Sashe 29
Bak'a Ce Part 1 Complet Hausa Novel · about 8 min read
Da sauri saurayin ya tashi ya zauna sai sasada kai yake tamkar ya yi karya gaban sarki, tsoro yake a ransa domin a gaban idonsa akaiwa wata dukan tsiya wanda ya sa har ta sume dan kirikiri ta yi ikirarin ita ko wacece ta tofar da yawu ta dura ashar ta ci alwashin gyatiminta zai zo ya fitar da ita har sai uban gidansu Wardugu ya bata hakuri hakan ya sa su kuwa suka nuna mata da gidan maza ta shigo ba gidan yara ba, suka murza kwonji a jikinta har ta some, labarin da ya kaiwa Wardugu da ya fito a gaban mutanen nan na cel ya zuba mata ruwa da kansa wanda hakan ya farfado da ita, sai dai tana tashi ya wanka mata wani marin da ya mayar da ita duniyar suma sannan ya nunata da yatsa ya ce" ban so tonawa kowa asiri ba shi yasa na saka aka shigarmin da iyayenku daga wancen dakin wanda ba wanda zai gane in an shigo da kai wanene mahaifinka kuma me ka aikata ba, sai gashi kin tonawa mahaifinki asiri a matsayinsa na dan siyasa kin kama sunansa har kin nuna mana halin kodin! Dole mu kai kararki wajen alkali kin zagi soji!
Haka aka kwasheta aka jefata cikin cel din ya koma ya ci gaba da aikinsa dan haka ne ya sa wannan saurayin kamar ya kwonta dan kadabi,
Wardugu ya ce" yaya sunanka?
Saurayin ya kalo shi kadan ya sada kai ya ce" sunana Murtala Tasiu,
Wardugu ya gyada kai ya ce" tun yaushe kake zuwa wardugu place? Kai da wa kuke zuwa? A nawa kuke biyan kudin shiga? Du sati sati kuke zuwa? Da yan mata kuke zuwa?
Murtala ya ce" ba.a fi shekara biyu ba,,
Ni da dan gidan Elhaji Dahiru muke zuwa,
Aa ba kowani sati ba dan kudin shigan da muke biya shima ba kulun yake da shi ba jika goma goma, sannan in mun shiga ga kudin kashewa , aa iya mu muke zuwa a can muke haduwa da yan mata kowani sati akoy a ciki,
Wardugu ya tsare shi da ido ya ce " tun daga bakin lokacin ka fara busa kodin?
Murtala ya shiga raraba ido, ya daga hannu zai fara rantse rantse Wardugu ya ce" murtala, ka fada mini gaskiya mai yiwuwa ka samu sasauci!
Murtala ya ce" oga, ka rufa mani asiri dan girman Allah, mahaifina gajiyaye ne, sai na bi abokin nan nawa yake bani wani dan abin na je na ciyar da mahifina da kanwata, kanwata bata gani, mahaifina kuwa ya tsufa, ba a son raina nake saka kafata wajen nan ba,
Wardugu ya ce" ban tambayeka labarinka ba Murtala, ban yi niyar wulakanta ba ina rokonka kar ka wulakantani, kar ka kawo mani shirme a nan , da farko dai du idan ka ga soji rikeken dan tasha ne domin tashanci koya mana ake mu shanye sai dai muna aiki da shi ne kan tsari, na jima a aikina hakan ya saka ana yi min karya nake ganewa, ka bani amsata ko mu baje basirar rainin hankalin ni da kai!.............
🐫🐫🐫 *BAK'A CE*🐫🐫🐫
Na *SAJIDA*
*بسم الله الرحمن الرحيم*
____________________________________
*🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
____________________________________
3️⃣1️⃣
Da sauri Murtala ya ce" Eh eh , tun daga lokacin da muka je abokina ya siya ya saka na taba tun daga lokacin nima nake sha ,
Wardugu ya shiga gyada kai ya ce" kana iya fita,
Dan mikewa ya yi, sai ya mike sai ya dan duduka sai da wani soja ya shigo ya finciko shi ya mayar da shi cel,
Da mijin Auntyn walyn aka shigo,
Mutun har mutun, sai sasada kai yake na kunya,
Warsugu ya tsare da da ido, wai tun a nan duniya ka kasa hada ido da mutanen da basu baka ko cin wuni daya ba, ya zaka kare da wanda ya haliceka ya baka dukiya dan gannin ya zaka tafiyar da ita, ya ara mata lafia, gani da ji, ya baka ikon motsi, ya baka damar magana, ya kaika kasar da ba yake yaken yu da kulun wa.inda zasu iya tayar maka da hankali , ya baka isashen lokaci dan kawai ka bauta masa ka yi masa biyaya, sai gaka tsofai tsofai a gidan badaka tare da yar shilar yarinya ta tube kusan zindir tana maka rawa tana ciyar da kai gasashen kifi, shine zakana wani sada kai a gabana kai ga cikenken dan iska! Du wardugu ke jifansa da wani matsiyacin kallo sannan yana ayyana du haka a ransa,
Wardugu ya ce" ya sunanka malan?
Mijin aunty da mamaki ya dago yana kallon wardugu ya ce" haba haba wardugu, ai ko me ake a san na gida, a fitar da na gida, ka yi hakuri kure na aikata ba zan kuma ba , ka salame ni na koma ba tare da wani bama ya ji abin kunya ne ace ka rufe mijin kanwar babar matarka!
Baki wardugu ya dan daga na mamaki, ka ji wani dogon bayani wai mijin kanwar babar matata,
Kai ya girgiza a ransa ya yi murmushi, a fili ya kuma furta" ya sunanka malan!
Yana mai dagowa da yanayin dakewa,
Mijin auntyn walyn nan ya fara zufa, yana gagawar magana ya ce" tototo, sunana Lawali , Elhaji lawali,
Wardugu ya ce" me ya kai ka Wardugu place? Kai da wa ka je? Me ka je yi? Tun yaushe ka fara zuwa? Me ka lura ana yi a wannan waje?
Lawali ya ce" ni kam wannan waje na je ne bisa tsautsayi da rabon a yi, domin dai yarinyar nan na so na aura sai take shaida min na kaita mu sha iska, to da muka je shikenan sai muka mayar da wajen wajen zuwanmu lokaci zuwa lokaci yanzun dai an kai shekara uku,
Sannan a wannan wajen gaskiya na lura ana abubuwan da bai dace irin ahaye shaye, wannan da ka ganni tana yi wai karamin ne, eh wanda muke yi shine karamin ba Allah ja da kwana....
Ya karashe yana jinjina
Wardugu ya jinjina kai, ya ce" lawali kada daga Kokin ne?
Da sauri ya dago yana duban wardugu, ya ce" bilahilazi ban taba ba, ai ni ko warinta na ji juwa ke kayar da ni, ka rufa mani asiri rashin jina bai kai can ba,
Wardugu ya dago yana dubansa, wai rashin jinsa, kai ya girgiza da hannu ya yi masa nuni da ya fita,
Yana kokarin kara magiya Marahut ya shigo inda sojan nan ya biyo bayansa yana dan kame kame ya rasa me zai yi, su dai ba wanda bai san oga Marahut mahaifin uban gidansu ba, shi ya isa ya masa iyaka ne? Tun daga babar kofa ya samu shigowa ya ratso du zone na control ba.a hana shi ba sai shi tal dake tsaye dan kula da bude kofa da kuma rufewa da kyau ne zai hana shi shigowa?
Kallon Lawali Marahut ya yi kafin yake girgiza kai yana murmushi daga cikin rawaninsa,,
Kai sade Lawali ya fice domin ya ji kunyarsa ainun
Marahut ya bi tsararen tankamemen office dan nasa, bMarahut ya ce" ya aka yi ka canza kanshin turarenmu ne Wardugu? Kuma ya aka yi ba hotona a office dinka bayan kai din dan halal ne koda shege ai ado yake da ubansa bale dan halal ,
Wardugu dake ta cika takardu yana dan dana laptop bai ce da shi ci kanka ba,
Marahut ya ce" Warsugu Abanka ne fa ni ? In ba ruwanka da mutane su ga kana min haka ba ruwanka da Allah ne??
Wardugu ya ajiye biron dake hannunsa ya dan shafa kansa ya dago da kallonsa wajen mahaifinsa wanda a kamaninsu haske ne kadan ya dan fi shi domin farin wardugu ba irin cancan din nan bane,
Warsugu ya ce" Aban Wardugu ra.ayi ne ya sa na daina anfani da turaren da ka sanni da shi, sannan ni ba mace bane da zan kawo hotonka office na buga, kuma shegema mutun ne!
Murmushi marahut ya yi ya karasa wajen kujera ya zauna ya ce" to ka fido mani matata mu tafi gida Wardugu,
Wardugu ya yi murmushi a bayane shima ya ce" ba zan so shakar iskar da kuke shaka ba ko na second daya, sai dai ya zama dole ne, matarka mai laifi ce
Meye laifinta wardugu? Me ta yi da tsanani haka? Ka san yara da kin ji suke,aman ai koma me ta yi ina gannin sai mu kashe mu birne abinmu a tsakaninmu ko wardugu? Marahut ya fada yana dubansa
Wardugu ya ce" zan so haka, sai dai ka ga rashin jin nata ne ya yi kamari, tana shigo da kwaya ne tana siyarwa wannan ba boyayiyar shaida bace, abinda nake bincike kawai na samu hanyar da take shigo da ita ko wanda ke bata sai na mika su kotu koda kuwa *kai ne*, sai dai ban san ba yin hakan ko Allah zai kama ni da shi?
Da sauri marahut ya ce" Quoi? (What?), wani irin kwaya? A Wardugu place din? Innalilahi wa.ina ilaihi raj.une, wardugu ka kara mani haske a lamarin nan
Wardugu da ya ji ya dan samu sasauci, domin a sama yake, jininsa a saman akaifa, tsoro yake kar a je rinjayar nata ya kai ta saka Marahut a wannan harka? Aman yanzu ko ba komai ya ji dan sanyi a ransa dan kuwa har gobe da sunnan mahaifinsa yake anfani,
Wardugu ka fada mani mana, Marahut ya fada yana dubansa da yannayin serius
Wardugu ya yi umarnin a kawo AISATA,
Shigo da ita aka yi, dare daya tak du ta fara fita hayacinta abinka da wada ya saba da hutu,
Tana gannin Marahut ta sauke ajiyar zuciya mai nauyi kafin da sauri ta nufi wajensa ta saki kukan kirsa,
Tana kukan ta ce" ka ga abinda Wardugu ya yi mini? Wannan wani irin tsana da cin mutunci ne? A gaban jama.a ya saka mini anker tamkar wada na yi sata, ai a tunanina ya dace komai ya fice tsakaninmu ko me na yi sai ya hukunta ni a gida ba wai a gaban duban mutanen da zasu yi min dariya ba,
Haka aka kwasheta aka jefata cikin cel din ya koma ya ci gaba da aikinsa dan haka ne ya sa wannan saurayin kamar ya kwonta dan kadabi,
Wardugu ya ce" yaya sunanka?
Saurayin ya kalo shi kadan ya sada kai ya ce" sunana Murtala Tasiu,
Wardugu ya gyada kai ya ce" tun yaushe kake zuwa wardugu place? Kai da wa kuke zuwa? A nawa kuke biyan kudin shiga? Du sati sati kuke zuwa? Da yan mata kuke zuwa?
Murtala ya ce" ba.a fi shekara biyu ba,,
Ni da dan gidan Elhaji Dahiru muke zuwa,
Aa ba kowani sati ba dan kudin shigan da muke biya shima ba kulun yake da shi ba jika goma goma, sannan in mun shiga ga kudin kashewa , aa iya mu muke zuwa a can muke haduwa da yan mata kowani sati akoy a ciki,
Wardugu ya tsare shi da ido ya ce " tun daga bakin lokacin ka fara busa kodin?
Murtala ya shiga raraba ido, ya daga hannu zai fara rantse rantse Wardugu ya ce" murtala, ka fada mini gaskiya mai yiwuwa ka samu sasauci!
Murtala ya ce" oga, ka rufa mani asiri dan girman Allah, mahaifina gajiyaye ne, sai na bi abokin nan nawa yake bani wani dan abin na je na ciyar da mahifina da kanwata, kanwata bata gani, mahaifina kuwa ya tsufa, ba a son raina nake saka kafata wajen nan ba,
Wardugu ya ce" ban tambayeka labarinka ba Murtala, ban yi niyar wulakanta ba ina rokonka kar ka wulakantani, kar ka kawo mani shirme a nan , da farko dai du idan ka ga soji rikeken dan tasha ne domin tashanci koya mana ake mu shanye sai dai muna aiki da shi ne kan tsari, na jima a aikina hakan ya saka ana yi min karya nake ganewa, ka bani amsata ko mu baje basirar rainin hankalin ni da kai!.............
🐫🐫🐫 *BAK'A CE*🐫🐫🐫
Na *SAJIDA*
*بسم الله الرحمن الرحيم*
____________________________________
*🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
____________________________________
3️⃣1️⃣
Da sauri Murtala ya ce" Eh eh , tun daga lokacin da muka je abokina ya siya ya saka na taba tun daga lokacin nima nake sha ,
Wardugu ya shiga gyada kai ya ce" kana iya fita,
Dan mikewa ya yi, sai ya mike sai ya dan duduka sai da wani soja ya shigo ya finciko shi ya mayar da shi cel,
Da mijin Auntyn walyn aka shigo,
Mutun har mutun, sai sasada kai yake na kunya,
Warsugu ya tsare da da ido, wai tun a nan duniya ka kasa hada ido da mutanen da basu baka ko cin wuni daya ba, ya zaka kare da wanda ya haliceka ya baka dukiya dan gannin ya zaka tafiyar da ita, ya ara mata lafia, gani da ji, ya baka ikon motsi, ya baka damar magana, ya kaika kasar da ba yake yaken yu da kulun wa.inda zasu iya tayar maka da hankali , ya baka isashen lokaci dan kawai ka bauta masa ka yi masa biyaya, sai gaka tsofai tsofai a gidan badaka tare da yar shilar yarinya ta tube kusan zindir tana maka rawa tana ciyar da kai gasashen kifi, shine zakana wani sada kai a gabana kai ga cikenken dan iska! Du wardugu ke jifansa da wani matsiyacin kallo sannan yana ayyana du haka a ransa,
Wardugu ya ce" ya sunanka malan?
Mijin aunty da mamaki ya dago yana kallon wardugu ya ce" haba haba wardugu, ai ko me ake a san na gida, a fitar da na gida, ka yi hakuri kure na aikata ba zan kuma ba , ka salame ni na koma ba tare da wani bama ya ji abin kunya ne ace ka rufe mijin kanwar babar matarka!
Baki wardugu ya dan daga na mamaki, ka ji wani dogon bayani wai mijin kanwar babar matata,
Kai ya girgiza a ransa ya yi murmushi, a fili ya kuma furta" ya sunanka malan!
Yana mai dagowa da yanayin dakewa,
Mijin auntyn walyn nan ya fara zufa, yana gagawar magana ya ce" tototo, sunana Lawali , Elhaji lawali,
Wardugu ya ce" me ya kai ka Wardugu place? Kai da wa ka je? Me ka je yi? Tun yaushe ka fara zuwa? Me ka lura ana yi a wannan waje?
Lawali ya ce" ni kam wannan waje na je ne bisa tsautsayi da rabon a yi, domin dai yarinyar nan na so na aura sai take shaida min na kaita mu sha iska, to da muka je shikenan sai muka mayar da wajen wajen zuwanmu lokaci zuwa lokaci yanzun dai an kai shekara uku,
Sannan a wannan wajen gaskiya na lura ana abubuwan da bai dace irin ahaye shaye, wannan da ka ganni tana yi wai karamin ne, eh wanda muke yi shine karamin ba Allah ja da kwana....
Ya karashe yana jinjina
Wardugu ya jinjina kai, ya ce" lawali kada daga Kokin ne?
Da sauri ya dago yana duban wardugu, ya ce" bilahilazi ban taba ba, ai ni ko warinta na ji juwa ke kayar da ni, ka rufa mani asiri rashin jina bai kai can ba,
Wardugu ya dago yana dubansa, wai rashin jinsa, kai ya girgiza da hannu ya yi masa nuni da ya fita,
Yana kokarin kara magiya Marahut ya shigo inda sojan nan ya biyo bayansa yana dan kame kame ya rasa me zai yi, su dai ba wanda bai san oga Marahut mahaifin uban gidansu ba, shi ya isa ya masa iyaka ne? Tun daga babar kofa ya samu shigowa ya ratso du zone na control ba.a hana shi ba sai shi tal dake tsaye dan kula da bude kofa da kuma rufewa da kyau ne zai hana shi shigowa?
Kallon Lawali Marahut ya yi kafin yake girgiza kai yana murmushi daga cikin rawaninsa,,
Kai sade Lawali ya fice domin ya ji kunyarsa ainun
Marahut ya bi tsararen tankamemen office dan nasa, bMarahut ya ce" ya aka yi ka canza kanshin turarenmu ne Wardugu? Kuma ya aka yi ba hotona a office dinka bayan kai din dan halal ne koda shege ai ado yake da ubansa bale dan halal ,
Wardugu dake ta cika takardu yana dan dana laptop bai ce da shi ci kanka ba,
Marahut ya ce" Warsugu Abanka ne fa ni ? In ba ruwanka da mutane su ga kana min haka ba ruwanka da Allah ne??
Wardugu ya ajiye biron dake hannunsa ya dan shafa kansa ya dago da kallonsa wajen mahaifinsa wanda a kamaninsu haske ne kadan ya dan fi shi domin farin wardugu ba irin cancan din nan bane,
Warsugu ya ce" Aban Wardugu ra.ayi ne ya sa na daina anfani da turaren da ka sanni da shi, sannan ni ba mace bane da zan kawo hotonka office na buga, kuma shegema mutun ne!
Murmushi marahut ya yi ya karasa wajen kujera ya zauna ya ce" to ka fido mani matata mu tafi gida Wardugu,
Wardugu ya yi murmushi a bayane shima ya ce" ba zan so shakar iskar da kuke shaka ba ko na second daya, sai dai ya zama dole ne, matarka mai laifi ce
Meye laifinta wardugu? Me ta yi da tsanani haka? Ka san yara da kin ji suke,aman ai koma me ta yi ina gannin sai mu kashe mu birne abinmu a tsakaninmu ko wardugu? Marahut ya fada yana dubansa
Wardugu ya ce" zan so haka, sai dai ka ga rashin jin nata ne ya yi kamari, tana shigo da kwaya ne tana siyarwa wannan ba boyayiyar shaida bace, abinda nake bincike kawai na samu hanyar da take shigo da ita ko wanda ke bata sai na mika su kotu koda kuwa *kai ne*, sai dai ban san ba yin hakan ko Allah zai kama ni da shi?
Da sauri marahut ya ce" Quoi? (What?), wani irin kwaya? A Wardugu place din? Innalilahi wa.ina ilaihi raj.une, wardugu ka kara mani haske a lamarin nan
Wardugu da ya ji ya dan samu sasauci, domin a sama yake, jininsa a saman akaifa, tsoro yake kar a je rinjayar nata ya kai ta saka Marahut a wannan harka? Aman yanzu ko ba komai ya ji dan sanyi a ransa dan kuwa har gobe da sunnan mahaifinsa yake anfani,
Wardugu ka fada mani mana, Marahut ya fada yana dubansa da yannayin serius
Wardugu ya yi umarnin a kawo AISATA,
Shigo da ita aka yi, dare daya tak du ta fara fita hayacinta abinka da wada ya saba da hutu,
Tana gannin Marahut ta sauke ajiyar zuciya mai nauyi kafin da sauri ta nufi wajensa ta saki kukan kirsa,
Tana kukan ta ce" ka ga abinda Wardugu ya yi mini? Wannan wani irin tsana da cin mutunci ne? A gaban jama.a ya saka mini anker tamkar wada na yi sata, ai a tunanina ya dace komai ya fice tsakaninmu ko me na yi sai ya hukunta ni a gida ba wai a gaban duban mutanen da zasu yi min dariya ba,