← Book details Bak'a Ce Part 1 Complet Hausa Novel Local reading mode
READING PART 53 OF 110

Sashe 53

Bak'a Ce Part 1 Complet Hausa Novel · about 8 min read

Da wannan kallon cikin idon da ta yi masa na tsayin lokaci inda ya dora hannunsa na dama yana gyara mata dogon gashinta da ya bazu kan bed dinta kafin a hankali ya ce" ki yafe mini,

A haka ya ja mata bargo ya lulubeta ya kashe mata fitilar dakin ya fita da nufin ya barta ta yi baci ko me?
A haka ta hangi ficewarsa wajen ainahin aminiyarsa , Aminiyarsa, aminiyarsa!

Abinda ya faru da Agaishat da Mu.azam da khadija kennan kafin a kawo Mu.azam asibiti bisa kulawar likitoci sa Agaishat da Khadija aka shiga saka masa magungunna ta hanyar karin ruwa da nanauyan magugunnan baci dan ya samu isashen hutu.....
Wannan kennan

Wardugu na karasawa gidansa ya fita ya nufi sashensa,

Yana budewa ya shiga da sabon cerrure din da ya canza ,
Yana shiga ya ga sabuwar mai aikin da ya dauka, wace a da babu namiji a yan aikin bangarensa bisa umarnin walyn, aman a yanzu ya dauka ta gyara falon ta saka turaren ruwa mai kanshi ta ajiye abinci,

Ya san tana can bangaren da ya saka aka kaita wanda ke nesa da wajensa sosai dan haka ya zarce dakinsa

Sauri sauri ya yi wanka ya dauki jakarsa irin ta sojoji ya saka kananun kayansa na bukata da maclean da bros, da complet daya ,
Kananun kaya ya saka a jikinsa bakin dogon wando da bakar riga kafin yake dora costume (veste) saman rigar ya caje gashinsa ya gyara sosai ya fesa turare mai kanshi,

Jakar ya dauka da passport dinsa sai cart dinsa ta can wace a bankin can ya yita,

Fitowa ya yi yana duba dakin bai bar komai a jone ba?
Nan ya ga hajia Walyn tsaye, ta sha kwaliya mai kyau da birgewa tana masa murmushi ,

Kallo daya ya yi mata kafin ya kawar da fuskarsa ya juya ,
Yannayin hade fuskar da ya yi ya saka bata iya tankasa ba, tsoro ya hanata tambayarsa inda zai je duda ta sani ne fita ne zai yi ya dawo dan haka sai ta nemi waje ta mike tana jiran dawowarsa ta lalabe shi ya manta fushin da yake su shirya (to ka ji)!

Bai dauki mota ba, bai kuma bi ta kan kowa ba ya fice a kafarsa yana mai duba agogo

Taxi ya tsayar ya shiga ya fada masa aeroport,

Timiya

🐫🐫🐫🐫 *BAK'A CE* 🐫🐫🐫🐫

https://www.facebook.com/Idan-rana-ta-fito-writers-association-114558343535568/?referrer=whatsapp

*☀IDAN RANA TA FITO WRITER'S ASSO🌤* ____________________________________________

*Fad'akar da al'umma tare da nishad'antar da masoya shine fatanmu*😘🤝🏻😘

Na
*SAJIDA*

5️⃣3️⃣

Timiya

A wannan ranar da kyar aka samu Anna ta koma ta zauna , shima sai da y'ayata suka rikice da koke koken dan girman Allah ta zauna a zana sunnan jaririn nan da aka samu sai su tafi, dan Gaishata ta kara kai da kasa yan uwanta da mahaifiyarta ba zasu tafi su duka su barta ba, kar a je su ki dawowa,
Gannin haka shima sarkin hankalinsa ya tashi dan haka harda shi a yan magiyar ta zauna a yi suna sai ya yi masu rakiya wajen wanda yake da alaka da gidan , wato sarkin agadez, shima rakia ya yi masa wani lokaci da suka je banban birnin, suna ganewa junna,

Haka dai Anna ta yarda ba dan hankalinta ya kwonta ba, sai dan tinawa da ta yi y'ayanta, idan ta tafi wajen wa zasu rabu su ji sanyi? Dama gashi ya fara tado maganar mutanen da suka kawo kudin aurensu sun waiwayo zasu zo a daura aure,
Wani murmushi ta yi mai ma.anoni da dama kafin take fita ta juye zuwan zafin dake tafasa Mariama ta kama suka kai bayi ta fito fuska a dan hade ta zanawa sirikin nata du abin bukata na wankan jego kan a yi gagawa a kawo kafin ruwan ya huce, (abinda da bata iya ko tsayuwa gata ga shi, Annar yanzu ba ruwanta ba wani shaka ko tsoro),
Da sauri ya amsa ya fita a gidan, inda Anna ta tube jaririn sai hada rai take na yannayin tsaftar gidan , du hankalinta da nutsuwarta ba a waje daya suke ba, sai ma da aka tashi neman turare abinka da batuba, kaf gidan Mariama ce kawai mai turare , itama irin na duran nan ne mai karfin tsiya, dan haka dole su Mariaman suka karbi makulin dakin Gaishata suka nufi gidan sarki dan ita tana da dan turaran wuta da na ruwa dan idan sarki ya je cikin birni yana bada kudi wajen mai dakin sarkin agadez q harhada masu tsumamun turaruka da sauran su,....

Wannan kennan

*Paris*

Jirgi na sauke shi ya kunna abin localisat@ din wayarsa ya shiga carte cikin iphone dinsa ya danna localisation din wayar Mu.azam, domin a kunne take kuma ya tabata nasama ba a kashe ba,

Taxi na ajiye shi kofar asibitin ya je wajen shiga ya nuna takardar shaidar waye shi, ya bada cikenken kwatancen wajen wanda ya zo da ranar da aka kawo shi da komai kafin ake barinsa shiga dan an rigaya an hana shiga, suma da suke tare da shi dan Khadija na ma.aikaciyar wajen ita da Mu.azam din,

Yana shiga ya fitar da wayar ya shiga bin kwatancen da ta dora masa saman screen dinsa har ya iso dakin da yake kwonce,

Da yake akoy katon madubin da ana tsayawa a ga marar lafia ta nan, sai Wardugu ya tsaya ya harde hannayensa ya zuba masu ido,
Khadija na nanade saman salaya carbinta ya fadi da alama tana ja baci ya kwasheta,
Agaishat na zaunen dai saman kujera kuma lokaci zuwa lokaci takan dan motsa kafarta idannuwanta a rufe har yanzu kamar mai baci, da dogon hijabinta mai ruwan jini,
Sai Mu.azam dake sheme saman gadon mararsa lafia, an aske kansa kwalkwal har kyali yake , wanda shi ya saka aka aske masa da kansa tun kafin a shiga aikinma, yana ajiye numfashi a hankali,
Idannuwansa ya rintse ya karasa wajen doguwar kujerar silbar da ya ganni a wajen ya zauna ya daga kansa sama yana jan carbin hannunsa ya tsurawa fitilar dakin ido

Yanda Wardugu ya ga rana haka ya ga dare, wajen karfe biyu ya ji motsi a dakin nasu wanda ya kyautata zaton alwalla aka dauro dan an jima ana dan motsi kafin ya ji shiru, a hankali ya leka nan ya ga Agaishat ce ta kai sujada kanta kasa tana adu.a, kawar da kansa ya yi da sauri ya koma ya zauna ya ci gaba da jan carbinsa, har karfe biyar ta yi
Ba kiran sallah zasu ji ba dan haka da agogo suke aiki , da lokaci ya yi zasu mike su yi sallah ne,
Zuwa ya yi ya samu ya dauro alwallah ya dawo,
Tapis ya dauka cikin jakarsa ya kebance kansa dan likitoci sun fara dan kai kawo ya tayar da sallarsa,
Ya jima yana rokom Allah ya sa a yi aikin nan lafia, yana gamawa ya mike dan shida ta gota ya dauki jakarsa ya dan kwonkwasa dakin

Agaishat dake kusa da kofar ta mike ta bude ,
Gabanta ne ta ji ya wani tsintsinke ya fadi a lokaci guda,
Kanta ta daga kafin take iya kallon fuskarsa, wanda shima ya dan duko da kansa ya sauke idannuwansa kan fuskarta,
Ba zaka iya karantar yannayin fa yake ciki ba, fuskarsa ba yabo ba falasa,
Shigowa ya yi ya mayar da kofar ya rufe,
Fuskarta da idannuwanta sun kumbura, hakan na nuni da ta yi kuka,
Kawar da dubansa ya yi daga kanta ya mayar kan Khadiha da ta mike itama tana dubansa,
Fuskarta itama ta bumbura ta yi jajajir,
Bai amsa gaisuwar da suke masa ba sai zarxewa da ya yi wajen Mu.azam,

Kujerar dake kusa da gadonsa ya ja a hankali ya zauna yana kallonsa, karfe bakwai saura yan mintuna Mu.azam ya farka,
Farkawarma ba can bace, ya fan buda idannuwansa da sukai masa wani irin nauyi ne,
A hankali ya ga Wardugu dake zaune ya rike hannunsa na dama,
Allah ya bashi ikon yin murmushi yana duban Wardugu,
Magana yake a hankai wanda Wardugu ya kunnayensa aman bai ji komai ba dan haka ya nuna masa da ya yi shiru,

Da idannuwansa ya nuna ya yi shirun inda ya lumshe idannuwan sai ga hawaye sun fito daga cikin idannuwan nasa,
Docter Ce ta shigo da farar riga irin ta likitoci tare da nurse da uku da gadon tura marar lafia

Wani irin mikewa Khadija ta yi ta zuba masu ido inda docter ta girgiza mata kai, haka ne daman idan kana son gannin rikicewa sai idan ciwo ya taba likita, yakan fice a hayacinsa ya zama wani kala, yakan rude komai kankantar ciwo bale mai tsanani,
Hakan ce ta faru da khadija, domin a lokaci daya ta rikice ana nuna mata kar ta yi gabansa aman ina bata san lokacin da ta dora hannayenta duka biyu saman kanta ta fashe da kuka , da sauri Wardugu ya juyo ya cire gilas din idannuwansa domin har ya mana dan baya so a san halin da yake ciki,,

Da sauri Docter ta kama hannunta suka fice inda wasu likitocin maza biyu suka shiga kokarin daukansa suka dora saman dayan bed din

A hankali Wardugu ya saka hannunsa cikin sumar kansa ya shiga yamutsawa inda gaba daya jijiyoyin jikinsa suka mike tsabar yana cikin tashin hankali

Agaishat dake tsaye sai zarar ido take gannin yanda Khadija ta fashe da kuka aka fita da ita, da yanda aka dauki Mu.azam ranga ranga aka dora saman wani gado, du fuskokin likitocin a hade irin sun ci kalar serius din nan sai ta rikice,
Tana ta zaro ido tana kallon yanda suka saka masa oxygen suka gyarashi da kyau saman gadon ,
Sai bayan sun gama gyara shi wani likita ya zo da takarda a hannunsa cikin file , da yaren faransanci ya ce" Chef, (sire), docter Khadija tace Nan zan samu Wardugu?

Wardugu dake tsaye shima yana kallon yanda aka yiwa amininsa, nan zuciyarsa ta kara tsorata da girman ikon ubangiji, kaga mutun yanzu yanzu ka zama tamkar gawa ko gawar,
Chapter 53 · 0% Book details