Sashe 67
Bak'a Ce Part 1 Complet Hausa Novel · about 8 min read
Ayya bata da yanda zata yi, na farko dai ita ta yi imanin idan da zuciya biyu ne Allah zai iya masu, na biyu ko ba komai ta ji dadin ashe matar dan nata ta san bata kyautawa ? Duda bata nemeta ba sai a yanzu da take gannin ta masa madaukakin laifi? Na uku gaskiya ne, yayan yanzu sunna abubuwa ne gabam kansu, ba zata so a saki yar wani ba dan an saki tata bata ji dadi ba, a gaskiya sakin da akaiwa Agaishat ta ji shi har cikin ranta, dan haka ta amince ta zauna nan gidanta na dan lokaci har ta iya da lamarin Wardugu sai ta koma dakinta,
Duda ba haka suka so ba, sun so ne ta yi kiransa a lokacin ta bashi umarni, aman sai suka hakura dan matakin da suka taka na neman galaba kar ya kubuce masu,
Dalilin da ya saka Walyn ke zaune a gidan Ayya yau kwana biyu, inda take cikin dakin da yake na Mu.azam, domin dakin Wardugu daman Agaishat ta zaune shi ,
Tana zaune a gidan ne ba tare da shiga sabgar kowa ba, idan lokacin cin abinci ya yi mai aiki zata je ta fada mata, wani lokacin ta fito a ci da ita inda tana ci tana dana waya, wani lokacin kuwa tace bata ci sai sun gama ci ta zo ta diba ta ci,
Sai abinda ke bata mamaki irin yanda yarinyar nan yar kauye da suka dauko ta zama, duka dukama wani lokaci ta dauka a gidan? Aman cikin ikon Allah yarinyar ta wanku ta zama wata big girls irin yayan yan gayun nan, komanta irin na yan gayu ne, ita tambayace cike da cikinta, ba ita bace Mu.azam ya aura? To ina Mu.azam din? Duda tana yawan zama da doguwar riga da dan kwalinta a kanta, bata wani harkar samari dan Ayya na kilaceta wai ida take, sai karatu da aka daukar mata malamar makaranta dake zuwa tana koyar da ita sau biyu a wuni dan Agaishat dai ba komai take yi ba, ita kuwa malamar apbashin koyar da agaishat din yama fi na wanda ake biyanta a makaranta , dan haka ta rike damarta take aikinta da zuciya daya inda suke bi a hankali suna karatun su,
Ba abinda ke hada su , dan walyn bata taba zuwa ta tarar da Agaishat zaune ta nuna ta san da mutun a wajen ko ta yi kata salama ba, itama Agaishat ta gwada gaisheta sau uku aman Walyn bata amsawa dan haka sai ta kama kanta, domin wani yatsina fuska Walyn take idan ta ganta, wai yar kauye ta samu waje,
Zaune suke a fali, Ayya na saman kujera baba inda Agaishat ke zaune kasa da litafi a hannunta tana bitar hada sunna tana karantawa a hankali Ayya na gyara mata wajen gyarawa,
Bayan sati biyu
Fitowa ta yi ta sha shada tana baza kamshi ta dan tsaya nesa da su Ayya kadan ta ce" Ayya, zan je wajen auren kawar tawa,
Ayya ta dago tana dubanta, ta so ta share ta tafin, sai dai fa tunanin yanzu fa a wuyanta take ya saka ta ce" bari na fadawa mijinki,
Wayarta ta saka Agaishat ta dauko mata domin wayar a kashe take wajen sati biyu kennan dan kara nunawa Wardugu tsananin fushin da take ciki,
Agaishat ta mike yau kuma da yake ta san ba wani namijin dake shigo masu iya su ne, dogon wando ne jikinta mai dan santsi sannan daga kasa da irin igiyar nan ta daure kasan da shi, bai kamata ba aman ya bi shap din jikinta, sai fara kar din riga body wace bata da kwaliyar komai jikinta, sai dan kwali karami da ta yane gaban goshinta da shi , idan ka ganta kamar irin beautiful din balck americain din nan, ga kamshin turaran wankanta mai karawa fata santsi da take bazawa du idan ta gita,
Da ido Walyn ta bita kafin take yatsina fuska, kamar tace a barshi kar a yi kiransa dan bata so, ko da wasa bata shirya tarbansa a yanzu yanzu ba, ita gaba ta kaita rashin zuwansa gidan, da farko a dari dari take daga baya ta sake abinta take lamuranta hankali kwonce , ba abinda ta nema ta rasa, dan haka ta kwontar da hankalinta ta san dai ko ba jima zai nemeta tunda bai saketa ba,
Kafinma Agaishat ta dawo da wayar karan dankareren babur din nan nasa ya isar da zuwansa gidan,
Wani irin juyawa Walyn ta yi wajen kofar gabanta na faduwa da wani irin sauti da cikinta ya bada, Wardugu ne a gidan warhaka?
Ai bata san lokacin da ta cire dogon takalmin nata ta jefar nan bayan kujerar Ayya ta yi sauri ta karasa saman cafet ta zauna ba saman kujera ba,
Ayya dake binta da kallo ta dago sukai ido hudu, wata kunya ta ji ta kamata, tunda suke bata taba zama a kasa Ayya ta zauna a sama a matsayinta na wace ta girmeta bale a je ga maganar sirikarta, zama take duwaiwanta da nata ba abinda ya shafeta aman yanzu da ta ji motsin Wardugu ta zo da gudu ta zauna a kasa,
Murmushi Ayya ta yi tana waiwayawa dan jin tafiar Agaishat wato ta dauko wayar,
Tana saukowa shi kuwa yana shigowa,
Matatakalar ba a saitin kofar shigowar take ba aman dan fitina idannuwansa suka hasko masa ita ta cikin bakin gilashin da ya saka,
Kara kicin kicin ya yi da fuska ya maido dubansa wajen Ayya wace itama ta hade fuska inda Agaishat ta juya da gudu ta koma dan saka hijab
Harga Allah bai ga Walyn ba, domin tunaninsa ba zai taba kawo masa wai Walyn na zaune a gidansu ba, sannan Walyn a kasa a zaune? Bai kawowa ransa haka ba, dan haka ya karasa kujerar dake facing din Ayya ya zauna yana kallon Fuskar Ayya, a ransa ya ayyana bata huce ba dai,
Murmushi ya yi kafin ya ce" Maman Wardugu barka da yama,
Ayya ta zabga masa harara kafin ta ce" ni zaka gaisar da gilash?
Cire gilash din ya yi wanda ya saka ta ga idannuwansa sun yi ja, ko na meye oho?
Wardugu na cirewa ya ce" ina son Ayyana 👏🏻
Ayya ta yatsina baki tana duban Walyn, hakan da ta yi ya saka shi duban inda take kallo,
Zoben hannunta na zinari ya toni ko wacece domin shi ya sayi zoben,,
Juyar da kansa ya yi tamkar bai gane wacece ba, kamarma bai ga wanda ke zaune ba,
Ayya ta girgiza kanta dan sarai ta san ya gane ko waye aman ya wani basar,
Ayya ta ce" kai, mace na karkashinka aman bata gidanka tsayin wannan lokacin baka bibiyi inda take ba? Kana da lafia kuwa Wardugu?
Wardugu ya kaleta irin kallon nan na tsai, murmushi ya yi ,
Ayya ta ce" wani ahu ta yi maka ne?
Wardugu ya girgiza kai bai yi magana ba,
Ayya ta ce" Wardugu ka min magana mana ko kurma ka zama?
Wardugu ya yi murmushi dan kuwa ko ba komai yanda ta masa magana haka ya ji dadi, dan haka ya ce" wace matata?
Ayya ta kale shi inda Walyn ta dago da sauri itama tana dubansa,
Ayya ta hade fuska ta ce" ka dauki matarka ku koma gidanku , koma me ta yi ka yi hakuri ,
Wardugu ya dago da sauri ya ce" Ayya?
Ayya ta hade fuska ta kawar da kanta ta ce" na ce ka yi hakuri.
Wardugu ya dan matso bakin kujerar,
Hannunsa mai dauke da zoben azurfa ya dago a hankali ya shafo kansa zuwa sajensa,, ya yi haka sau wajen biyu kafin yake dan dagowa ya kalli Ayya, itama shi take kallo sannan da idannuwanta ta nuna masa da ya bi umarninta,
Wani murmushi mai ciwo ya sakar mata kafin yake dan muzgutawa ya koma cikin kujerar ya zauna ,
Ayya ta dubi wajen Walyn dake zaune ta ce" ki tashi ki koma dakinki, ki kiyaye dukan abinda mahaifiyarki ta fada
Mikewa ta yi zurbat ta dan sosa kanta tana duban Ayya, aman batai masa gargadin kar ya mata wani abin ko ya daina fushin da yake da ita ba,
Sai dai ba halin ta kawo maganar domin ko a fuskar Ayyan bata ga fuska ba,
Dan haka ta samu ta raba Ayya ta fice da sauri ta shiga motarta ta nufi gidanta.
Tana fita Ayya ta maido hankalinta wajensa tana dubansa, ta sani sarai shirunnan da ya yi gwara ya yi magana, aman sai ta share, idan tana son tankwasa shi bata nuna wani tausayi ko tsoron zuciya,
Rai ta hade ta ce" an yi maka laifi mai girma, ka yi hakuri , kar ka ci gaba da nuna mata wani abin, ka kwontar da hankalinka, dukan tsanani yana tare da sauki.
Idannuwansa ya lumshe ya kai dubansa wajen matatakalar Ayya, kansa ya juyo yana duban Ayya ya ce" alfarma faya nake nema a wajenki Ayyana,
Ayya dake dubansa ta ce" wace alfarma ce?
Idan na tashi neman aure , ina so tsakanina da ke ki sanya mani albarka, ba ruwanki da maganar wani al.adu da me za.a dube ki, Ayya bafa adini bane, dan na taka ba Allah zai kama ni ba, ba kuma wani zqi hana mini ci ko sha ba, ba wanda zai hana ni shiga inda nake so, hasalima koda za.a yi da ni sai dai a yi a boye, ki toshe kunnayenki na roke ki!
Ayya ido kawai ta zuba masa, zata fi kowa murnar gannin wardugunta ya samu wani canji bangaren mata,
Ya kasance mai farin jinnin mata, suna likun masa a duk inda ya saka kafarsa, sai dai abin takaicin cikin matan nan wa.inda ya samu wani kusanci da su du sun saka ya ji dan damanma, har yanaiwa mata kallon zuma daga nesa, idan suka karaso gareka sun zama madaci,
Me ya rasa? Ya kasance namiji har namiji sai dai ya rasa macen mutunci,
Duda ba haka suka so ba, sun so ne ta yi kiransa a lokacin ta bashi umarni, aman sai suka hakura dan matakin da suka taka na neman galaba kar ya kubuce masu,
Dalilin da ya saka Walyn ke zaune a gidan Ayya yau kwana biyu, inda take cikin dakin da yake na Mu.azam, domin dakin Wardugu daman Agaishat ta zaune shi ,
Tana zaune a gidan ne ba tare da shiga sabgar kowa ba, idan lokacin cin abinci ya yi mai aiki zata je ta fada mata, wani lokacin ta fito a ci da ita inda tana ci tana dana waya, wani lokacin kuwa tace bata ci sai sun gama ci ta zo ta diba ta ci,
Sai abinda ke bata mamaki irin yanda yarinyar nan yar kauye da suka dauko ta zama, duka dukama wani lokaci ta dauka a gidan? Aman cikin ikon Allah yarinyar ta wanku ta zama wata big girls irin yayan yan gayun nan, komanta irin na yan gayu ne, ita tambayace cike da cikinta, ba ita bace Mu.azam ya aura? To ina Mu.azam din? Duda tana yawan zama da doguwar riga da dan kwalinta a kanta, bata wani harkar samari dan Ayya na kilaceta wai ida take, sai karatu da aka daukar mata malamar makaranta dake zuwa tana koyar da ita sau biyu a wuni dan Agaishat dai ba komai take yi ba, ita kuwa malamar apbashin koyar da agaishat din yama fi na wanda ake biyanta a makaranta , dan haka ta rike damarta take aikinta da zuciya daya inda suke bi a hankali suna karatun su,
Ba abinda ke hada su , dan walyn bata taba zuwa ta tarar da Agaishat zaune ta nuna ta san da mutun a wajen ko ta yi kata salama ba, itama Agaishat ta gwada gaisheta sau uku aman Walyn bata amsawa dan haka sai ta kama kanta, domin wani yatsina fuska Walyn take idan ta ganta, wai yar kauye ta samu waje,
Zaune suke a fali, Ayya na saman kujera baba inda Agaishat ke zaune kasa da litafi a hannunta tana bitar hada sunna tana karantawa a hankali Ayya na gyara mata wajen gyarawa,
Bayan sati biyu
Fitowa ta yi ta sha shada tana baza kamshi ta dan tsaya nesa da su Ayya kadan ta ce" Ayya, zan je wajen auren kawar tawa,
Ayya ta dago tana dubanta, ta so ta share ta tafin, sai dai fa tunanin yanzu fa a wuyanta take ya saka ta ce" bari na fadawa mijinki,
Wayarta ta saka Agaishat ta dauko mata domin wayar a kashe take wajen sati biyu kennan dan kara nunawa Wardugu tsananin fushin da take ciki,
Agaishat ta mike yau kuma da yake ta san ba wani namijin dake shigo masu iya su ne, dogon wando ne jikinta mai dan santsi sannan daga kasa da irin igiyar nan ta daure kasan da shi, bai kamata ba aman ya bi shap din jikinta, sai fara kar din riga body wace bata da kwaliyar komai jikinta, sai dan kwali karami da ta yane gaban goshinta da shi , idan ka ganta kamar irin beautiful din balck americain din nan, ga kamshin turaran wankanta mai karawa fata santsi da take bazawa du idan ta gita,
Da ido Walyn ta bita kafin take yatsina fuska, kamar tace a barshi kar a yi kiransa dan bata so, ko da wasa bata shirya tarbansa a yanzu yanzu ba, ita gaba ta kaita rashin zuwansa gidan, da farko a dari dari take daga baya ta sake abinta take lamuranta hankali kwonce , ba abinda ta nema ta rasa, dan haka ta kwontar da hankalinta ta san dai ko ba jima zai nemeta tunda bai saketa ba,
Kafinma Agaishat ta dawo da wayar karan dankareren babur din nan nasa ya isar da zuwansa gidan,
Wani irin juyawa Walyn ta yi wajen kofar gabanta na faduwa da wani irin sauti da cikinta ya bada, Wardugu ne a gidan warhaka?
Ai bata san lokacin da ta cire dogon takalmin nata ta jefar nan bayan kujerar Ayya ta yi sauri ta karasa saman cafet ta zauna ba saman kujera ba,
Ayya dake binta da kallo ta dago sukai ido hudu, wata kunya ta ji ta kamata, tunda suke bata taba zama a kasa Ayya ta zauna a sama a matsayinta na wace ta girmeta bale a je ga maganar sirikarta, zama take duwaiwanta da nata ba abinda ya shafeta aman yanzu da ta ji motsin Wardugu ta zo da gudu ta zauna a kasa,
Murmushi Ayya ta yi tana waiwayawa dan jin tafiar Agaishat wato ta dauko wayar,
Tana saukowa shi kuwa yana shigowa,
Matatakalar ba a saitin kofar shigowar take ba aman dan fitina idannuwansa suka hasko masa ita ta cikin bakin gilashin da ya saka,
Kara kicin kicin ya yi da fuska ya maido dubansa wajen Ayya wace itama ta hade fuska inda Agaishat ta juya da gudu ta koma dan saka hijab
Harga Allah bai ga Walyn ba, domin tunaninsa ba zai taba kawo masa wai Walyn na zaune a gidansu ba, sannan Walyn a kasa a zaune? Bai kawowa ransa haka ba, dan haka ya karasa kujerar dake facing din Ayya ya zauna yana kallon Fuskar Ayya, a ransa ya ayyana bata huce ba dai,
Murmushi ya yi kafin ya ce" Maman Wardugu barka da yama,
Ayya ta zabga masa harara kafin ta ce" ni zaka gaisar da gilash?
Cire gilash din ya yi wanda ya saka ta ga idannuwansa sun yi ja, ko na meye oho?
Wardugu na cirewa ya ce" ina son Ayyana 👏🏻
Ayya ta yatsina baki tana duban Walyn, hakan da ta yi ya saka shi duban inda take kallo,
Zoben hannunta na zinari ya toni ko wacece domin shi ya sayi zoben,,
Juyar da kansa ya yi tamkar bai gane wacece ba, kamarma bai ga wanda ke zaune ba,
Ayya ta girgiza kanta dan sarai ta san ya gane ko waye aman ya wani basar,
Ayya ta ce" kai, mace na karkashinka aman bata gidanka tsayin wannan lokacin baka bibiyi inda take ba? Kana da lafia kuwa Wardugu?
Wardugu ya kaleta irin kallon nan na tsai, murmushi ya yi ,
Ayya ta ce" wani ahu ta yi maka ne?
Wardugu ya girgiza kai bai yi magana ba,
Ayya ta ce" Wardugu ka min magana mana ko kurma ka zama?
Wardugu ya yi murmushi dan kuwa ko ba komai yanda ta masa magana haka ya ji dadi, dan haka ya ce" wace matata?
Ayya ta kale shi inda Walyn ta dago da sauri itama tana dubansa,
Ayya ta hade fuska ta ce" ka dauki matarka ku koma gidanku , koma me ta yi ka yi hakuri ,
Wardugu ya dago da sauri ya ce" Ayya?
Ayya ta hade fuska ta kawar da kanta ta ce" na ce ka yi hakuri.
Wardugu ya dan matso bakin kujerar,
Hannunsa mai dauke da zoben azurfa ya dago a hankali ya shafo kansa zuwa sajensa,, ya yi haka sau wajen biyu kafin yake dan dagowa ya kalli Ayya, itama shi take kallo sannan da idannuwanta ta nuna masa da ya bi umarninta,
Wani murmushi mai ciwo ya sakar mata kafin yake dan muzgutawa ya koma cikin kujerar ya zauna ,
Ayya ta dubi wajen Walyn dake zaune ta ce" ki tashi ki koma dakinki, ki kiyaye dukan abinda mahaifiyarki ta fada
Mikewa ta yi zurbat ta dan sosa kanta tana duban Ayya, aman batai masa gargadin kar ya mata wani abin ko ya daina fushin da yake da ita ba,
Sai dai ba halin ta kawo maganar domin ko a fuskar Ayyan bata ga fuska ba,
Dan haka ta samu ta raba Ayya ta fice da sauri ta shiga motarta ta nufi gidanta.
Tana fita Ayya ta maido hankalinta wajensa tana dubansa, ta sani sarai shirunnan da ya yi gwara ya yi magana, aman sai ta share, idan tana son tankwasa shi bata nuna wani tausayi ko tsoron zuciya,
Rai ta hade ta ce" an yi maka laifi mai girma, ka yi hakuri , kar ka ci gaba da nuna mata wani abin, ka kwontar da hankalinka, dukan tsanani yana tare da sauki.
Idannuwansa ya lumshe ya kai dubansa wajen matatakalar Ayya, kansa ya juyo yana duban Ayya ya ce" alfarma faya nake nema a wajenki Ayyana,
Ayya dake dubansa ta ce" wace alfarma ce?
Idan na tashi neman aure , ina so tsakanina da ke ki sanya mani albarka, ba ruwanki da maganar wani al.adu da me za.a dube ki, Ayya bafa adini bane, dan na taka ba Allah zai kama ni ba, ba kuma wani zqi hana mini ci ko sha ba, ba wanda zai hana ni shiga inda nake so, hasalima koda za.a yi da ni sai dai a yi a boye, ki toshe kunnayenki na roke ki!
Ayya ido kawai ta zuba masa, zata fi kowa murnar gannin wardugunta ya samu wani canji bangaren mata,
Ya kasance mai farin jinnin mata, suna likun masa a duk inda ya saka kafarsa, sai dai abin takaicin cikin matan nan wa.inda ya samu wani kusanci da su du sun saka ya ji dan damanma, har yanaiwa mata kallon zuma daga nesa, idan suka karaso gareka sun zama madaci,
Me ya rasa? Ya kasance namiji har namiji sai dai ya rasa macen mutunci,