← Book details Bak'a Ce Part 1 Complet Hausa Novel Local reading mode
READING PART 94 OF 110

Sashe 94

Bak'a Ce Part 1 Complet Hausa Novel · about 8 min read

Ayya ta kai dubanta kansa, ta girgiza kai ta ce" ya gabatar da hujarsa, wace sam bai dace dan wannan hujar a saki mace ba, batai masa laifin komai ba, shima bai mata ba, hasalima tun kafin a yi masa aikin ya yi sakin, bisa hujarsa na aminin nasa ya fi shi son ta!

Dum gabansa ya fadi, da sauri ya kalli Ayya, la.ila ha ilala , shi ne abinda ya iya cewa, ya ake maganar yana magana kai tsaye bayan ga wada ke yi? Bai taba zaton, bai taba kawowa ransa cewar Ayya zata fadi maganar haka kai tsaye ba ,

Shiru ne wajen ya dauka, kafin Ayya ta ci gaba" na ji ba dadi, na yi fushi, Aure? Sai kace abin wasa? Ya tashi ya guntule igiyar auren yarinyar da bata san me ake ciki ba? Kan wani shirme? , shima Wardugun ya nuna masa ba dadi, maganar da nake maka har yanzu ba wani jituwa tsakaninsu,
Nan ta kwashe du abinda ya faru ta sanarwa Gukunni da da farko ya dauki zafi har ya ga kamar an wulakanta yarinyar ne dan anai mata kallon marar gata, sai dai daga baya da ya ji komai ya yi tsam ya dubi Ayya, ya kuma dubi Wardugu da ya dafe kansa yana tunani, aa, du wannan jawabin na menene? Ya Allah🤦🏻‍♂️

A daidai lokacin da Agaishat ta fito dauke da farantin da ta soyawa Wardugu dankalin turawa da plantain ta nufo falon,
Muryar Gukunni ta karade wajen da tambayar da ya saka ni ranaza har na saki biron hannuna,

Gukunni ya dubi Wardugu ya jefo tambayar da basu tsamaci zai yita ba, Gukunni ya ce" *SHIN DA GASKE KANA SON AGAISHAT NE? ZAKA IYA AURENTA KODA KUWA TABON DA RAYUWARTA KE DA?**************

MEMBERS BAK'A CE GRUP, WOLLAH INA JI DA KU TAMKAR NAMA DAYA A MIYA,
WATO KUNA SAKANI NISHADI DA COMMENT DIN KU,
HAR KUKE SAKAWA NA JI NI YESSSSSS NI DIN TAKU CE😌😌😌😌😌

🐫🐫🐫🐫 *BAK'A CE* 🐫🐫🐫🐫

Na
*SAJIDA*

7️⃣7️⃣

*KUTKALE* (PRISON)

*AURE YAKIN MATA NE*

*KAMARTA, BATA DA NIYAR CUTARWA*

daga alkalamin yar mutan niger *SAJIDA* in sha Allah,

........kar ku bari a baku labari.....

Da sauri Ayya ta ce" Aman ya Gukunni, ba shi ya dace a tambayi wannan abin ba, bana so a kuma yiwa y'ata abinda akai mata sai ta zaba! Kuma da ake maganar nan , bai jima da yin aure ba fa, ko cike shekara hudu bai yi, hasalima matarsa na kwonce asibiti dan ya dankara mata maganar cewa yarinyata *Orronur* dinsa ce! , dan Allah kar a tauye min yarinya,

Dubansa ya kai kan Agaishat da ta ja ta tsaya tana binsu da kallo, wai bata fahimci wa ake shirin hadata da shi kuma? Waye matarsa ba lafia? Wardugu ne, meye kalmar Orronur ke nufi? Ya Allah wani hadin za.a kuma yi mata ko me? Hadinma da Wardugu? Mutumen da ita ce shaidar irin yanda yake kwasa da matar so ma bale ita?, mutumen da ta yi imanin har abada ba macen da zata samu gurbi a zuciyarsa kamar yanda *AISATA* ta gama mamaye ko.ina? Domin a yi yawo da ganga ba zata hadiye cewar ba sonta da yake ne ya saka ya kasa yafewa mahaifinsa dan ya aureta ba! Mijin WALYN? ko ba wannan ba, ita ta yi imanin koda daura masa ita za.a yi a kafa zai ja banza a titi sannan ya take da ranjasss ya bale ya jefawa karnuka su cinye banza, ita a wa? Yar wa? Algabitt? Um, yayan manya, manyan kansu suna farauta ? Ita bata son mai kyau dan kar a ringa rububinsa, ita ita....

Tunaninta ne ya katse a lokacin da Ayya ta ce" kar mu yi haka da kai,

Tsai ta kai dubanta wajen Ayya a ranta tana fadin" ki yi wani abu, ni ban san wani kaka ba, yaushe ma ya zo gidan? Ki yi wani abu kar a kashe maki d'a, sannan a kashe maki y'a!

Wajen sai ya kasance Agaishat na kallon Ayya da wani yannayi, Wardugu kuwa tsai kawai ita yake kallo yana son sannin halin da ta shiga dan kuwa ya san ba kurma bace, kuma ba sakara bace, tabas ta fahimci maganar da ake,

Ayya kuwa Na duban Gukunni, inda Gukunni ya gyara zama yana sakin murmushi yana duban Wardugu da yannayinsa, ya san waye shi, ba zai taba amsa shi a haka ba, ya kuma lura da yannayin Agaishat da irin duban da take yiwa uwar rikonta, wani sanyi ya ji a ransa domin ya ga shakuwa, kauna ta Allah tsakanin Agaishat da mahaifiyar Wardugu,

Mikewa ya yi ya yiwa su Ayya salama, inda Wardugu ya mike ya bi bayansa dan yi masa rakiya yana mai jin ba laka a jikinsa,

Sai da suka dangana da motarsa ya dakatar da shi, inda ya dauki katuwar wayarsa ya danna kira,

Dagawa ya yi tare da kara yin salama sannan ya ce" honorable ka samu ganninsa ne?

Gukunni ya yi murmushi ya ce" wato Alhaji, ka manta ni lauta ne kafin na zama alkali, ? Bayan wannan ka manta numberka na niger ne na kira ya shiga ba cod ba komai? Kana ina ne? Domin ina so in sha Allah mu hadu kafin lokacin sallar azahar, ina tare da Wardugu,

Jim ya yi yana jin ba dadi, ya Allah, kowa dai ya san halin da suke ciki da matarsa uwar dansa, koda yake shekara da shekaru its normal,

Fada masa ya yi su hadu a Wardugu Palas, wajen da ya dawo operation irin na da,

Wardugu kam gum da baki, bai ce komai ba ya bi bayan Gukunni cikin motarsa da bodyguard dinsa biyu suka daga sai wajen da yake ainahin wajensa,

Murmushi Marahut yake tunda ya gama magana, ya dubi Wardugu ya ce" kana son ta kennan?

Wardugu ya hade fuskarsa ya kawar da kansa irin ba shi ya kawo maganar ba,

Marahut ya girgiza kai yana murmushi ya ce" mai hali, baya daina halinsa!

Honorable, kana nufin, ba zaka juya chaina a gobe ba sai an daura auren nan? Baka gudun rigimar Ayyansu? Ita yarinyar shin tana so?

Gukunni ya ce" ina tunanin su za.aiwa alfarma!

Marahut ya sada kansa,
Agogon hannunsa ya duba, sannan ya mike ya ce" karfe 2 ka zo da sadaki saifa millions arba.in. ka same mu a masalacin Elhaj Murtala ,

Yana gama fada ya mike ya shige ciki inda Gukunni baki bude ya mike ya bi bayansa yana fadan wani irin Millions 40 sai kace wata yar gwal ko wata budurwa?

Wardugu kam wani tsadaden murmushi ne ya saki daga zaunen da yake, yau ranar Asabar, 5 ga watan Jun , rana ta raba tsaka zai malaketa,

Jama.ar da suka halarci sallar azahar suka shaidi daurin auren, Daurin auren *WARDUGU MARAHUT* da *AGAISHAT ALGABITTT* bisa sadaki Millions 40 cefa ladakan, ,

Zamanin whatsup, zamanin android , nan da nan mutane suka fara watsa wannan lamari, inda ake yayatun buzuwa ce, suna yi har fiye da haka, Buzuwa ce General ya santale,

Nan da nan yan jaridu suka fara neman Wardugu cikin birnin Niamey,

Yan mata suka fara doka waya suna neman jin karin bayani,
Gidan redio ta saki labari,

Walyn,
Walyn dake kwonce tana shating ta ga kanwar kawarta ta dora saman status cewa" kaka kara kaka, wai da gaske ne ko da wasa? General ya bada sadakin buzuwa million 40 arma ta zama tasa? General wardugu ya watsa kuraye, abin son jinma ana cewa Black ce!....?

Ta karanta ya fi a girga , kafin kamar hadin baki, kira ne, mesage ne whatsup ne, facebook ne? Abu ya zama a lokaci daya ya shiga shigowa,

Bata gama tantancewa ba mahaifiyarya ta shigo dakin asibitin a fujajan ta ce.............

Ayya hankalinta ne ya gama tashi a lokacin da ta ji wannan bayani ta bakin Marahut da ya yi kiranta da bakuwar number ya yi mata murna da fada mata ya daurawa dansa aure da yarta ga sadakin nan zai zo ya kawo da kansa idan tana so ta saka a hana shi shiga!

Wardugu,
A lokacin da ya ji eh lale Allah ya damka masa igiyoyin jan ragamar rayuwarta ya mike ya shiga motarsa da kayan jikinsa na tun jiya da bai samu ya tsaya bama bale ya canza,

Zama ya yi ya jinginar da kansa, idannuwansa ya lumshe sai kuma Walyn ta fado masa a rai,
Wani tausayinta ne ya ji ya dirar masa, dan ya sani ne Allah kawai zai tsayar da ita kan saka kanta a uku,

Motarsa ya tayar da kansa ya harbata bakin titi da gudun balaki......

Bai zame ko.ina ba sai clinik din da Walyn take,

A nitse ya kashe motar ya zare kys din ya fice daga ciki,

Taku yake cikin nutsuwa da ingarma, ba zaka taba fahimtar halin da yake ciki ba har ya tura kofar ya bude,

Ido hudu suka yi shi da ita, tana zaune ta ziro kafafuwanta kasa, ta ja rigar clinik din can saman cinyoyinta, kanta bude gashin kanta ba ribom, ta tsurawa waje daya ido domin jinta da ganninta ne suka fauke na dan lokaci,

A hankali ya karasa kusan gadon da take zaune ya cire takalmin kafarsa ya dan saci duban mahaifiyarta ya ga tanai masa wani kallon da ba zai gane na kyama ne? Na tsana ne? Ko na deception bane!
Hannunta ya kamo yana dubanta,
Murya cinkushe ya ce" Walyn,

Idannuwanta kawai binsa suke da kallo, Namiji? Bata taba sannin kalmar da zata yi ajalinta bane sai yau! Namiji Namijinma wanda ta fi aminta da shi, Kishiya? Kishiya Wardugu ya yi mata? Ita Walyn? Me ta rage shi? Menene? Ita ya wulakanta a idon duniya? Ita ya wulakanta a dangi? Yanzu uban wa zata yiwa daga kai da jiji da kai a gari? An taka dokar al.adunta ma, an tarwatsa takamarta ma, an ci amanarta, dan me? Me ya yi zafi? Me na rasa? Ban taba haihuwa ba....hasalima ban bar kwan ya zama gudaji ba na watsa shi, du domin ka???

Muryarta na rawa ta ce" Wardugu, dandan me? Sex ne ko? Dan wannan ka tozarta ni? Nawa bai isheka ba???
Chapter 94 · 0% Book details