← Book details Bak'a Ce Part 1 Complet Hausa Novel Local reading mode
READING PART 57 OF 110

Sashe 57

Bak'a Ce Part 1 Complet Hausa Novel · about 8 min read

Amsawa Anna ta yi , sannan suka kara daidaita maganar inda dole dai da Gaishata za.a tafi dan ta kafe , yanzu kuwa Anna ta zama mai son y'ayanta, tausayinsu na mamaye zuciyarta, takan yi tir da wannan rayuwa, sai kuma ta godewa Allah da ya dawo da ita hanyacinta tun yanzu.

*After 2 weeks*
Paris

🐫🐫🐫🐫 *BAK'A CE* 🐫🐫🐫🐫

https://www.facebook.com/Idan-rana-ta-fito-writers-association-114558343535568/?referrer=whatsapp

*☀IDAN RANA TA FITO WRITER'S ASSO🌤* ____________________________________________

*Fad'akar da al'umma tare da nishad'antar da masoya shine fatanmu*😘🤝🏻😘

Na
*SAJIDA*

5️⃣6️⃣

Barka da juma.a

A kwanakin nan 14 da aka yi ,duka kaf Wardugu na nan , ba.inda ya je, yana tsaye kan lamarin amininsa, du wani abinda za.a fitar da kudi komai nauyinsu yakan karba ya je ya dawo da abinda aka bukata,
Ya kasance du idan lokacin cin abinci ya yi zai fita ya shigo masu kowa da nasa ci uku a yini,
Yakan yi jim idan ya ga sun yi jigum jigum ya ce da su" zai tashi, ku mu yi masa adu.a

Wannan abubuwan ya saka Khadija ta mugun zube kasa, wato ta ga ita ba komai bace a wajen son kyautatawa Mu.azam, wani irin girman wardugu da kwarjini, da kunyarsa suka karu a wajenta,
Ya kasance a yanzu ta yarda ba ita ta fi kowa son Mu.azam ba, sannan ta dan ja baya in dai Agaishat na wajen takan rage yawan leka wajen da Mu.azam din yake ma, sai dai idan bata nan kuma zata je ta tsurawa wajen ido,

Agaishat kanta da ya kasance kulun da sasafe zai zo ya dauketa su je asibiti, idan abinci zai je siya sai ta fadi wanda take iya ci, idan rana ta yi ya mayar da ita gida kuma sai bayan magariba ya daukota, duda ba wani hira ke hada su ba, sai kusancinsu ya karu, shakuwa ta shiga tsakaninsu, wanda hakan ba karamin illah ne ga dayansu ba,
Idan ya kawo abinci bata ci ba kuwa zai kama dago kansa jefi jefi yana duban abincin ya dubeta ya kawar da kansa, idan har ya ga lokacin cin abincin zai shige bata ci ba zai mike daga inda yake ya zo ya bude ya ajiye mata ba tare da yace da ita kala ba ya koma mazauninsa,
Kudi sun ji jiki, wai danma wasu abubuwan rabi yake biya albarkacin yana ma.aikacin asibitin, sannan likitocin nan tsaye suke kansa, baban likitan kansa ke kula da komai na Mu.azam har zuwa wannan rana inda suke tsaye a kofar su duka suna hangen likitoci uku dake tsaye kansa,
Tunda safe ya dace ya motsa, aman shiru ba alamu,
Wannan zuwansu na hudu ne wanda ya kama karfe shida daidai aman shiru Mu.azam bai motsa ba,
Zuciyoyi sun karaya, hankali ya tashi, a tsaye suke cir da kafafuwansa inda cikinsu ba wanda ya saka komai a bakinsa bale ya kai cikinsa, kai da azumi ma Wardugu ya tashi, su kuwa ba wace ta kula da wani cikinta ,
Agaishat hankalinta a karshen tashi yake, dan sala sala khadija ta kwatanta mata komai a jiya da yama, dan Gaskiyarta ta fadawa khadijar cewa ita ba karatun boko ta yi ba, bata san komai game da abinda ke faruwa ba,

Khadija ta yi mamaki ainun, daman wanda bai yi karatun boko yana iya zama wayis haka? Ita bata ga wani kauyanci a tare da Agaishat ba, ko aman da ta yi ta kelayawa a jirgi ta yi tunnanin ko irin mutanen nan ne da basa son tafiar jirgi ko mota yanzu sa kama amai, du kai kawon nan da ake a tunaninta ta gane komai idan likita ya fito ya yi bayani da french a tunaninta ta iya ta san me aka ce,
Kwarai ta ji ba dadi, ta yi tunanin da itace fa? Hakan ya sa ta zauna ta yi iya yinta da kwatance da cicirarar hausarta ta fada mata komai a nitse wanda sai da ta yi data sannin fada mata dan sai a lokacin Agaishat ta birkice fiye da da ta ringa irgen lokaci tana fadin ya taimaka ya buda ido, ita a barya ta je ta tashe shi,
Wannan karon wardugu bai iya wani tsawata mata ba, shima zuciyarsa a hautsine take

Jikinta duka rawa yake, a hankali ta kai hannunta wajen Khadija dake tsaye tamkar ba jini a jikinta ta damie hannunta ko zata ji sasaucin tsoron da take ciki,
Khadijarma ta rike hannun nata gamgam suna gannin yanda likitocin ke ta aune aune suna magana suna rubutu a takarda,

A yannayin da suka fito, dole ne hankali ya tashi,
Wannan karon kam ba wani boye boye suka tsaya gaban Wardugu, Khadija, da Agaishat suka yi masu bayannin bai farka ba kuma basu san dalili ba,
Sun auna basu ga abinda ya tare mashi farkawar ba,
Suna fadi ne fuskarsu cike da alhini,
Khadija ta kwala kara ta ce" non, non impossible non (no, no imposible no!),

Wardugu dai na duban likitan dake bayani, ya ci gaba fa fadin" cikin wasiyarsa ya bar maganar, in dai bai farka ba, kar a ci gaba da rayashi da inji, a cire masa injin dake taimakawa lumfashinsa a bar shi ya tafi, lokacinshi je ya yi ba yanda za.a yi, dan haka ku saka ranar da za.a cire masa na.urar dake bashi lumfashi,

Wayo ba za.a cire ba, wayo na shiga uku, Mu.azam kar ka yi kin haka, Wardugu ba za.a cire masa ba, in dai kuka cire mashi kun kashe ni nima walahi ko kwana daya ba zan kara ba sai dai ku kaimu mu biyu, khadija ke fada tana girgiza Wardugu kan kar ya saka hannu a wannan decision din,

Agaishat ta matso da sauri ta kama dayan hannun Khadija itama tana kuka a rikice da yaren buzanci ta ce" ya mutu ne? Ya mutu? Khadija Mijina ya mutu? Innalilahi wa.ina ilaihi raj.une ,
Ta cika hannun khadija ta damki na Wardugu fake tsaye yana dubansu zuru tamkar bai san yaren kowace cikinsu ba, tamkar wanda ya rayu cikin jeji shi kadai, sun zame masa sababin halita a gabansa,

Agaishat ta rike shi da kyau ya dago hannunsa ta dora gefen fuskarta ta girgiza hannun da kyar ta ce" Wardugu, ya mutu? Mutuwa ya yi? Wardugu ya mutu ne?

Wardugu ya janye hannayensa a jikin nasu ya juya da wani irin sauri ya fice a wajen baki daya,

Khadija ta zube kasa tana kuka inda likitocin abokannan aikinta ke rarashinta, Agaishat ta karasa jikin madubin ta jinginna kanta ta hadiye kukan a ranta ta shiga zabga masa adu.a tana tofawa tana duban ba.a rufe shi ba,

Wata likitar ta zo wajenta itama ta shiga rarashinta tana dafa kafadarta da yaren frency inda Agaishat dubanta kawai take aman bata san me take fada ba, ita dai zuciyarta ta cunkushe kukan ya tsaya cak, adu.a take ta yi kan Allah ya sa ba mutuwa ya yi ba!

Wardugu na fita ya je ya tsaya bakin titi ya tsurawa hanya ido,
Ba komai idannuwansa ke ganni ba sai zaman da suka yi da Mu.azam, abubuwa da dama wanda yawancinsu irin girman hakurinsa da zama da Wardugun ne, da wanda in ya juye wani sa.in sai an nemo Mu.azam din,

Ina son na rayu War, ina son na rayu na haihu nima na ga yarana sun girma, sai dai ban san ba ko zan samu haka?
Magangannun suka fadowa Wardugu a rai,
Idannuwansa ya rintse suka kara rikidewa sukai wani ja mai duhu!

Wani lokaci sun je kauye mai sunna Matamai nan yankin damagaran kusa da nigeria ya ga yanda garin keda ni.ima, tsarin rayuwar garin ta mugun birge shi inda ya nace sai da suka kara kwanaki kan wa.inda sukai niyar yi,
Suna lambu ne cikin garin sansayar iska na kada su yace" ka san Wani abu Wardugu?, duda an ce mutun idan ya mutu halayensa ke binsa, khairin ko sharin gwargwadon aikinsa gwargwadon kabarinsa, aman zan so na mutu a garinnan ni.imar garin ta yi min ,
Wardugu ya daki kafadarsa ya ce" sai kace wani saudiya? Kai fa haka kake motsi kadan mutuwa motsi kadan mutuwa, du inda ta zo fatan shine a cika da imani,

Ji yake jikinsa na yi masa nauyi, zuciyarsa ta cinkushe,
Wayarsa ke kuka kamar ta fasa aljihun wandonsa ta fito aman kunnayensa basa ji,
A fili ya ce" ya zaka bar wasiyoyinnan a kaina Mu.azam? Wa ya fada maka ni inada karfin zuciyar da zan iya saka hannu a takardar da zata bada damar a cire maka damar shakar numfashi ka tafi na dindindin? Wa ya fada maka cewar ni inada karfin da zan iya daukan gawarka na kaita inda zan kaita? Kai wama ya fada maka cewar ni din zan jure gannin an rufa maka dara? Innalilahi wa.ina ilaihi raj.une,!

Wayarsa ya lalubo jikinsa na wani irin kadawa , zafi kuwa ya dume masa jiki baki daya ya danna numbobin da bai yi tunanin idan an daga zai samu mutumen ba,

Da asalamu alaikum aka amsa wayar,

Wardugu ya ce" Mu.azam ne yace wai na saka hannu a takardar cire masa oxygene,

Shiru ya yi , inda hankalinsa ya tashi, murya a dan rikice ya ce" kana ina? Kuna ina?

Wardugu ya amsa da " muna paris, muna ma.aikatar Mu.azam, Mu.azam ya ki tashi!

Mikewa ya yi daga zaunen da yake , da hannunsa ya yiwa abokinsa alama da ya tafi ya fice ya nufi aeroport dan gannin ko zai samu jirgin da zai sada shi da Paris a yau yau, inda hali a yanzu????

😭

Wa Wardugu ya yi kira,?

MU.azam ya tafi kennan?

Agaishat, Khafija, Wardugu👏🏻🙁😢😔😔😔😔😔

🐫🐫🐫🐫 *BAK'A CE* 🐫🐫🐫🐫

https://www.facebook.com/Idan-rana-ta-fito-writers-association-114558343535568/?referrer=whatsapp

*☀IDAN RANA TA FITO WRITER'S ASSO🌤* ____________________________________________

*Fad'akar da al'umma tare da nishad'antar da masoya shine fatanmu*😘🤝🏻😘

Na
*SAJIDA*

5️⃣7️⃣

Tafia ta manya ce ya yi, in ba dan manyan ba daga shi sai suturar jikinsa sai cart dinsa ta banki, da ita ya ciri tiket, ya zauna yan mintuna inda jirgi ya daga da su, da ita ya ciri kudi ya yi shatar taxi ta kai shi asibiti
Chapter 57 · 0% Book details