Sashe 48
Bak'a Ce Part 1 Complet Hausa Novel · about 8 min read
Kanta tsaye ta nufe shi inda ya mike da sauri daga kujerar mulkinsa dogarai suka shiga baza manyan rigunansu suna kare su, yan zama fada suka fara darewa da sauri sauri
Tana isa jikinsa ta zube wanda sukai taga taga dalilin kibar da ta kara ga kuma tsohon ciki,
A hankali ya samu ya daidaitata a jikinsa ya dora hannunsa inda ta dora nata wato saman cikinta da take ji baki daya yana wani irin yamutsa mata bayanta na sarawa,
Me ke damunki Gaishana,
Ya fada yana mai nuna tsantsar damuwarsa da tashin hankali, yanaiwa Gaisha soyaya mai karfin gaske,
Da kyar ta iya sauke ajiyar zuciya muryarta na rawa ta ce" Anna ce, Anna ce ta fadi, kuma tana numfashi aman ta ki farkawa,
Rigarsa ta jimke jin ciwon na tsananta ta ce" idan wani abin ya sami mahaifiyata zan shida duhu sarkina👏🏻
Zaunar da ita ya yi saman kujerar ya cire babar rigarsa ta turkudi ya rufa mata ya yi gyaran murya,
Dogari ne ya amsa masa,
Sarki ya ce" ka je wajen jakadiya ingozoma ka fada mata Gimbiya na Daka.
Da gudu ya juya inda sarki ya daga karewar da akai masa ya fita da niyar zuwa gidan su Ba, yau kam za.a yita ta kare, ba zai yarda haka ana tayarwa matarsa hankali ba, ! Gashinnan tashin hankali ya sakata nakudar dole,
*Niamey*
Tunda Ayya ta fara magana tana duban Agaishat da dukan kulawa kan Agaishat ke kasa tana zubar da hawaye,
Abaya ce baka mai shegen kyau , bata da wata kwaliya sai zif din da ya hadeta a jikinta, gyaran fatar kwana biyun da Ayya ta yi ta dilketa ya saka fatarta ta kara wani haske da santsi wanda ko a ido ka dubeta zaka ga ta gyaru iya gyaruwa,
Dan kwalin Abayar ne ke dan zamewa tana rikeshi har ya kai karfinta ya kare ta sake shi ta duke sosai tana kuka inda gaba daya jikinta ke jijiga
Idannuwansa ya rintse da karfin gaske, sannan ya jimki kujerar da yake kai,
Kansa ya juyar gefe yana jin saukar kukan nata tamkar ana narkar masa da dalma a kahon zuciya,
Mu.azam dake gefensa shima cike da tausayin matar tasa ya mintsini hannun Wardugu yanai masa nuni da ya yi wani abin mana?
Wardugu ya juyo inda take suke Ayya na rarashinta itama na sharar hawayen ya hade fuska sosai ya ce" ke!
Yannayon yanda ya ambaci ke din sole ka tsorata, yannayi ne ya garwaye da halin da yake ciki,
Da sauri ta juyo tana kara shigewa jikin Ayya,
Mikewa ya yi ya ce" mu je!
Da sauri ta waigo wajen Ayya, wace rake cikin damuwar rabuwa da yar tata, wace kamar da wasa shakuwa mai girma ta kara shiga tsakaninsu,
Tun jiya ya dace su tafi aman cikin ikon Allah Agaishat ta rikice ta yi ta kuka har zazabi ya rufeta wai ita ba zata bisu ba,
Ayya ta yi gargadin ta yi fadan, ta dawo lalaba tana mai shaida mata tamkar suna tare ne, ga waya, ta bi mijinta zai dawo da ita da wuri
Kamar da gaske ta yarda a jiya da dare, a yanzu da suka shirya har Wardugu ya zo rakiyarsu ta kuma birkicewa,
Ayya ta ce" Wardugu kar ka yi mata da zafi mana, rabuwa da iyaye ba dadi ka lalabata na roke ka,
Wardugu ya juyo yana duban Ayya, idannuwansa sun kade sun yi jajir, a ransa kam birgeshima suke , su sun samu kukan, sun huta,
Lebensa ya dantse kawai ya girgiza kai ya dawo da wani irin taku ya dauki dan kwalinta dake kasa ya rufa mata , da idannuwansa ya yi mata nunin ta fice ko jikinta ya gaya mata,
Da sauri ta yi gaba tana waiwayen Ayya, wace ta koma saman kujerar tama fasa rakasu dan ba zata juri yanda Agaishat ke kukan ba zata je wata kasa ba, ba zata je ba ta fasa auren!
Ko a cikin mota Mu.azam na gaba ne, Agaishat da Mariama na baya, direba na jansu, ta madubi yake duban yanda ta yi lakwas da ita, yana matukar son ya rarasheta aman yana jin nauyin Mariama, baya so ran Mariamarma ya bace dan haka ya adanna rarashin idan sun sauka zai mata, duda har yanzu Mariama bata ce komai game da auren nasa ba, bata nuna damuwarta ki farin cikinta ba, haka shima kwata kwata baya nuna zumudinsa ko wata shakuwa tsakaninsa da amaryar tasa,
Mita wajen biyarce ke tafe har aeroport, suna karasawa inda ake ajiye motoci du suka firfito banda taron sojojin dake tare da su,
Wardugu ya bude gefen da yake ya fara fitar da kafarsa ta dama kafin ya fitar da ta hagu,
Yau a kakin sojoji yake, ya nanade hannayen rigar har saman damtsen hannunsa hakan ya baiwa rigar damar tamke shi, jijiyoyin hannunsa sun yi rado rado ,
Da karfinsa ya taka ya shiga inda iya su suka bi bayansa
Bakin gilas ne rufe da idannuwansa , duda haka zaka gane fuskarsa a tamke take ba alamar fara.a
Polisan dake aiki a wajen du idan ya zo ficewa sai sun sara masa, shi kuwa sai dai ya shige yau arzikin daga hannunma basa samu
A haka har suka karaso, yauma Allah ya so su da sun rasa jurgin domin lokaci ya tafi har an fara shiga
Tsaye ya yi a inda iyakar yan rakiya kennan, ya juyo wajen Mu.azam dake biye da shi,
Hannunsa ya kamo suka damke juna,
Murmushi Mu.azam ya sakar masa yana mai nuna masa ba komai ya kwontar da hankalinsa,
Bai bashi amsa ba sai kafadarsa da ya daka da hannunsa ya nuna masa sai ya zo,
Gaba Mu.azam ya yi shima yana mai jin zuciyarsa na tsintsinkewa ya nufi wajen da zai shiga jirgi dan an kirayi sunnan Khadija har ta yi gaba .
Du takunsa dan nufar wajen da take tsaye wanda wajen ya kasance hanyarsa ta fita, daidai da bugun zuciyarsa ne, bai so tsayawa ba, sai dai ya ji ya tsaya facing dinta
A hankali ya dora hannunsa dake dan bari kan habarta ya dago da ita inda ya tsare idannuwansa da kallo,
A hankali ya saka hannunsa na hagu ya share mata hawayen dake mata zarya,
Wayar hannunsa ya saka cikin hannunta ya dan ja gefe ya kama hannunta ya jata a hankali har inda Mu.azam yake ya saka hannun nata cikin na Mu.azam ya dan yi tsai sannan ya juya da wani mugun saurin da sai da ya gansa a waje shi kansa
Da sauri Mu.azam ya kama hannunta suka shiga taka matatakalar jirgi, wanda ya kasance hawanta ya farki, shigarta ta fari suka shiga
Kusa da Khadija ya zaunar da ita shi kuwa ya je kujerar bayansu , du yana haka ne kar Khadija ta kulace ahi, wanda shirunta ke damun nutsuwarsa
😅😅siga baya kiran kansa siga, sai dai wani ya fada,😅😅
*☀IDAN RANA TA FITO WRITER'S ASSO🌤*
____________________________________________
*Fad'akar da al'umma tare da nishad'antar da masoya shine fatanmu*😘🤝🏻😘
🐫🐫🐫🐫 *BAK'A CE* 🐫🐫🐫🐫
Na
*SAJIDA*
5️⃣0️⃣
Allah ya sauke su lafia, du kuwa da irin yanda Agaishat ta jigata domin har amai ta yi a lokacin fa jirgi zai tashi da irin yar jijigar nan da yake kafin ya mike da tafia, sannan a lokacin saukarsa wannan kasan da abubuwan ciki ke yi suka saka shima ta yi tamakar ta sume,
Mu.azam na kule da ita , tausayinta yake ji, khadija ce ke kiran yan matan nan na jirgi da ta ga zata shiga wani yannayi , su ke zuwa su bata kulawa har jirgin ya sauka,
Agaishat dai na mamakin irin halin shariyar da Mu.azam ke nuna mata idan suna tare da Khadija, tun bata gane komai ba har ta gane sai dai bata nuna ko a fuska ba,
Ko wajen sauka shi ne gabansu su kuwa suna biye da shi a baya inda Agaishat ta zama ta karshe
Kanta ne ta ji yana juya mata lokacin da ta ganta cikin tankamemen aeroport din *Paris*
A hankali ta sada kanta dan ta lura du idan ta daga kan ta ga irin tsaruwar garin ne hankalinta ke tashi,
Fitowa suka yi inda manyan motocin taxi ke laye, da yawa an yi kiransu je, daidaiku ne suka zo wajen dan radin kansu
Wajen motar suka nufa , nan Mu.azam ya juyo gannin Khadija bata biyo su ba,
Budewa Agaishat ya yi ta shiga ta zauna inda Direban ya saka akwatinta bayan motar,
Wajen Khadija ya nufa yana son sai ya karanci fuskarya aman ta ki bashi dama,
Yana zuwa hannayenta ya kama yana dubanta ya ce" ba zaki biyo mu ba?
Murmushi ta sakar masa ta girgiza kai ta ce" ku je da matarka, nima zan dauki wata taxi din, zan leko ka, ka kular min da kanka nan da kwana hudu zaka dawo asibiti ka kwana biyu bisa kulawar docters kafin a shiga aiki da kai,
Murmushi ya sakar mata ya lakace hancinta ya saki hannayenta ya juya ya nufi motar inda sai a lokacin Agaishat ta kawar da fuskarta gefen madubin motar
Satar kallonta ya yi, sai a lokacin ya ji wani nauyinta, rabonsa da ya yi wani maganar nutsuwa da ita tun da Khadija ta sauka a gidan Ayya,
Kwarai Ayya ta yi masa mutunci ta nuna komai ba komai ba ta hanyar kawar da kanta ta kuma karbi bakuwarsa duda tsanar akidar kawance tsakanin mace da namiji da ta yi kuwa, sannan koda suka tashi tafia ta yi masa gargadi nasiha kamar yanda iyayensa zasu yi masa, sai dai kuma ta nanata ya rike amanar baiwar Allah,
Gabansa ne ya ji ya fadi, amanar Agaishat ya karbo fa, amana ya karba, anya kuwa haka amana ta ce?
A hankali ya mika hannunsa na hagu ya dora saman cinyarta , wanda ke nuni da yana son kara kusancinsa da ita,
Agaishat ta juyo ta dora tsararun irannuwanta saman hannunsa, daga nan bata kai dubanta sama ba ko dan kar idannuwansu su shaku da juna, sai ta kawar da kanta ta mayar bakin titi tana kallon hanya da mamakin irin tsarin garin da irin shigar mutanen garin
Tana isa jikinsa ta zube wanda sukai taga taga dalilin kibar da ta kara ga kuma tsohon ciki,
A hankali ya samu ya daidaitata a jikinsa ya dora hannunsa inda ta dora nata wato saman cikinta da take ji baki daya yana wani irin yamutsa mata bayanta na sarawa,
Me ke damunki Gaishana,
Ya fada yana mai nuna tsantsar damuwarsa da tashin hankali, yanaiwa Gaisha soyaya mai karfin gaske,
Da kyar ta iya sauke ajiyar zuciya muryarta na rawa ta ce" Anna ce, Anna ce ta fadi, kuma tana numfashi aman ta ki farkawa,
Rigarsa ta jimke jin ciwon na tsananta ta ce" idan wani abin ya sami mahaifiyata zan shida duhu sarkina👏🏻
Zaunar da ita ya yi saman kujerar ya cire babar rigarsa ta turkudi ya rufa mata ya yi gyaran murya,
Dogari ne ya amsa masa,
Sarki ya ce" ka je wajen jakadiya ingozoma ka fada mata Gimbiya na Daka.
Da gudu ya juya inda sarki ya daga karewar da akai masa ya fita da niyar zuwa gidan su Ba, yau kam za.a yita ta kare, ba zai yarda haka ana tayarwa matarsa hankali ba, ! Gashinnan tashin hankali ya sakata nakudar dole,
*Niamey*
Tunda Ayya ta fara magana tana duban Agaishat da dukan kulawa kan Agaishat ke kasa tana zubar da hawaye,
Abaya ce baka mai shegen kyau , bata da wata kwaliya sai zif din da ya hadeta a jikinta, gyaran fatar kwana biyun da Ayya ta yi ta dilketa ya saka fatarta ta kara wani haske da santsi wanda ko a ido ka dubeta zaka ga ta gyaru iya gyaruwa,
Dan kwalin Abayar ne ke dan zamewa tana rikeshi har ya kai karfinta ya kare ta sake shi ta duke sosai tana kuka inda gaba daya jikinta ke jijiga
Idannuwansa ya rintse da karfin gaske, sannan ya jimki kujerar da yake kai,
Kansa ya juyar gefe yana jin saukar kukan nata tamkar ana narkar masa da dalma a kahon zuciya,
Mu.azam dake gefensa shima cike da tausayin matar tasa ya mintsini hannun Wardugu yanai masa nuni da ya yi wani abin mana?
Wardugu ya juyo inda take suke Ayya na rarashinta itama na sharar hawayen ya hade fuska sosai ya ce" ke!
Yannayon yanda ya ambaci ke din sole ka tsorata, yannayi ne ya garwaye da halin da yake ciki,
Da sauri ta juyo tana kara shigewa jikin Ayya,
Mikewa ya yi ya ce" mu je!
Da sauri ta waigo wajen Ayya, wace rake cikin damuwar rabuwa da yar tata, wace kamar da wasa shakuwa mai girma ta kara shiga tsakaninsu,
Tun jiya ya dace su tafi aman cikin ikon Allah Agaishat ta rikice ta yi ta kuka har zazabi ya rufeta wai ita ba zata bisu ba,
Ayya ta yi gargadin ta yi fadan, ta dawo lalaba tana mai shaida mata tamkar suna tare ne, ga waya, ta bi mijinta zai dawo da ita da wuri
Kamar da gaske ta yarda a jiya da dare, a yanzu da suka shirya har Wardugu ya zo rakiyarsu ta kuma birkicewa,
Ayya ta ce" Wardugu kar ka yi mata da zafi mana, rabuwa da iyaye ba dadi ka lalabata na roke ka,
Wardugu ya juyo yana duban Ayya, idannuwansa sun kade sun yi jajir, a ransa kam birgeshima suke , su sun samu kukan, sun huta,
Lebensa ya dantse kawai ya girgiza kai ya dawo da wani irin taku ya dauki dan kwalinta dake kasa ya rufa mata , da idannuwansa ya yi mata nunin ta fice ko jikinta ya gaya mata,
Da sauri ta yi gaba tana waiwayen Ayya, wace ta koma saman kujerar tama fasa rakasu dan ba zata juri yanda Agaishat ke kukan ba zata je wata kasa ba, ba zata je ba ta fasa auren!
Ko a cikin mota Mu.azam na gaba ne, Agaishat da Mariama na baya, direba na jansu, ta madubi yake duban yanda ta yi lakwas da ita, yana matukar son ya rarasheta aman yana jin nauyin Mariama, baya so ran Mariamarma ya bace dan haka ya adanna rarashin idan sun sauka zai mata, duda har yanzu Mariama bata ce komai game da auren nasa ba, bata nuna damuwarta ki farin cikinta ba, haka shima kwata kwata baya nuna zumudinsa ko wata shakuwa tsakaninsa da amaryar tasa,
Mita wajen biyarce ke tafe har aeroport, suna karasawa inda ake ajiye motoci du suka firfito banda taron sojojin dake tare da su,
Wardugu ya bude gefen da yake ya fara fitar da kafarsa ta dama kafin ya fitar da ta hagu,
Yau a kakin sojoji yake, ya nanade hannayen rigar har saman damtsen hannunsa hakan ya baiwa rigar damar tamke shi, jijiyoyin hannunsa sun yi rado rado ,
Da karfinsa ya taka ya shiga inda iya su suka bi bayansa
Bakin gilas ne rufe da idannuwansa , duda haka zaka gane fuskarsa a tamke take ba alamar fara.a
Polisan dake aiki a wajen du idan ya zo ficewa sai sun sara masa, shi kuwa sai dai ya shige yau arzikin daga hannunma basa samu
A haka har suka karaso, yauma Allah ya so su da sun rasa jurgin domin lokaci ya tafi har an fara shiga
Tsaye ya yi a inda iyakar yan rakiya kennan, ya juyo wajen Mu.azam dake biye da shi,
Hannunsa ya kamo suka damke juna,
Murmushi Mu.azam ya sakar masa yana mai nuna masa ba komai ya kwontar da hankalinsa,
Bai bashi amsa ba sai kafadarsa da ya daka da hannunsa ya nuna masa sai ya zo,
Gaba Mu.azam ya yi shima yana mai jin zuciyarsa na tsintsinkewa ya nufi wajen da zai shiga jirgi dan an kirayi sunnan Khadija har ta yi gaba .
Du takunsa dan nufar wajen da take tsaye wanda wajen ya kasance hanyarsa ta fita, daidai da bugun zuciyarsa ne, bai so tsayawa ba, sai dai ya ji ya tsaya facing dinta
A hankali ya dora hannunsa dake dan bari kan habarta ya dago da ita inda ya tsare idannuwansa da kallo,
A hankali ya saka hannunsa na hagu ya share mata hawayen dake mata zarya,
Wayar hannunsa ya saka cikin hannunta ya dan ja gefe ya kama hannunta ya jata a hankali har inda Mu.azam yake ya saka hannun nata cikin na Mu.azam ya dan yi tsai sannan ya juya da wani mugun saurin da sai da ya gansa a waje shi kansa
Da sauri Mu.azam ya kama hannunta suka shiga taka matatakalar jirgi, wanda ya kasance hawanta ya farki, shigarta ta fari suka shiga
Kusa da Khadija ya zaunar da ita shi kuwa ya je kujerar bayansu , du yana haka ne kar Khadija ta kulace ahi, wanda shirunta ke damun nutsuwarsa
😅😅siga baya kiran kansa siga, sai dai wani ya fada,😅😅
*☀IDAN RANA TA FITO WRITER'S ASSO🌤*
____________________________________________
*Fad'akar da al'umma tare da nishad'antar da masoya shine fatanmu*😘🤝🏻😘
🐫🐫🐫🐫 *BAK'A CE* 🐫🐫🐫🐫
Na
*SAJIDA*
5️⃣0️⃣
Allah ya sauke su lafia, du kuwa da irin yanda Agaishat ta jigata domin har amai ta yi a lokacin fa jirgi zai tashi da irin yar jijigar nan da yake kafin ya mike da tafia, sannan a lokacin saukarsa wannan kasan da abubuwan ciki ke yi suka saka shima ta yi tamakar ta sume,
Mu.azam na kule da ita , tausayinta yake ji, khadija ce ke kiran yan matan nan na jirgi da ta ga zata shiga wani yannayi , su ke zuwa su bata kulawa har jirgin ya sauka,
Agaishat dai na mamakin irin halin shariyar da Mu.azam ke nuna mata idan suna tare da Khadija, tun bata gane komai ba har ta gane sai dai bata nuna ko a fuska ba,
Ko wajen sauka shi ne gabansu su kuwa suna biye da shi a baya inda Agaishat ta zama ta karshe
Kanta ne ta ji yana juya mata lokacin da ta ganta cikin tankamemen aeroport din *Paris*
A hankali ta sada kanta dan ta lura du idan ta daga kan ta ga irin tsaruwar garin ne hankalinta ke tashi,
Fitowa suka yi inda manyan motocin taxi ke laye, da yawa an yi kiransu je, daidaiku ne suka zo wajen dan radin kansu
Wajen motar suka nufa , nan Mu.azam ya juyo gannin Khadija bata biyo su ba,
Budewa Agaishat ya yi ta shiga ta zauna inda Direban ya saka akwatinta bayan motar,
Wajen Khadija ya nufa yana son sai ya karanci fuskarya aman ta ki bashi dama,
Yana zuwa hannayenta ya kama yana dubanta ya ce" ba zaki biyo mu ba?
Murmushi ta sakar masa ta girgiza kai ta ce" ku je da matarka, nima zan dauki wata taxi din, zan leko ka, ka kular min da kanka nan da kwana hudu zaka dawo asibiti ka kwana biyu bisa kulawar docters kafin a shiga aiki da kai,
Murmushi ya sakar mata ya lakace hancinta ya saki hannayenta ya juya ya nufi motar inda sai a lokacin Agaishat ta kawar da fuskarta gefen madubin motar
Satar kallonta ya yi, sai a lokacin ya ji wani nauyinta, rabonsa da ya yi wani maganar nutsuwa da ita tun da Khadija ta sauka a gidan Ayya,
Kwarai Ayya ta yi masa mutunci ta nuna komai ba komai ba ta hanyar kawar da kanta ta kuma karbi bakuwarsa duda tsanar akidar kawance tsakanin mace da namiji da ta yi kuwa, sannan koda suka tashi tafia ta yi masa gargadi nasiha kamar yanda iyayensa zasu yi masa, sai dai kuma ta nanata ya rike amanar baiwar Allah,
Gabansa ne ya ji ya fadi, amanar Agaishat ya karbo fa, amana ya karba, anya kuwa haka amana ta ce?
A hankali ya mika hannunsa na hagu ya dora saman cinyarta , wanda ke nuni da yana son kara kusancinsa da ita,
Agaishat ta juyo ta dora tsararun irannuwanta saman hannunsa, daga nan bata kai dubanta sama ba ko dan kar idannuwansu su shaku da juna, sai ta kawar da kanta ta mayar bakin titi tana kallon hanya da mamakin irin tsarin garin da irin shigar mutanen garin