← Book details Bak'a Ce Part 1 Complet Hausa Novel Local reading mode
READING PART 101 OF 110

Sashe 101

Bak'a Ce Part 1 Complet Hausa Novel · about 8 min read

Agaishat da jikinta ke rawa rawa ta dan girgiza kai bata iya amsawa ba,
Wardugu ya dan kara goga mata sajen fuskarsa a dokin wuyan nata yana lumshe ido sannan a hankali yana lura da yannayinta yanda du ta firgice da bakon lamarin da bata taba gani ko ji a tare da ita ba, sai ya dauki hakan a wata fasara daban, ganninsa ta saba ne, har ta fara daukan caji... dan haka ya sasauta rikon da ya yi mata ya ja hannunta ya kaita kusan bayin dakin ya nuna mata da hannunsa, sannan ya nuna mata salaya ya juya ya fice,
Wata wawiyar ajiyar zuciya ta sauke kafin take dora hannunta daidai zuciyarta, wai Allahna, shine abinda ta fada....menene wannan? Me yasa idan na ganka nake jin irin wannan faduwar gaba da tsoron ka gusa daga inda nake? Me ya sa ka zama mai zafin taba fatar jikina aman maimakun na hana sai na bige da lafewa a fafadan kirjinka, Sadaukina....bakon mijina, zan kwatanta yi maka biyaya mudin raina, Allah ya bani ikon cin nasara
..

Haka ta shiga bayin da ta so zama yar kauye, du kuwa da irin wajajen gayun da ta rayu,
Da kyar ta samu ta daura alwallah ta fito ta yi sallah,
Ba wani wanka da zata yi, bata zo da wannan rawar kan ba, sannan kafin a kawota sai da Ayyanta ta cika mata ciki dan haka tana gama sallah mikewa ta yi ta nemi wajen kwonciya ta nade saman lalausan lafiyayen bed din da bashi da wani tsayi sosai sai dai fadi,

Bata wani jira gannin ya zo inda take ba, domin kuwa koda Ayya ke mata jawabi ta cika da tambayar kanta daman miji zai tardota inda take ko me? Ita dai a aurenta na fari, bai taba zama saman bed dinta ba, bale a kai ga kwonciya, dan haka bata cire doguwar rigarta ba ta yi kwonciyarta da abinta, (kar ku manta, budurwa take, du wani rawar kai wani a cire kaya a sake wanka , a wani canza kaya sai kace uwar mata ko wata wace ta jima a lamarin , walahi a kiyaye, zaki iya sakawa mijin dar a zuciyarsa, koda kuwa a bazawara ya aureta idan ya tardo cas cas malan ka8 nake jira ba wani aji ba wani dan kunya ina dalili? Dan Allah ku mu dauki al.adunmu na malan bahaushe, amarya amarya ce, ta bari a tardota, kai koda ta san lamarin ta bari ya ja daren farkon nan, aman ba wai daga an tabaki ba kema har kin koya! Yin farin? Zuwan farin? Yan mata yaya dai?🤣🤣🤣🤣😹😹😹😹😹),

Luluba ta yi cikin bargonta dake malale saman bed din, bayan ta yi adu.o.inta cike da kewar ayyanta ta lumshe ido da fatan Allah ya tasheta lafia cike da tunanin ta ina zata ji kiran sallah wannan gida tamkar ma.aikata ko hotel?

Wardugu kam, haka ya je masu shi kadai yana muzurai, domin sun shirya yar karya karya tsakaninsu idan an kawo amarya harda amaryar, sai dai ganninsa suka yi shi daya,
Ba wanda ya takura shi haka suka dan jima ana murnar karin aurwn general kafin suke watsewa , ciki kuwa harda Alhinayett da mijinta da yan uwanta inda suka tafi suna kunshe dariyar lamarin wardugu,

A nitse ya koma bangarensa, lokacin har karfe daya na faman yi, dan haka wanka ya fara nema ya dauro alwallah,
Shafa.i da wuturi ya yi, ya shafa adu.a inda yake jin cikinsa na kuwar yinwa, sannan abin mamaki bata zo inda yake ba, dan kuwa Walyn ita ke tardo shi koda yaushe, shi ba zai irga ranar da ya je mata ba,

Mikewa ya yi ya kai dubansa kan ledar da aka bashi, wai kajin amarci,
Murmushi kawai ya yi ya zauna ya bude,
Bridel ya gani ciki dan haka ya bude da bismillah ya kafa kansa, sai da ya yi kat ya ajiye goran ya rufe ledar ya mike ya zauna bakin bed,
Shiru ya yi yana tunanin me ya hanata zuwa inda yake?
*DAN BAKA ISA BA, BA KAI TAKE SO BA!* tunaninsa ya bashi haka,
A hankali ya dora kafarsa ta dama saman ta hagu yana kadawa, ya yatsina fuskarsa, wani sashe na zuciyarsa ya tunasar da shi.... Wardugu, amanar Ayya? Idan fa tana cikin wani hali? Gata bakuwa a wajen?

Agogon dakin ya kaiwa kallo, karfe biyu kennan, dan haka ya ajiye carbin hannunsa na dannawa ya mike ya fice a dakin nasa ba tare sa ya kashe komai ba nufinsa ya lekota ya dawo abinsa....

A hankali ya shiga, gannin tar dakin da haske ba.a kashe ba ya saka shi dan dudubata,
Hango tudu tudu saman bed ya saka shi gane tana sama baci take, aman ta shige gaba dayanta har kanta cikin bargon,

A hankali ya karasa bayan ya rufe dakin ya karasa har wajen gadon,
Hannunsa ya saka da niyar janye bargon, aman ta nadidiyeshi sosai kamarma bata samun isashen numfashi,

Kansa ya girgiza ya samu ya haye saman bed din da kyau, ya samu gefenta ya bude bargon kadan sannan ya saka hannunsa yana dan tapin din wajen da bai san ko menene ba yana kiram sunnanta a hankali,
Tsai ta yi da sauke lumfashi kafin ta bude idonta cike da nanauyan baci,
Shiru ta yi cike da tsoron meye? Waye? Wayo Allahna Ayya!
Ta fada can kasan makoshi kafin ta shiga neman wajen da zata yaye bargon jikinta sai bari yake,
Taimaka mata ya yo ta yaye bargon , inda gaba daya ta ruruko idannuwanta cike da tsoro take dubansa bayan ta dubi agogon bangon dakin fari kal mai adon dawissu fari kalkal da shi, ta ce" me me lafia? Me aka yi?

Wani kallo na kin raina min wayo ko? Ya yi mata kafin ya bi yanda gaba daya jikinta ke bari,
Da yatsarsa ya nunata ya ce" ke meye jikin ki ke rawa haka?

Agaishat ta hade hannayenta dan ta samu karfi karfi a jikinta, ta dube shi da kyau ta ganshi dare dare saman bed din da take tunanin nata ne na cikin dakinta ta ce" to aman me ka zo yi dakina karfe biyu na dare? Ko dai nan dakinka ne na kwonta har na yi baci?

Kan Uba, ido kawai ya zaro yana dubanta, a tunaninsa, salo ne irin na mata zatai masa na rainin wayo, lalalallala shi? Me ya zo yi inda take? Me yasa take son yi masa abinda zai iya mangareta ko ya dauke mata jinta ta hanyar wanka mata mari ne wai? Ko dan ta san baya son kai hannunsa jikinta ne?

Kafafuwansa ya tankwashe yana dubanta ya ce" zo,

Inda ya nuna mata ta kala, kusa da shi, koma tace gabansa, wai ta je?
Ido ta kikifta tana dubansa ta kasa motsawa daga inda take,

Kansa ya juyar yana tunani, wato shi bai isa ba ko? Bai kai wajen da zata zo gareshi ba ? Aman waninsa har yanai masa ikirarin ni.imarta?

Juyo da dubansa ya yi kanta, ransa ya fara baci ya mika hannunsa ya janyota jikinsa inda ta zo gaba dayanta luu ta shige jikinsa,
A ransa fadi yake kamar mage, aman a fili a hankali ya saka hannunsa ya dan dagota daga kwonciyar da ta yi jikinsa,
Fuskarta ya tsurawa ido yanda ta lumshe ido, a hankali ya kai dubansa kan lebunanta, duda ta yi baci man leben nan, bata side shi ba,
Yana kallon leben yana kara kusancin fuskarsa da tata, har ya hade lebensa da nata,.....
Lokaci guda ta bude idannuwanta tana zaro su,
Janye kanta ta so yi domin har ta yi nasarar raba lebenta da nasa dan kuwa dama ba wani harshensa ya zira bakinta ba, gannin tana neman daukaka rainin hankalinta a kansa ya saka shi rikota ya rike kanta da karfin da ba zata iya koda juyar da kan bane....
Ya yi haka ne dan ya horar da bakinta da fada masa magana gatsal, domin shi a ganninsa tana nan fitina da shi ne,
Sai dai ina , a hankali ya shiga sarafa yannayin kissing din, daga zafi zafi zuwa slowly,
A hankali ya sasauta rikon karfin da ya yi mata, sannan itama jikinta ya mutu ido kawai take zarowa cike da tsoro da mamakin bakinsa cikin nata? Wayo Allah, bata kara firgicewa ba sai da ta ga ya kai hannunsa bayan rigarta ya ja zif din rigar cikin wani yannayin da ba zata fadi lokacin da ya kai nan ba
,idannuwanta ta bude ta zuba cikin nasa kafin ta shiga mutsu mutsu da bakinta da ya mayar tamkar alewa a nasa tana fadin"umumumumumum sannan tana dan girgiza kanta da dan karfin da ya rage mata,
Aman me, gaba dayama sai ya kwontar da ita saman bed din ya yi mata runfa,
Bai tashi idasa rikice mata ba ya kasance idannuwansa sun rufe ba sai da ya ji bayin Allahn nan biyu tawaye fiye da yanda yake hasashe,
A hankali ya zare bakinsa daga nata ya bude idannuwansa da suka canza kala wa.inda ta yi dan daman bata hada ido da shi ba a wannan lokacin ya shiga yin kasa da kansa har wajen da bata tsamani............a takaice, a wannan rana, wajen karfe uku na dare, Wardugu ya yiwa Agaishat wani irin zuwa,
Ya salam bai yi haka dan ya cutar da ita ba, sai irin yanda ya kasa tsayar da kansa,
Wayo Wayo Wayo Allahna.... shi ne abinda ya yawaita fada , haka bayan ya samu nutsuwa zama ya yi ya dafe kansa ya tsurawa yannayin da ya kaita ido, cike da tausayawa, da wani matsanancin kaunarta ya koma gefenta ya rungumeta a jikinsa yana mai fadin.......

Ku yi hakuri, ba zan iya fayace wani lamari ba, 😔😔😔😔 bana iyawa😭

🐫🐫🐫🐫 *BAK'A CE* 🐫🐫🐫🐫

Na
*SAJIDA*

8️⃣2️⃣

*KUTKALE* (PRISON)

*AURE YAKIN MATA NE*

*KAMARTA, BATA DA NIYAR CUTARWA*

daga alkalamin yar mutan niger *SAJIDA* in sha Allah,

........kar ku bari a baku labari.....
Chapter 101 · 0% Book details