Sashe 30
Bak'a Ce Part 1 Complet Hausa Novel · about 8 min read
Hannunsa ya saka ya dagota daga jikinsa yana dubanta, kadara, Aisata kadara ce mai wutsiya, a dalilin Aisata ya rabu da farin cikinsa da girmansa a idannuwan iyalinsa, maciya ce Aisata, Aisata zinari ce,
A nitse ya ce" me da me kuke aikatawa a Wardugu place?
Aisata ta yi tsam kafin ta shiga cicira ido ta kali dan ta kali uban, cikin yannayin barikinta ta ce" me muke yi kuwa banda neman kudi? A wardugu place ba abinda muke yi,
Wardugu dake rubutu a takarda ya dan yi tsam ya dago ya dube su ya maida kansa ya ci gaba da aiki,
Bai jima ba ya daga wayar office din ya danna kira,
Cikin girmamawa ya gaisar da jujun kafin yake fadin" mai girma na gama nawa binciken, yanzu ana kawo maka takardu ka duba, daga nan na mika maka su kawai ,
Amsa shi ya yi kafin yake kashewa,
Marahut da ya gama fahimtar wayar da Wardugu ya yi shima yana dubansa, cikin yannayin nutsuwarsa dai ya ce" har yanzu baka daina jin haushina kan Aisata ba?
Wardugu ya juyo da sauri, ido ya zazaro baki daya kafin yake mikewa ya tofar da yawu a nan cikin office din ya ce" kan wannan? Ya fada yana nuna aisata,
Ya girgiza kai ya ce" ai koda me daraja ce bata kai na yi anfani da damata dan wulakanta ku ba, ka gane laifi ta yi, idanma baka yarda ba ai kai din oga ne kawai ka je wajen wa.inda zan mikawa takarda idan sun baka matarka ruwansu ni dai ai na tono barnar ko? Ka fi kowa sannin waye wardugu domin kaine mutun na farko da ka rikeni a duniya bayan likitar da ta fitar da ni daga cikin mahaifiyata!
Yana gama fada ya ja kys din motarsa ya dauki gilashinsa ya fice a office din yana mai jin haushin yanda mutane ke magiya kan a bari a ci gaba da yada barna!
Jikin Ayya ne ya yi sanyi bayan korar Agaishat da ta yi, a hankali ta mike ta nufi dakinta tana mai jin wani iri me ya yi zafi harda laifin wani zai shafi wani?
Tana zuwa ta shiga da salama,
Agaishat dake zaune kasa ta dora kanta a gefen gado tana jan carbi da hannunta ta dago da sauri tana kokarin mikewa tana duban Ayya,
Karasawa Ayya ta yi ta riketa ta zaunar da ita gefen gado,
A nitse ta ce" ki yi hakuri yar gidan Ayya, ba zan kuma yi maki irin haka ba ,
Agaishat ta sauke ajiyar zuciya tana dubanta,
Ayya ta ce" bara na baki labarin mu..... na fada maki wacece *AYYA?*, na fada maki waye *MARAHUT a rayiwar Ayya?*, na fada maki wanene *WARDUGU* sannan wani irin girman daraja yake da shi a rayuwar Marahut da Ayya? Yarinta bara na baki labarin da ba kowa ya sani ba................
🐫🐫🐫 *BAK'A CE*🐫🐫🐫
Na *SAJIDA*
*بسم الله الرحمن الرحيم*
____________________________________
*🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
____________________________________
3️⃣2️⃣
labarin Wardugu da tushensa a gajarce
.
........ ..................
Sunana *Zanaba SHAU*, sunnan Mahaifin Wardugu *MARAHUT ELUM*, ni marainiya ce gaba da baya, na taso a hannun kakata ta wajen uwa da ta yi min saura,
Marahut dan gata ne gaba da baya, ya kasance a lokacin anguwarmu daya domin gida uku kawai ke tsakaninmu,
Tun wayona bai gama fahimtar Marahut na sona ba har na gane domin kiri kiri idan na yarda wani lokacin na yi dan shirin atampa na yafa mayafi na fito zai rufe ido ya kora ni yana masifa,
A anguwa ana girmama kakata domin mace ce da ta san girmanta, ba abinda ya shafeta da abin hannunka, ga mutunci ga zumunci,...du juma.a zaki ga an kawowa kakata abinci daga gidajen anguwar nan ciki kuwa harda gidan su Marahut inda mahaifiyarsa shuwa arab ke turowa kakata da gurasa ta kasa, irin wace ake yi a kasa ta ainahin da miya mai dadi harma ki ga an zuba tawa miyar mai magi domin a lokacin an hana kaka shan magi.
Sosai muke soyaya da Marahut, duk da wani lokacin nakan zauna na yi shiru ina tunanin Marahut na so na kamar yanda nake son sa kuwa?
Hakan sai ya tayar min da hankali sosai domin Marahut dai jarumin namiji ne mai cike da abubuwan da mata ke marari har suna kai wawa, harma wani lokaci na kwatanta masa....
Tsareni ya yi da ido kawai, zuwa wani dan lokacin ya mike ya fice abinsa hakan ya haifar min da faduear gaban ko ya yi fushi ya bar ni ne?
Kwana biyu tsakani na dawo daga makarantar dare islamiya da nake zuwa a kusa da mu na tarar da kakata zaune tana jan carbinta da rufarta bata kwonta ba, ba kamar sauran lokutan ba,
Da sasarfa na karasa wajenta dan gannin abinda ke damunta sai dai ina zuwa ta rike hannayena tana kallona ido cikin ido ta ce" Zannaba, kina ta adu.ar neman Allah ya baki miji na garin nan kuwa?
Na amsata ina dubanta da wani irin yannayi ta ci gaba" an zo neman auren ki daga gidan Elum, Zannaba kin ji zuciyarki ta aminta da Marahut?
Wara irin kunya ce ta diro mani, domin fa Agaishat yata tubawa na da muguwar kunya, batuben mutun na da kunya harda ta mamaki, hakan ya saka na sada kaina kasa harma jikina ya fara rawa,
Kakata ta ce" kul, na hane ki da ki yi haka da ni, ke kawai gare ni kema ni kawai na rage maki, Allah shi ne gatanmu, zan so ace na bar ki hannu mai kyau, dan haka maza bani hankalin ki mu gama magana,
In takaice maki a wannan rana bamu kwonta ba du sai da muka dauki niyar istihara wace cikin kwana uku hankalin mu ya gama kwonciya har ma muka aminta da auren nan,
Marahut ya yi min gata , agaishat ya kai kudin aurena ya yi min kayan da aka jima ana labarinsa, aka daura aurena irin na kowace yar gata inda kakata ta bada mamaki ashe tana ajiye da sarkokin aurensu ita da mahaifiyata, ta kai aka buge akai min tafkekiyar sarka da abubuwan hannu na zinari irin na kowace batuba yar gata, sannan ta fitar da kadarorin mahaifanna harma da nata gaba daya ta raba aka yi min kayan daki sauran ta damkawa mai anguwar anguwarmu amana,
Wsshe garin auren mu Marahut ya dankara min wata makekiyar sarka ta zinari tatare da kwacakwablarta bisa al.adun tubawa wanda hausa ce cikin hausa, ba.a jima ba muka daga dan komawa bakin aikinsa inda aka maida shi domin baban likita ne kuma yana harkar kasuwanci da kiwo.....
Mun kasance cikin farin ciki, mutunta juna, da kaunar juna, muna tafiar da rayuwar aurenmu bisa tsarin islama muna kiyaye du wani abinda zai firgita mu sai dadaykun da baza.a rasa ba na yau da kulun!
A haka na samu cikin wardugu,
Mu kai rainon abinmu har na tashi haihuwa inda Allah ya taimake ni na haihu a hannun mijina a asibitin da yake aiki da taimakawar nurse..
.
Mun koma gida dan zanen sunna, nan Marahut ya gabatar da sunnan *WARDUGU* a matsayin sunnan da ya zaba,
Kowa ya jinjina lamarin sai dai ikonsa ne, dansa ne, aman sunnan Wardugu linzami ne ga mutun mai zuciya, mai fada, mai balaki, kai ba.a zama lafia da mai sunna wardugu, Wardugu! HUM, ko canfawa ne mun yi kuma yana bin mu, kwarai zahiri ne Wardugu duniya ne guda, ba sai an koya masa ba da abinsa aka haife shi.......
Ina wanka a gida wajen kakata, tana kula da lamarina sosai da sosai, wata rana muka wayi gari da kyautar Allah, inda mutuwa ta sake zagayowa ta tsame min wace ta min saura a tarihin iyayena,
Ayya ta yi shiru ta share kwalar da ta zubo mata,
Agaishat da ta yi lamo ta dora kanta a hannun Ayya, Ayya ta ci gaba" Agaishat na ji mutuwar baiwar Allahn nan, domin ni ita ce duniyata, ko me na kwaso ita nake fadawa a nitse ta warware min, ta rasu ta bar ni da jaririn da a lokacin bana iya daukansa da garaje dan girmansa masha Allah, ta bar ni da dan labubun yaron da yakan calara kuka wai shima nice mahaifiyarsa, na ga rana na godewa Allah,
Agaishat ta kara jimke hannun Ayya itama tana jin yanda hawayen ya zubo mata, Ayya baiwar Allah, bata da kowa gaba da baya, ashe du yanda mutun ya kai ga malakar arziki bashi da cikeken farin ciki na yanayin rayuwar yau da kulun?
Ayya ta ce" na dawo ga marahut, bani da kowa bani da komai sai Shi a nan cikin duniya,
Bayan an yi bakwai muka juya garinmu inda na dauki girma na ajiyewa kaina na karfi da yaji na ci gaba da karatun likitana da nake yi a Ensp,
Can tsakiyar dare nakan dadaba Marahut, idan ya farka sai nace" Marahut, kar ka wulakanta ni a duniya, kai ne duniyata, kai ne farin cikina,
Yakan riko ni jikinsa ya ce" ban aure ki ba sai da na gane ke ce lumfashina, a duniya baki daya me ya kai lumfashin mutun tsada? Ba zan yi garajen gannin hawayenki ba sai na kadara!
Magangannunsa da alkawarurukansa suka saka na samu nutsuwar zuciyata harma na warware na ci gaba da shagulgulana na yau da kulun tare da yarona,
Tun Wardugu na da wata bakwai ya mike, yana tafiya da kafafuwansa digir digir tamkar dan gwari,
Du inda na yarda na je da shi idan ya damki yaro ko matashi sai an kwace da kyar,
Ya kasance ba.a gardama da shi da ya warware, yana fama da ciwon athsm wace in dai na yarda ransa ya baci toh fa a kadan mu yi kwana uku a asibiti domin athsmar nan zata tashi ne ya kasance daga ta kwonta sai ta kuma tashi domin ba zai kwontar da hankalin nasa ba,
Wardugu zuciyar mahaifinsa ne, domin daga shi ko batan wata ban kuma yi ba, muna bibjyar komai nasa tamkar ranmu, kai har bama kawaici a nuna soyayarsa,
A nitse ya ce" me da me kuke aikatawa a Wardugu place?
Aisata ta yi tsam kafin ta shiga cicira ido ta kali dan ta kali uban, cikin yannayin barikinta ta ce" me muke yi kuwa banda neman kudi? A wardugu place ba abinda muke yi,
Wardugu dake rubutu a takarda ya dan yi tsam ya dago ya dube su ya maida kansa ya ci gaba da aiki,
Bai jima ba ya daga wayar office din ya danna kira,
Cikin girmamawa ya gaisar da jujun kafin yake fadin" mai girma na gama nawa binciken, yanzu ana kawo maka takardu ka duba, daga nan na mika maka su kawai ,
Amsa shi ya yi kafin yake kashewa,
Marahut da ya gama fahimtar wayar da Wardugu ya yi shima yana dubansa, cikin yannayin nutsuwarsa dai ya ce" har yanzu baka daina jin haushina kan Aisata ba?
Wardugu ya juyo da sauri, ido ya zazaro baki daya kafin yake mikewa ya tofar da yawu a nan cikin office din ya ce" kan wannan? Ya fada yana nuna aisata,
Ya girgiza kai ya ce" ai koda me daraja ce bata kai na yi anfani da damata dan wulakanta ku ba, ka gane laifi ta yi, idanma baka yarda ba ai kai din oga ne kawai ka je wajen wa.inda zan mikawa takarda idan sun baka matarka ruwansu ni dai ai na tono barnar ko? Ka fi kowa sannin waye wardugu domin kaine mutun na farko da ka rikeni a duniya bayan likitar da ta fitar da ni daga cikin mahaifiyata!
Yana gama fada ya ja kys din motarsa ya dauki gilashinsa ya fice a office din yana mai jin haushin yanda mutane ke magiya kan a bari a ci gaba da yada barna!
Jikin Ayya ne ya yi sanyi bayan korar Agaishat da ta yi, a hankali ta mike ta nufi dakinta tana mai jin wani iri me ya yi zafi harda laifin wani zai shafi wani?
Tana zuwa ta shiga da salama,
Agaishat dake zaune kasa ta dora kanta a gefen gado tana jan carbi da hannunta ta dago da sauri tana kokarin mikewa tana duban Ayya,
Karasawa Ayya ta yi ta riketa ta zaunar da ita gefen gado,
A nitse ta ce" ki yi hakuri yar gidan Ayya, ba zan kuma yi maki irin haka ba ,
Agaishat ta sauke ajiyar zuciya tana dubanta,
Ayya ta ce" bara na baki labarin mu..... na fada maki wacece *AYYA?*, na fada maki waye *MARAHUT a rayiwar Ayya?*, na fada maki wanene *WARDUGU* sannan wani irin girman daraja yake da shi a rayuwar Marahut da Ayya? Yarinta bara na baki labarin da ba kowa ya sani ba................
🐫🐫🐫 *BAK'A CE*🐫🐫🐫
Na *SAJIDA*
*بسم الله الرحمن الرحيم*
____________________________________
*🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
____________________________________
3️⃣2️⃣
labarin Wardugu da tushensa a gajarce
.
........ ..................
Sunana *Zanaba SHAU*, sunnan Mahaifin Wardugu *MARAHUT ELUM*, ni marainiya ce gaba da baya, na taso a hannun kakata ta wajen uwa da ta yi min saura,
Marahut dan gata ne gaba da baya, ya kasance a lokacin anguwarmu daya domin gida uku kawai ke tsakaninmu,
Tun wayona bai gama fahimtar Marahut na sona ba har na gane domin kiri kiri idan na yarda wani lokacin na yi dan shirin atampa na yafa mayafi na fito zai rufe ido ya kora ni yana masifa,
A anguwa ana girmama kakata domin mace ce da ta san girmanta, ba abinda ya shafeta da abin hannunka, ga mutunci ga zumunci,...du juma.a zaki ga an kawowa kakata abinci daga gidajen anguwar nan ciki kuwa harda gidan su Marahut inda mahaifiyarsa shuwa arab ke turowa kakata da gurasa ta kasa, irin wace ake yi a kasa ta ainahin da miya mai dadi harma ki ga an zuba tawa miyar mai magi domin a lokacin an hana kaka shan magi.
Sosai muke soyaya da Marahut, duk da wani lokacin nakan zauna na yi shiru ina tunanin Marahut na so na kamar yanda nake son sa kuwa?
Hakan sai ya tayar min da hankali sosai domin Marahut dai jarumin namiji ne mai cike da abubuwan da mata ke marari har suna kai wawa, harma wani lokaci na kwatanta masa....
Tsareni ya yi da ido kawai, zuwa wani dan lokacin ya mike ya fice abinsa hakan ya haifar min da faduear gaban ko ya yi fushi ya bar ni ne?
Kwana biyu tsakani na dawo daga makarantar dare islamiya da nake zuwa a kusa da mu na tarar da kakata zaune tana jan carbinta da rufarta bata kwonta ba, ba kamar sauran lokutan ba,
Da sasarfa na karasa wajenta dan gannin abinda ke damunta sai dai ina zuwa ta rike hannayena tana kallona ido cikin ido ta ce" Zannaba, kina ta adu.ar neman Allah ya baki miji na garin nan kuwa?
Na amsata ina dubanta da wani irin yannayi ta ci gaba" an zo neman auren ki daga gidan Elum, Zannaba kin ji zuciyarki ta aminta da Marahut?
Wara irin kunya ce ta diro mani, domin fa Agaishat yata tubawa na da muguwar kunya, batuben mutun na da kunya harda ta mamaki, hakan ya saka na sada kaina kasa harma jikina ya fara rawa,
Kakata ta ce" kul, na hane ki da ki yi haka da ni, ke kawai gare ni kema ni kawai na rage maki, Allah shi ne gatanmu, zan so ace na bar ki hannu mai kyau, dan haka maza bani hankalin ki mu gama magana,
In takaice maki a wannan rana bamu kwonta ba du sai da muka dauki niyar istihara wace cikin kwana uku hankalin mu ya gama kwonciya har ma muka aminta da auren nan,
Marahut ya yi min gata , agaishat ya kai kudin aurena ya yi min kayan da aka jima ana labarinsa, aka daura aurena irin na kowace yar gata inda kakata ta bada mamaki ashe tana ajiye da sarkokin aurensu ita da mahaifiyata, ta kai aka buge akai min tafkekiyar sarka da abubuwan hannu na zinari irin na kowace batuba yar gata, sannan ta fitar da kadarorin mahaifanna harma da nata gaba daya ta raba aka yi min kayan daki sauran ta damkawa mai anguwar anguwarmu amana,
Wsshe garin auren mu Marahut ya dankara min wata makekiyar sarka ta zinari tatare da kwacakwablarta bisa al.adun tubawa wanda hausa ce cikin hausa, ba.a jima ba muka daga dan komawa bakin aikinsa inda aka maida shi domin baban likita ne kuma yana harkar kasuwanci da kiwo.....
Mun kasance cikin farin ciki, mutunta juna, da kaunar juna, muna tafiar da rayuwar aurenmu bisa tsarin islama muna kiyaye du wani abinda zai firgita mu sai dadaykun da baza.a rasa ba na yau da kulun!
A haka na samu cikin wardugu,
Mu kai rainon abinmu har na tashi haihuwa inda Allah ya taimake ni na haihu a hannun mijina a asibitin da yake aiki da taimakawar nurse..
.
Mun koma gida dan zanen sunna, nan Marahut ya gabatar da sunnan *WARDUGU* a matsayin sunnan da ya zaba,
Kowa ya jinjina lamarin sai dai ikonsa ne, dansa ne, aman sunnan Wardugu linzami ne ga mutun mai zuciya, mai fada, mai balaki, kai ba.a zama lafia da mai sunna wardugu, Wardugu! HUM, ko canfawa ne mun yi kuma yana bin mu, kwarai zahiri ne Wardugu duniya ne guda, ba sai an koya masa ba da abinsa aka haife shi.......
Ina wanka a gida wajen kakata, tana kula da lamarina sosai da sosai, wata rana muka wayi gari da kyautar Allah, inda mutuwa ta sake zagayowa ta tsame min wace ta min saura a tarihin iyayena,
Ayya ta yi shiru ta share kwalar da ta zubo mata,
Agaishat da ta yi lamo ta dora kanta a hannun Ayya, Ayya ta ci gaba" Agaishat na ji mutuwar baiwar Allahn nan, domin ni ita ce duniyata, ko me na kwaso ita nake fadawa a nitse ta warware min, ta rasu ta bar ni da jaririn da a lokacin bana iya daukansa da garaje dan girmansa masha Allah, ta bar ni da dan labubun yaron da yakan calara kuka wai shima nice mahaifiyarsa, na ga rana na godewa Allah,
Agaishat ta kara jimke hannun Ayya itama tana jin yanda hawayen ya zubo mata, Ayya baiwar Allah, bata da kowa gaba da baya, ashe du yanda mutun ya kai ga malakar arziki bashi da cikeken farin ciki na yanayin rayuwar yau da kulun?
Ayya ta ce" na dawo ga marahut, bani da kowa bani da komai sai Shi a nan cikin duniya,
Bayan an yi bakwai muka juya garinmu inda na dauki girma na ajiyewa kaina na karfi da yaji na ci gaba da karatun likitana da nake yi a Ensp,
Can tsakiyar dare nakan dadaba Marahut, idan ya farka sai nace" Marahut, kar ka wulakanta ni a duniya, kai ne duniyata, kai ne farin cikina,
Yakan riko ni jikinsa ya ce" ban aure ki ba sai da na gane ke ce lumfashina, a duniya baki daya me ya kai lumfashin mutun tsada? Ba zan yi garajen gannin hawayenki ba sai na kadara!
Magangannunsa da alkawarurukansa suka saka na samu nutsuwar zuciyata harma na warware na ci gaba da shagulgulana na yau da kulun tare da yarona,
Tun Wardugu na da wata bakwai ya mike, yana tafiya da kafafuwansa digir digir tamkar dan gwari,
Du inda na yarda na je da shi idan ya damki yaro ko matashi sai an kwace da kyar,
Ya kasance ba.a gardama da shi da ya warware, yana fama da ciwon athsm wace in dai na yarda ransa ya baci toh fa a kadan mu yi kwana uku a asibiti domin athsmar nan zata tashi ne ya kasance daga ta kwonta sai ta kuma tashi domin ba zai kwontar da hankalin nasa ba,
Wardugu zuciyar mahaifinsa ne, domin daga shi ko batan wata ban kuma yi ba, muna bibjyar komai nasa tamkar ranmu, kai har bama kawaici a nuna soyayarsa,