gaji nayi zuciya na barki da abunki, yanzu ma gashi kin kuma, anya Deeyanah babu wani abu da kike b'oyewa, shekara kusan biyu fa bamuyi sex ba, and shekara d'aya da rabi bama tare baki ganni ba ban ganki ba, bakiji d'umin jikina ba ban ji d'umin jikinki ba, amma ace dana dawo ko marmarima da d'orina bakiyi?

"Dana tafi America ko sau d'aya tak baki tab'a kira na kince min sha'awa na damunki ko you're in the mood ba, baki tab'a kira na video call ba, ke bama ki bani time & attention d'inki ba, babu wata kula da kika bani har naje na dawo a matsayi na mijinki, dana dawo maimakon ma ace kece ke rushing in to sex amma kece ke denied, why Deeyanah?

"Ina sha'awarki take tafiya?

"Wake gusar miki da ita Deeyanah?

"Anya bakya neman maza da aure na akanki!?

"Wad'annan sune tambayoyin da ke san na rink'a yiwa kaina har zarginki ya shiga raina auren mu ya haramta?

"Ko ko kin d'auki aure abin wasa da sai lokacin da kike da buk'atar koma meye za'ayi?

"Bana san na zarge ki, please karki tilastawa zuciya ta zarginki dan hakan bazai tab'a haifar mana d'a me ido ba, dan Allah karki tursasa ni na shiga zarginki, daga ni har ke bazamu ji dad'in abun ba, gwara tun wuri ki nemarwa kanki mafita, imma wasu k'awayen kikayi suke neman hure miki kunne gwara ma tun wuri tun kan dare yayi miki ki canja tunani, har ya juya zai bar wajen ya juyo ya sake jefa idonshi cikin nata yana kallan kwayar idonta ya nuna mata d'an yatsa yace " duk abinda zakiyi kije kiyi ta yinshi zan iya jurewa, amma middin kika sake kika ci amanata, ya cije lips d'inshi na k'asa.
Chapter 31 · 0% Book details