Sashe 68
Bak'a Ce Part 1 Complet Hausa Novel · about 8 min read
Ya mace zata zubar da cikinka wai a zuwan ba zata haihu da wuri da kai ba dan tana maka tsananin son da ba zata so ka auri wata ba?
Ta iya zubar da gudan jininta, dan sunna dan tsaninin kishi ya zata dauki lamarin zaka auri wata?
Danma a haka wai tana shayinsa, du haukanta tama tsoron su hade daga ita sai shi idan ta yi masa laifi, aman lamarinta na saka Ayya a shakun jin wai wardugu zai dubi wata bare ya aureta,
Sai dai ina, ba zata shiga hakinsa ba , ba zata shiga ba, ya isa haka, harda laifinta irin yanda take tsawata masa idan ya dace ya hukuntata, ta samu damar da take sakawa ranta ita daya kwal ta ishe shi ko kowa ya rasa,
Ajiyar zuciya ta sauke tana kawar da kanta, zatai ta adu.a, aman ko wacece zai aura zata hadu da fitinar matarsa sai dai idan ita dinma wata kwaron kanta ce!
Gidan su Anna
Tunda suka sauka a gidan su Anna ba rajar banza da ba za.a yi baki ba, sun zo yi masu barkar gannin y'arsu,
Abin har mamaki yake baiwa su Gaishata, sai dai duba da irin mukami da datijantakar tsohon gidan ya tarawa kansa daraja,
Wani abu dake baiwa gaishata mamaki, shi ne irin kirarin da ake yiwa mahaifiyar Anna,
Sai dai zaman da ta yi da ita na dan lokacin nan ya saka ta gane ba wai likawa aka yi ba, ta cancanci hakan ne,
Ita bata taba gannin mace irinta ba, a duniya duda tsufan da ya kamata ko me take, ko da wa take, mijin nan nata yana gaba da komai,
Wato wani irin kulawa, wani irin cancanna, wani irin salo da take bazawa a cikin gidan ba ruwanta da jikokinta ki yayanta ko wasu sirikai, ta iya tafia da mijinta a gaban kowa, kuma cikin ikon Allah du irin zafinsa idan ya kwashi zafi ya fice zatai murmushi ne idan ya je ya dawo ta bi bayansa zai fito kamar ba shi ba,
Har wani kirari take masa namijin mazaje ja gaban Hatimi aban Herde da Allatchi,
Zaka ga yana wani kayatancen murmushi,
Ko yanzu gaba ta saka Gaishata bayan ta gama lumdarta da turare, domin ita ke kula da harkar wankan jegonta koda yaushe tana daka tana lumdeta da shan zafin daki ta dubeta ta ce" ni kishiyoyinki nawa?
Gaishata ta ce" biyu,
Yara ne suma kamarki ko sun manyanta?
Gaishata ta ce" dayar na fita, dayar kuma ta manyanta,
Hatimi ta gyada kanta ta mike ta dauko wani kindirmo da ta dada ta zuba wani ruwan itace da ta dafa da kanta ta bata ta ce" ya mu.amalarki da su? Irin zumunta?
Gaishata ta ce" a gaskiya bama fada kuma bama shiga harkar juna,
Hatimi ta ce" me yasa bakwa shiga harkar juna? Kina nufin a cikin gida daya kuke aman ba ruwan kowa da kowa? Irin rayuwar idan wani na cikin wani hali ma ba ruwan dan uwansa da shi?
Gaishata ta ce" da na je na tarar da ita bata taba nunan hanyar zumunci ko akasin hakan ba, yayanta basa zuwa inda nake, hakan ya sa nima nake rayuwana, da ya kara aurema itama da ta zo bata shiga sabgarmu,
Hatimi ta tsaya tana dubanta da mamaki, kafin take cewa" kuma ya shi yake daukan haka?
Gaishata ta ce " yakan yi jajen wani lokacin, aman wani lokacin baya nunawa,
Hatimi ta girgiza kanta ta ce" bakwa tsoron Allah? Kishin ne haka ko hauka? Ku baku yi zubde zubden hauka ba , aman kuna zama tamkar masu gaba da juna? Me hakan ke nufi?????????
Gaishata ta ce" ni ban san ya zan yi ba,
Akoy lokacin da ta haihu na je barka, ina shiga aka rufe jaririn, ni kuwa da na dawo ban koma ko zaman wuni ba,
Kuma yanzu da na haihu cikinsu ba wanda ta leko ni, har ranar sunna, sai ana gobe zamu taho na ji hayaniyarsu suna fadan dan me zai biyo mu, shi kuwa ya fada masu ba zai iya zama ba
Ajiyar zuciya ta sauke ta umarceta da ta shiga wanka, ita kuma ta fita ta je ta dauki waya suka gama waya da wanda ta saka a kawo sabin kayan daki dan canzawa gaishata idan ta tashi komawa, sannan ta je tsakar gida ta fice yan matan biyu wato su mariama suna ta dariya da aku suna magana yana maimaitawa,
Su Herde ta gani zaune suna hira, kanta ta girgiza ta ga halamar idan ba da gaske aka yi ba zasu daina tuno da suna kukannan ba,
Da kyar ta ga mijin nata da jikansa a cinyarsa dan jariri ya rungume, ga kuma sirikin suna zaune saman tabarmar leda kasan inuwar mangwaro suna hira a nitse,
Salama ta yi masu ta samu waje ta zauna,
Nan sarki ya mike dan basu waje
Hatimi ta dube shi ta ce" aa mai gida, ai ni da san samu na yi wajenka na zo,
Dawowa ya yi ya zauna yana dubanta,
Ajiyar zuciya ta sauke kafin ta ce" ban san ta inda zan fara ba, aman zan so ka sani ba kawo min hirar gidanka ta yi ba hasalima mamaki ne ya ishe ni gannin garinku akoy network, kuma yarinyar nada kishiyoyi, sai dai ban ga suna wani kiran juna ba, duda da wuya idan basu da waya?
Ka yi hakuri, ina jin yaran nan har tsokar jikina, a yanzu da ta yi nesa da yan uwanta bata da kowa sai su sai kai a garin, rayuwa zai mata wahala idan ya kasance ba wani zumunci ko fahimtar junna tsakanin su,
Menene matsalar? Zan so a gane a yi masalaha tsakaninsu, dan kai namiji ne, ba koda yaushe zaka zauna ka yi hira da ita ba, duba da ba ita kadai keda kai ba, ga fita nema da sauransu.
Ajiyar zuciya sarki ya sauke, a nitse ya ce" an samu matsalar ne tun daga aurenta, ita ta nuna ba zata zauna da kishiya ba , ni kuwa na jima daman ina son na samu aurenta, shine na yi rantsuwar sai na rabu da ita idan ta kawo min wani abin a cikin maganar aurena,
Shi ne tace ba komai na je na auro yar gwal, ita kuwa zata zuba mana ido ta ga ta zaman lafia,
Hatimi ta jinjina kanta tana dubansa ta ce" eyah,
Ga tushen fadan,
Ka yi hakuri d'ana, aman na tabata kana nuna wani fifiko tsakanin su?
Gukunni dake dubansu ya kai dubansa wajen sarkin ya ce" aboki, shin ka kasance mai nuna wani wariya tsakanin matanka wanda har matan naka suka fahimta suka san ka fi son wani da wani tsakanin su??
Kansa ya sada ya shiga tunani kafin yake dagowa ya ce
🐫🐫🐫🐫 *BAK'A CE* 🐫🐫🐫🐫
https://www.facebook.com/Idan-rana-ta-fito-writers-association-114558343535568/?referrer=whatsapp
*☀IDAN RANA TA FITO WRITER'S ASSO🌤* ____________________________________________
*Fad'akar da al'umma tare da nishad'antar da masoya shine fatanmu*😘🤝🏻😘
Na
*SAJIDA*
6️⃣3️⃣
Ya jima kafin yake cewa" ni babu wani madaukakin bambanci da nake nunawa a tsakaninsu, abu daya dai na sani idan sako ne zuwa wajena fada du wace ya kasance dole sai na ji a lokacin da nake zaune da talakawa sai an bi ta kanta, wannan kuma dalilina shi ne, zata shigo min da nutsuwa koda kuwa sakon mai firgitarwa ne,
Abu na biyu, sababin suturuna na ajiye a wajenta, dan ita ke kilace min ta yi masu wajen da ba mai zuwa sai ni,
Sai idan zan yi bakin kunya, ita ke girkinsu dan ta iya girkin sannan takan sako mini a kwanon da ba zan ji kunya ba
Ni kam iya abubuwan da zan iya tinawa kennan, sai wa.inda a rashin sani ne,
Hatimi ta gyada kanta ta ce" wa ke saya masu kwanoni? Shin kai ne? Idan kai ne kana saya kowace iri guda?
Ka taba baiwa wata cikinsu ajiyar kayan aka bata? Ka nuna mata dalilin da zai sa zaka kwashe bata kula ba?
Sai maganar tarar da kai wajen taronka da talakawan garinka, shin watansu ta taba zuwar maka a hargitse ne? Ta tayar maka da hankali? Ka zaunar da su ka nuna masu ga yanda kake so su kasance idan zasu je wajenka basu kiyaye ba?
Ajiyar zuciya ya sauke ya ce" kwanoni ni ke sayan masu du idan na shiga birni,
Nasu na bacewa ne da wuri sai su ce wai yara ke lalatawa, kuma ba ruwansu ba zasu nemi gyarawa ba idan na yi bakon sai dai na ga wani abin tashin hankali cikin har hada min marfi ake daban da kwano,
Sannan gaskiya ban taba zaunar da su na fasa masu su kilace min suturuna ba, a ganina irin girman miji a gurin matarsa har sai na fada masu haka? Da girmansu da komai? Ita ai ba fada mata na yi ba,
Sannan a gaskiya sau biyu aka yi irin ina cikin mutane, idan abin kuka ne za.a shigo mini da gudu jiki fata fata a ja a tsaya an ci damara a gwaza kuka ana jijiga , har sai na yi rarashi da roko kafin a gwaza min abinda ke faruwa, hakan ya saka na soke tarar da ni fada ,
Murmushi ta yi ta ce " ka yi hakuri mai martaba, mace du girmanta idan ta takarkare ta tafka maka wani abin wani lokacin sai ka yi mamaki,
Kar yannayin da Gaishata ke nunawa na kimtsi ya saka ka tunanin ita kadai xe kimtsatsiya a cikin matanta ko mai tarbiya, idan fa tana haka ne dan bata fara haihuwa ba?
Ta iya zubar da gudan jininta, dan sunna dan tsaninin kishi ya zata dauki lamarin zaka auri wata?
Danma a haka wai tana shayinsa, du haukanta tama tsoron su hade daga ita sai shi idan ta yi masa laifi, aman lamarinta na saka Ayya a shakun jin wai wardugu zai dubi wata bare ya aureta,
Sai dai ina, ba zata shiga hakinsa ba , ba zata shiga ba, ya isa haka, harda laifinta irin yanda take tsawata masa idan ya dace ya hukuntata, ta samu damar da take sakawa ranta ita daya kwal ta ishe shi ko kowa ya rasa,
Ajiyar zuciya ta sauke tana kawar da kanta, zatai ta adu.a, aman ko wacece zai aura zata hadu da fitinar matarsa sai dai idan ita dinma wata kwaron kanta ce!
Gidan su Anna
Tunda suka sauka a gidan su Anna ba rajar banza da ba za.a yi baki ba, sun zo yi masu barkar gannin y'arsu,
Abin har mamaki yake baiwa su Gaishata, sai dai duba da irin mukami da datijantakar tsohon gidan ya tarawa kansa daraja,
Wani abu dake baiwa gaishata mamaki, shi ne irin kirarin da ake yiwa mahaifiyar Anna,
Sai dai zaman da ta yi da ita na dan lokacin nan ya saka ta gane ba wai likawa aka yi ba, ta cancanci hakan ne,
Ita bata taba gannin mace irinta ba, a duniya duda tsufan da ya kamata ko me take, ko da wa take, mijin nan nata yana gaba da komai,
Wato wani irin kulawa, wani irin cancanna, wani irin salo da take bazawa a cikin gidan ba ruwanta da jikokinta ki yayanta ko wasu sirikai, ta iya tafia da mijinta a gaban kowa, kuma cikin ikon Allah du irin zafinsa idan ya kwashi zafi ya fice zatai murmushi ne idan ya je ya dawo ta bi bayansa zai fito kamar ba shi ba,
Har wani kirari take masa namijin mazaje ja gaban Hatimi aban Herde da Allatchi,
Zaka ga yana wani kayatancen murmushi,
Ko yanzu gaba ta saka Gaishata bayan ta gama lumdarta da turare, domin ita ke kula da harkar wankan jegonta koda yaushe tana daka tana lumdeta da shan zafin daki ta dubeta ta ce" ni kishiyoyinki nawa?
Gaishata ta ce" biyu,
Yara ne suma kamarki ko sun manyanta?
Gaishata ta ce" dayar na fita, dayar kuma ta manyanta,
Hatimi ta gyada kanta ta mike ta dauko wani kindirmo da ta dada ta zuba wani ruwan itace da ta dafa da kanta ta bata ta ce" ya mu.amalarki da su? Irin zumunta?
Gaishata ta ce" a gaskiya bama fada kuma bama shiga harkar juna,
Hatimi ta ce" me yasa bakwa shiga harkar juna? Kina nufin a cikin gida daya kuke aman ba ruwan kowa da kowa? Irin rayuwar idan wani na cikin wani hali ma ba ruwan dan uwansa da shi?
Gaishata ta ce" da na je na tarar da ita bata taba nunan hanyar zumunci ko akasin hakan ba, yayanta basa zuwa inda nake, hakan ya sa nima nake rayuwana, da ya kara aurema itama da ta zo bata shiga sabgarmu,
Hatimi ta tsaya tana dubanta da mamaki, kafin take cewa" kuma ya shi yake daukan haka?
Gaishata ta ce " yakan yi jajen wani lokacin, aman wani lokacin baya nunawa,
Hatimi ta girgiza kanta ta ce" bakwa tsoron Allah? Kishin ne haka ko hauka? Ku baku yi zubde zubden hauka ba , aman kuna zama tamkar masu gaba da juna? Me hakan ke nufi?????????
Gaishata ta ce" ni ban san ya zan yi ba,
Akoy lokacin da ta haihu na je barka, ina shiga aka rufe jaririn, ni kuwa da na dawo ban koma ko zaman wuni ba,
Kuma yanzu da na haihu cikinsu ba wanda ta leko ni, har ranar sunna, sai ana gobe zamu taho na ji hayaniyarsu suna fadan dan me zai biyo mu, shi kuwa ya fada masu ba zai iya zama ba
Ajiyar zuciya ta sauke ta umarceta da ta shiga wanka, ita kuma ta fita ta je ta dauki waya suka gama waya da wanda ta saka a kawo sabin kayan daki dan canzawa gaishata idan ta tashi komawa, sannan ta je tsakar gida ta fice yan matan biyu wato su mariama suna ta dariya da aku suna magana yana maimaitawa,
Su Herde ta gani zaune suna hira, kanta ta girgiza ta ga halamar idan ba da gaske aka yi ba zasu daina tuno da suna kukannan ba,
Da kyar ta ga mijin nata da jikansa a cinyarsa dan jariri ya rungume, ga kuma sirikin suna zaune saman tabarmar leda kasan inuwar mangwaro suna hira a nitse,
Salama ta yi masu ta samu waje ta zauna,
Nan sarki ya mike dan basu waje
Hatimi ta dube shi ta ce" aa mai gida, ai ni da san samu na yi wajenka na zo,
Dawowa ya yi ya zauna yana dubanta,
Ajiyar zuciya ta sauke kafin ta ce" ban san ta inda zan fara ba, aman zan so ka sani ba kawo min hirar gidanka ta yi ba hasalima mamaki ne ya ishe ni gannin garinku akoy network, kuma yarinyar nada kishiyoyi, sai dai ban ga suna wani kiran juna ba, duda da wuya idan basu da waya?
Ka yi hakuri, ina jin yaran nan har tsokar jikina, a yanzu da ta yi nesa da yan uwanta bata da kowa sai su sai kai a garin, rayuwa zai mata wahala idan ya kasance ba wani zumunci ko fahimtar junna tsakanin su,
Menene matsalar? Zan so a gane a yi masalaha tsakaninsu, dan kai namiji ne, ba koda yaushe zaka zauna ka yi hira da ita ba, duba da ba ita kadai keda kai ba, ga fita nema da sauransu.
Ajiyar zuciya sarki ya sauke, a nitse ya ce" an samu matsalar ne tun daga aurenta, ita ta nuna ba zata zauna da kishiya ba , ni kuwa na jima daman ina son na samu aurenta, shine na yi rantsuwar sai na rabu da ita idan ta kawo min wani abin a cikin maganar aurena,
Shi ne tace ba komai na je na auro yar gwal, ita kuwa zata zuba mana ido ta ga ta zaman lafia,
Hatimi ta jinjina kanta tana dubansa ta ce" eyah,
Ga tushen fadan,
Ka yi hakuri d'ana, aman na tabata kana nuna wani fifiko tsakanin su?
Gukunni dake dubansu ya kai dubansa wajen sarkin ya ce" aboki, shin ka kasance mai nuna wani wariya tsakanin matanka wanda har matan naka suka fahimta suka san ka fi son wani da wani tsakanin su??
Kansa ya sada ya shiga tunani kafin yake dagowa ya ce
🐫🐫🐫🐫 *BAK'A CE* 🐫🐫🐫🐫
https://www.facebook.com/Idan-rana-ta-fito-writers-association-114558343535568/?referrer=whatsapp
*☀IDAN RANA TA FITO WRITER'S ASSO🌤* ____________________________________________
*Fad'akar da al'umma tare da nishad'antar da masoya shine fatanmu*😘🤝🏻😘
Na
*SAJIDA*
6️⃣3️⃣
Ya jima kafin yake cewa" ni babu wani madaukakin bambanci da nake nunawa a tsakaninsu, abu daya dai na sani idan sako ne zuwa wajena fada du wace ya kasance dole sai na ji a lokacin da nake zaune da talakawa sai an bi ta kanta, wannan kuma dalilina shi ne, zata shigo min da nutsuwa koda kuwa sakon mai firgitarwa ne,
Abu na biyu, sababin suturuna na ajiye a wajenta, dan ita ke kilace min ta yi masu wajen da ba mai zuwa sai ni,
Sai idan zan yi bakin kunya, ita ke girkinsu dan ta iya girkin sannan takan sako mini a kwanon da ba zan ji kunya ba
Ni kam iya abubuwan da zan iya tinawa kennan, sai wa.inda a rashin sani ne,
Hatimi ta gyada kanta ta ce" wa ke saya masu kwanoni? Shin kai ne? Idan kai ne kana saya kowace iri guda?
Ka taba baiwa wata cikinsu ajiyar kayan aka bata? Ka nuna mata dalilin da zai sa zaka kwashe bata kula ba?
Sai maganar tarar da kai wajen taronka da talakawan garinka, shin watansu ta taba zuwar maka a hargitse ne? Ta tayar maka da hankali? Ka zaunar da su ka nuna masu ga yanda kake so su kasance idan zasu je wajenka basu kiyaye ba?
Ajiyar zuciya ya sauke ya ce" kwanoni ni ke sayan masu du idan na shiga birni,
Nasu na bacewa ne da wuri sai su ce wai yara ke lalatawa, kuma ba ruwansu ba zasu nemi gyarawa ba idan na yi bakon sai dai na ga wani abin tashin hankali cikin har hada min marfi ake daban da kwano,
Sannan gaskiya ban taba zaunar da su na fasa masu su kilace min suturuna ba, a ganina irin girman miji a gurin matarsa har sai na fada masu haka? Da girmansu da komai? Ita ai ba fada mata na yi ba,
Sannan a gaskiya sau biyu aka yi irin ina cikin mutane, idan abin kuka ne za.a shigo mini da gudu jiki fata fata a ja a tsaya an ci damara a gwaza kuka ana jijiga , har sai na yi rarashi da roko kafin a gwaza min abinda ke faruwa, hakan ya saka na soke tarar da ni fada ,
Murmushi ta yi ta ce " ka yi hakuri mai martaba, mace du girmanta idan ta takarkare ta tafka maka wani abin wani lokacin sai ka yi mamaki,
Kar yannayin da Gaishata ke nunawa na kimtsi ya saka ka tunanin ita kadai xe kimtsatsiya a cikin matanta ko mai tarbiya, idan fa tana haka ne dan bata fara haihuwa ba?