Sashe 21
Bak'a Ce Part 1 Complet Hausa Novel · about 8 min read
Wardugu ya karaso ya zauna shima, ya ce" ka san dai kana iya yiwa kowa karya banda ni! So ka fada min tun kafin na hasala Mu.azam, wata irin cuta ce wannan wanda baka taba yi a gabana ba ta zugeka haka? Me ya samu kasan gashinka ? Kana tunanin ban lura ba? To gashinan kasan gashinka a aske! Sai ka janyo sauran ka rufe, du ka zama wani iri? Ka duba fa ka gani wandon vest ne a jikinka ka dauko riga rose (pink) ka saka sai kace mace? Hannunka ba agogo, yannayinka na nuna kama tare da damuwar da ta fi karfin furucinka, ina hawa aiki karfe goma na dare, ka fada mani na juya!
Mu.azan da wata irin murya ya ce" Cancer du cerveau ke damuna..... (cancer ta kai)
Wani irin tsam Wardugu ya yi, ya kaste maganarsa a lokacin da bai shirya ba,
Zurbat ya mike yana duban Mu.azam, hannayensa duka biyu ya saka ya dafe kansa, baya baya yake ja ya......
🐫🐫🐫 *BAK'A CE*🐫🐫🐫
Na *SAJIDA*
*بسم الله الرحمن الرحيم*
____________________________________
*🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
____________________________________
2️⃣4️⃣
Wani irin tsam Wardugu ya yi ya katse maganarsa a lokacin da bai shirya ba,
Zurbat ya mike, duban Mu.azam yake da wani irin kallo, hannayensa duka biyu ya kai saman kansa ya shiga yamutsa gashin kansa , baya baya ya shiga yi da kafafuwansa, bai fi taku hudu ba ya tsaya ya juya ya juyo, hanunsa ya jimke ya daki dayan da shi,
A hargitse ya dawo wajen Mu.azam, so yake ya zauna aman ya kasa...... murya a cinkushe ya ce" yaushe, yaushe? Yaushe ka sani? Ya aka yi ka sani?????
Mu.azam ya mike yana dan sakar masa murmushi yana kokarin ganin ya saka shi ya dan nutsu aman ya kasa kama shi, dan haka ya tsaya yana kallonsa ya ce" Wardugu, har na kai wajen da gashina baya zama fa, ya jima a jikina ciwon ....nima ina gannin alamu a matsayina na likita sai dai ina turewa na ki maida hankali, ya kai ni sai na suma na yi awani a sume, na daina shiga tiyata ba yau ba, ina zuwa asibiti ne dan kar imanina ya yi rauni, ina zuwa ne dan haduwa da wa.inda suka fi ni damuwa, ina yi mana adu.a a tare, Wardugu idan na jima a gabannan na kara shekara hudu a duniya,...
"C'est faut!,(KARYA NE!) Wardugu ya fada tun karfi yana nuno Mu.azam da yatsarsa,
Taku ya yi wajensa ya ce" idan kai ka fada, idanma wani sakaran likitan ya fada na fada karya kuke, karya ne Mu.azam, ku baku isa ku fadi abinda Allah ya boye ba, ba wani mahalukin da ya san ranar mutuwarsa , mutuwa bata shawara, bata fadi sai an ganta, mutuwa na zuwarwa bawa a lokacin da bai sani ba, sannan a lokacin da bai shirya ba domin a kulun bawa baya cikin shirinta,
Wardugu ya yi shiru, gaba daya ji yake jikinsa ba karfi, a hankali ya kai kasa ya zauna nan kasa, waje guda ya tsurawa ido kafin ya ci gaba da fadin" sannan Allah kadai ya san gawar fari, ba wai dan wane bashi da lafia wane lafiarsa kalau za.a ce sai marar lafiar nan ya rigayi mai lafia rasuwa,
Mu.azam da ya karaso , a hanakli ya duka ya dora hannayensa saman na Wardugu, murya a raunane ya ce" ban taba tunanin wani abin zai girgizaka haka ba Wardugu, menene a ciki? Ko dan abin ya shafeka ne baka so ka ji? Wardugu ka yi hakuri, ka daina tayar da hankalinka kan maganar nan, nima na fada maka ne dan na ji sanyi sannan na samu wanda ya san ciwona, Wardugu ka....
Bai tsamaci lamarin ba, sai jinsa ya yi jikin Wardugu, Wardugu da dan ya tsokane shi yake ce masa sai sun yi gaisiwar larabawa, yau gashi da kansa ya rungume shi,
Murya a cunkushe wardugu ya ce" bana so bana so.....
Kasa karasawa ya yi kuma ya saki Mu.azam ya mike ya fice da wani irin sauri .......
A hankali Mu.azam ya hade kansa da gwuiwarsa, , tabas mutuwa Aya ce, duk mai rai mamaci ne, tabas ba karamar ni.ima bane da Allah ya boyewa bayi ranar mutuwarsu, shi gashi, hasashe ne aka yi, likitoci sukai a kansa, rayuwar turai da za.a fada maka komai kwaro kwaro ne, sun kiyasta lokacin da suke gani zai kai a raye a doron kasa sun fada masa, wai basu fada masa rana da lokaci bama aman gashi du ya firgice ya fice a hayacinsa,
Idannuwansa ya lumshe yana jin saukar zazafan hawayensa, zuciyarsa ce ta ci gaba da fada masa" ka zo kasar nan je dan ka kara ninninka ibadunka, ka kara yawaita sadaka da aikata abubuwan alkhairi, ka zo kasar nan ne dan ka samu ka raya sunnar ma.aiki idan Allah ya nufeka, mutuwa kowa yi zai yi Mu.azam, ka daina karaya ka yi hakuri har Allah ya yi ikonsa a kanka,
Wayarsa ce ta dauki kuka ya kai dubansa wajen wayar ya mike daga tsugunnin nan ya daukota ya daga,
Docter me ka yi kennan? Na zo wajen aiki na tarar da takardar barin aikin ka? Saboda ni kake son yin nesa da aikinka ko saboda na fada maka ka yi hakuri a yi maka aikin nan? ......
Kansa ya shafa yana sauraronta, masoyiyarsa wace ke nuna masa kauna, tana son Mu.azam tamkar nama daya na cikin miya, tana son kasancewa da shi, labarin rashin lafiarsa ya gigitata har itama ta kwonta, nan ne ta yi ta fadi tashi har ta gano ana iya yi masa aiki a cire wajen, aman aikin ne keda hatsari sosai, yana iya samun tabuwar tunaninsa, ko ya kasance ya shiga coma wace shigekan daga ita ba zai tashi ba, ko idan Allah ya aminta ya yi jinya sumul ya samu sauki aman shi ya kara kai da kasa ba zai harda a wani buda kansa ba a dawo kuna ba wani succes,
MU.azam ya ce" Aisha,
Aisha ta ce" ka dawo na roke ka, ka dawo tun kafin lokacin a iya yi maka aiki ya shige,
Ki yi hakuri ki daina kirana Aisha, Mu.azam ya fada da sanyin murya, ya ci gaba da fadin" nawa kuka yiwa aikin? Nawa suka fita? Karshe dai du yawanci daga dakin aikin za.a fitar da su basu san inda kansu yake ba, zasu dawo kulun a jone da inji yana taimaka masu wajen numfashi, da na.urori masu basu abinci, da masu jan fitsari da masu karban kashin su, zasu dauki lokaci a wannan yannayin har ya kasance ko a cire masu na.urorin ko dare daya su tsaya sun daina aiki, su basu dauki kadara suka yi ta ibada suna shinfida a makwoncinsu na gaskiya ba, su basu san a inda suke tsakannin duniya da lahira ba, Aisha, Allah ya dora mani, ba zan kai labari ba! Ki yi hakuri......
Yana gama fadar haka ya katse kiran,
Docter Aisha dake kai kawo tsakannin dakinta da falonta ta dafe kai ta fashe da kuka, yar balaraba kyakyawa da ita, a fili ta furta" innalilahi wa.ina ilaihi raj.une, Mu.azam, in sha Allah zaka warke, sai mun rayu da kai Mu.azam.......
(😔😔😔😔😔😔)
Bayan sati uku
Ayya ce zaune tana nunawa Agaishat yanda ake gyara lale ja domin tana son kunsa mata ne,
Bayan ta tankade shi lukui ta kawo mahanabiya ta zuba masa sannan ta zuba dan madaidaicin ruwa ta kwabe shi sosai ya yi shar da shi ta zuba dan ruwa gefe ta ajiye tana kallon Agaishat ta ce" yi ki wanke kafar mana Agaishat, kin ga yayanki Mu.azam ya ce zaku fita ku zaga gari , ni kuwa na fi so idan mun gama kunshin nan sai ku tafi....
Agaishat ta yi sauri ta shiga darwaye kafar nata ta cire ta dauke ruwan ta kai ta zubar ta dawo ta dauki abin goge kafar ta gogoge ruwan kafin take zama ta tankwashe kafafiwanta Ayya ta shiga daura mata iskwace tana fadin"ki lura dan gobe ki daura abinki kin ji Yar Ayya,
Agaishat ta gyada kai tana murmushi, a kowani lokaci a kowani yannayi ta tsinci kanta tunda ta sauke kafarta a gidan Ayya sai iyayenta da yan uwanta da baba sofo sun fado a ranta, bale yanzu Wardugu kansa da yake yawan hararata a farkp ya daina, shi dai baya shiga lamarinta aman baya hana wani shiga, Alhinayettt ma tana lekowa wani sa.in idan Wardugu na gidan su sha hira da yaren buzanci domin tana jin dadin jin yaren raurau ana hira da ita ba wani kyama, sosai Alhinayettt ke dan gwada mata wasu abubuwan, da hikima take nuna mata wasu yan al.adun yan birni sannan Mu.azam na mugumugun sakata a jiki, yana sakar mata fuska fiye da tunanin mai karatu, idan ta kali kayayakinta, suturun da suke malakinta a yanzu, sai ta ji hawaye na neman zubo mata, tunaninta me yan uwanta suke sakawa a yanzu? Wani hali suke ciki? Jiya i yau ne ki Baba ya canza halayensa?
Sai dai takan bi su da adu.a kawai, itace kadai abinda take iya yi masu a yanzu, kuma tanaiwa iyayen rikonta adu.ar gamawa da duniya lafia, ba.a wani sakata makarantar boko ba domin shekarunta sun tafi shekara goma sha takwas har ta kusa cike sha tara, aman a gida Ayya na koya mata abinda ya sawaka sai karatun islamiya da ta kara zurfafawa sosai tana kara neman ilimin adininta.
Mu.azan da wata irin murya ya ce" Cancer du cerveau ke damuna..... (cancer ta kai)
Wani irin tsam Wardugu ya yi, ya kaste maganarsa a lokacin da bai shirya ba,
Zurbat ya mike yana duban Mu.azam, hannayensa duka biyu ya saka ya dafe kansa, baya baya yake ja ya......
🐫🐫🐫 *BAK'A CE*🐫🐫🐫
Na *SAJIDA*
*بسم الله الرحمن الرحيم*
____________________________________
*🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
____________________________________
2️⃣4️⃣
Wani irin tsam Wardugu ya yi ya katse maganarsa a lokacin da bai shirya ba,
Zurbat ya mike, duban Mu.azam yake da wani irin kallo, hannayensa duka biyu ya kai saman kansa ya shiga yamutsa gashin kansa , baya baya ya shiga yi da kafafuwansa, bai fi taku hudu ba ya tsaya ya juya ya juyo, hanunsa ya jimke ya daki dayan da shi,
A hargitse ya dawo wajen Mu.azam, so yake ya zauna aman ya kasa...... murya a cinkushe ya ce" yaushe, yaushe? Yaushe ka sani? Ya aka yi ka sani?????
Mu.azam ya mike yana dan sakar masa murmushi yana kokarin ganin ya saka shi ya dan nutsu aman ya kasa kama shi, dan haka ya tsaya yana kallonsa ya ce" Wardugu, har na kai wajen da gashina baya zama fa, ya jima a jikina ciwon ....nima ina gannin alamu a matsayina na likita sai dai ina turewa na ki maida hankali, ya kai ni sai na suma na yi awani a sume, na daina shiga tiyata ba yau ba, ina zuwa asibiti ne dan kar imanina ya yi rauni, ina zuwa ne dan haduwa da wa.inda suka fi ni damuwa, ina yi mana adu.a a tare, Wardugu idan na jima a gabannan na kara shekara hudu a duniya,...
"C'est faut!,(KARYA NE!) Wardugu ya fada tun karfi yana nuno Mu.azam da yatsarsa,
Taku ya yi wajensa ya ce" idan kai ka fada, idanma wani sakaran likitan ya fada na fada karya kuke, karya ne Mu.azam, ku baku isa ku fadi abinda Allah ya boye ba, ba wani mahalukin da ya san ranar mutuwarsa , mutuwa bata shawara, bata fadi sai an ganta, mutuwa na zuwarwa bawa a lokacin da bai sani ba, sannan a lokacin da bai shirya ba domin a kulun bawa baya cikin shirinta,
Wardugu ya yi shiru, gaba daya ji yake jikinsa ba karfi, a hankali ya kai kasa ya zauna nan kasa, waje guda ya tsurawa ido kafin ya ci gaba da fadin" sannan Allah kadai ya san gawar fari, ba wai dan wane bashi da lafia wane lafiarsa kalau za.a ce sai marar lafiar nan ya rigayi mai lafia rasuwa,
Mu.azam da ya karaso , a hanakli ya duka ya dora hannayensa saman na Wardugu, murya a raunane ya ce" ban taba tunanin wani abin zai girgizaka haka ba Wardugu, menene a ciki? Ko dan abin ya shafeka ne baka so ka ji? Wardugu ka yi hakuri, ka daina tayar da hankalinka kan maganar nan, nima na fada maka ne dan na ji sanyi sannan na samu wanda ya san ciwona, Wardugu ka....
Bai tsamaci lamarin ba, sai jinsa ya yi jikin Wardugu, Wardugu da dan ya tsokane shi yake ce masa sai sun yi gaisiwar larabawa, yau gashi da kansa ya rungume shi,
Murya a cunkushe wardugu ya ce" bana so bana so.....
Kasa karasawa ya yi kuma ya saki Mu.azam ya mike ya fice da wani irin sauri .......
A hankali Mu.azam ya hade kansa da gwuiwarsa, , tabas mutuwa Aya ce, duk mai rai mamaci ne, tabas ba karamar ni.ima bane da Allah ya boyewa bayi ranar mutuwarsu, shi gashi, hasashe ne aka yi, likitoci sukai a kansa, rayuwar turai da za.a fada maka komai kwaro kwaro ne, sun kiyasta lokacin da suke gani zai kai a raye a doron kasa sun fada masa, wai basu fada masa rana da lokaci bama aman gashi du ya firgice ya fice a hayacinsa,
Idannuwansa ya lumshe yana jin saukar zazafan hawayensa, zuciyarsa ce ta ci gaba da fada masa" ka zo kasar nan je dan ka kara ninninka ibadunka, ka kara yawaita sadaka da aikata abubuwan alkhairi, ka zo kasar nan ne dan ka samu ka raya sunnar ma.aiki idan Allah ya nufeka, mutuwa kowa yi zai yi Mu.azam, ka daina karaya ka yi hakuri har Allah ya yi ikonsa a kanka,
Wayarsa ce ta dauki kuka ya kai dubansa wajen wayar ya mike daga tsugunnin nan ya daukota ya daga,
Docter me ka yi kennan? Na zo wajen aiki na tarar da takardar barin aikin ka? Saboda ni kake son yin nesa da aikinka ko saboda na fada maka ka yi hakuri a yi maka aikin nan? ......
Kansa ya shafa yana sauraronta, masoyiyarsa wace ke nuna masa kauna, tana son Mu.azam tamkar nama daya na cikin miya, tana son kasancewa da shi, labarin rashin lafiarsa ya gigitata har itama ta kwonta, nan ne ta yi ta fadi tashi har ta gano ana iya yi masa aiki a cire wajen, aman aikin ne keda hatsari sosai, yana iya samun tabuwar tunaninsa, ko ya kasance ya shiga coma wace shigekan daga ita ba zai tashi ba, ko idan Allah ya aminta ya yi jinya sumul ya samu sauki aman shi ya kara kai da kasa ba zai harda a wani buda kansa ba a dawo kuna ba wani succes,
MU.azam ya ce" Aisha,
Aisha ta ce" ka dawo na roke ka, ka dawo tun kafin lokacin a iya yi maka aiki ya shige,
Ki yi hakuri ki daina kirana Aisha, Mu.azam ya fada da sanyin murya, ya ci gaba da fadin" nawa kuka yiwa aikin? Nawa suka fita? Karshe dai du yawanci daga dakin aikin za.a fitar da su basu san inda kansu yake ba, zasu dawo kulun a jone da inji yana taimaka masu wajen numfashi, da na.urori masu basu abinci, da masu jan fitsari da masu karban kashin su, zasu dauki lokaci a wannan yannayin har ya kasance ko a cire masu na.urorin ko dare daya su tsaya sun daina aiki, su basu dauki kadara suka yi ta ibada suna shinfida a makwoncinsu na gaskiya ba, su basu san a inda suke tsakannin duniya da lahira ba, Aisha, Allah ya dora mani, ba zan kai labari ba! Ki yi hakuri......
Yana gama fadar haka ya katse kiran,
Docter Aisha dake kai kawo tsakannin dakinta da falonta ta dafe kai ta fashe da kuka, yar balaraba kyakyawa da ita, a fili ta furta" innalilahi wa.ina ilaihi raj.une, Mu.azam, in sha Allah zaka warke, sai mun rayu da kai Mu.azam.......
(😔😔😔😔😔😔)
Bayan sati uku
Ayya ce zaune tana nunawa Agaishat yanda ake gyara lale ja domin tana son kunsa mata ne,
Bayan ta tankade shi lukui ta kawo mahanabiya ta zuba masa sannan ta zuba dan madaidaicin ruwa ta kwabe shi sosai ya yi shar da shi ta zuba dan ruwa gefe ta ajiye tana kallon Agaishat ta ce" yi ki wanke kafar mana Agaishat, kin ga yayanki Mu.azam ya ce zaku fita ku zaga gari , ni kuwa na fi so idan mun gama kunshin nan sai ku tafi....
Agaishat ta yi sauri ta shiga darwaye kafar nata ta cire ta dauke ruwan ta kai ta zubar ta dawo ta dauki abin goge kafar ta gogoge ruwan kafin take zama ta tankwashe kafafiwanta Ayya ta shiga daura mata iskwace tana fadin"ki lura dan gobe ki daura abinki kin ji Yar Ayya,
Agaishat ta gyada kai tana murmushi, a kowani lokaci a kowani yannayi ta tsinci kanta tunda ta sauke kafarta a gidan Ayya sai iyayenta da yan uwanta da baba sofo sun fado a ranta, bale yanzu Wardugu kansa da yake yawan hararata a farkp ya daina, shi dai baya shiga lamarinta aman baya hana wani shiga, Alhinayettt ma tana lekowa wani sa.in idan Wardugu na gidan su sha hira da yaren buzanci domin tana jin dadin jin yaren raurau ana hira da ita ba wani kyama, sosai Alhinayettt ke dan gwada mata wasu abubuwan, da hikima take nuna mata wasu yan al.adun yan birni sannan Mu.azam na mugumugun sakata a jiki, yana sakar mata fuska fiye da tunanin mai karatu, idan ta kali kayayakinta, suturun da suke malakinta a yanzu, sai ta ji hawaye na neman zubo mata, tunaninta me yan uwanta suke sakawa a yanzu? Wani hali suke ciki? Jiya i yau ne ki Baba ya canza halayensa?
Sai dai takan bi su da adu.a kawai, itace kadai abinda take iya yi masu a yanzu, kuma tanaiwa iyayen rikonta adu.ar gamawa da duniya lafia, ba.a wani sakata makarantar boko ba domin shekarunta sun tafi shekara goma sha takwas har ta kusa cike sha tara, aman a gida Ayya na koya mata abinda ya sawaka sai karatun islamiya da ta kara zurfafawa sosai tana kara neman ilimin adininta.