Sashe 21
Auren Sirri Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Byn ta tura sakon ne ta goge "sannan takoma ta kwanta lamo tana jin yadda kirjinta ke tsarkewa ,ahankali ta lumshe" idanunta ,xuciyarta ke beating tare da yi mata fadar abinda ta aikata .
ita kanta tasan tayi babban kuskure sosai wajen tura masa text ,dan tasha jin yadda yake yawan yi complain akan tura masa sako ko kiran wayarsa yayinda yake kan aiki ,
Sai dashi duk lokacin daya gadama zai kiraka idan km baka dauka ba yazama matsala .
dan haka tayi shr kawai tana fidda numfashi sama sama .
Tsawon lokaci tana kwance "tana tunanin abinda zai biyo baya idan yaga sakonta , addu'a take Allah yasa ba karawa kanta laifi tayi ba agurinsa .
take tsoro da fargaba suka taru suka dira mata " alokaci daya.
Idanunta a lumshe har lokacin tana saka da warwara deeni dan ra'ayi baka masa dole ballanantana ta tursashi .
can taji alamun shigowar sako a zaburi ta mike" ta rarumi wayar jikinta har rawa yake .
idanunta ne suka ci karo da reply dinsa .
hankalinta a tashe tasoma karanta text din .
Ke ... Banida lokacin karanta wannan shirmen naki na baza , aikina yana da mahimmanci a wajena banida lokacin hada aikina da zantuttukan marasa ma'ana dan haka ki kiyaye gaba ..
Tana gama karantawa ta sauke ajiyar zuciya sannan ta sulale takoma ta kwanta tare da lumshe idanunta.
Tabbas tasan ta daukarwa kanta abinda yafi karfinta .
tayi shr ,tana son tayi nazari akan kalamansa tasan dai yakaranta sakonta sarai .
tsabar rainin wayo ne da miskilanci irin nasa .
yasa ya nuna kmr bai da lokacinta .
tayi juyi tana mai tausayawa kanta na nacewa auren DEENi.
yanzu Gabadaya son aurensa ya sire mata ya fita akanta.
, tsoro aurensa take km sai yanzu maganganun Ummi ke sake shigarta .
Inda tace zeenat ,kin fahimtata ne kawai deeni dana ne dana haifa a cikina.
baki fini sonshi ba sanin halin miskilancinsa da girman kai irin nasa yasa kikaga naki amincewa da aurenku wahala kawai zakisha a hannushi .
, gara yaje waje can ya nemo matarsa.
batayi aune ba taji saukar hawaye nabin kuncinta" bata hana su zubowa ba ,domin ita kanta zata fi so ta zubar dasu ,kodan samun natsuwarta.
Km ko ba komai hakan zaisa taji sanyi da ragewa kanta radadin abinda ke nukurkusan ruhinta.
Jikinta yayi matukar yin tsanyi ahankali tasoma sambatu ..
Wayo Allahna... ni zeenat yaya zanyi da zuciyata data ta makance akan kaunarka.
Ina sonka yaya deeni har bansan yadda zan misalta tarin soyayyata gareka ba.
kaunarka ajinina da ruhina yake .
daita Allah ya hallice . bazan iya daina sonka ba muddin rai .
koda baka sona ni Ina sonka km zan iya jurar komai akanka ,raba zuciyata da soyayyarka tamkar rasa numfashina ne .
Haka tayi surutai har sanda Tajiyo motsen shigowar Ummi .
tayi shr tare da saurin juya mata baya.
tana cigaba kukanta, kasa kasa batare Ummi ta Gane halin da take ciki ba .
Zuciyarta ke mata wani irin ciwo da radadi mai zafi .
Washegari ma sukusuku ta tashi tamkar wace batada lfy ta rame sosai " idanunta a kumbure kallo daya Ummi tayi mata ,ta Gane kuka tayi .
km daman tana lura daita jiya bawani baccin kirki tayi ba .
taji wani irin tausayinta ya tsarga mata har cikin zuciyarta "dan tasan tunda ta kwallafawa ranta auren DEENi , ta hadu da babban aiki .
km sai ta hadu da abinda yafi haka.a addu'a dai zata cigaba dayi musu Allah ya kauda fitana atsakaninsu.
Ahankali Ummi takira sunanta ...ta dago da kumburarun idanunta tana kallon Ummi dasu batare da tace mata komai ba byn gaisuwar datayi mata .
,Ummi tace meke damunki ne zeenat naga duk idanunki duk sun kunbura" sai naga ma kmr kuka kikayi .
Zeenat ta danyi murmushi dole sannan tace kai Ummi bbu komai fa, idanuna kemin ciwo ,km jiya da ciwon kai na kwana .
ta fadi hakan da hankalin Ummi ya kwanta .
Ummi tayi shr kusan minti goma tana kallonta sai da tagama nazarinta tsab sannan ta numfasa tace shikennan Allah ya sawake kinsha magani ?
Zeenat ta girgiza kai kawai.
Ummi tace maza ki tashi kije daki ki dauko magani kisha.
a sanyaye ta mike jikinta babu kwari tace to ...
tare da shigewa kitchen dan bataji zata iya shan wani magani a halin datake ciki yanzu ,dan tasan ko tasha bazai taba yi mata maganin damuwarta.
kusan duk dare sai bacci ya katse mata sakamakon tunanin DEENI da hali ko in kula da yake nuna mata .
, shi sam mutun ne da babu ruwanshi da wani damuwa harakar gabansa kawai yakeyi hankalinsa kwance .
tayi shr cikin zullumi irin zaman da zatayi da DEENi,a zahirin ce tagama duk wani tunani da zatayi akansa ,amman sam bata hango wani jin dadi ko kulawa da za samu aurenta dashi ba .
Sai yanzun take gane manufar Ummi" tana guje mata wahala ne yayinda ita km ta kasa fahimtar hska . gashi yanzu lokaci ya kure mata bata da daman tace ta fasa .
Misalin karfe takwas na dare .
kwance take a parlour kan doguwar kujerar three site .
hannuta rike da wayar Ummi ta juyata idanunta kuru akan TV .zaka dauka ko kallo take .
amman a hakikanin gaskiya kallo daya zaka mata ka gane Gabadaya hankali bai gurin TV .
tana can ta lula cikin duniyar tunani tunani .
, kamshin turarensa ne ya ankarar daita ,take tayi firgigib da dawo duniyar kasa dan tasan tunda Tajiyo kamshinsa yana kusa kennan dan haka ahankali ta dan juyo tsaitin datake jiyo kamshin nasa , ahankali idanunta suka cin karo da kyakkyawan fuskarsa ko kallonta inda take baiyi ba , yakarasa shigowa parlour fuskar nan tashi a daure tamkar zaki .
,take taji zuciyarta ta tsinke tasoma rawa wata irin zazzafar kaunarshi ce ta dinga taso mata tamkar ta tarwatsa mata zuciya , lokacin data daura idanunta kansa.
kamshin turarensa ya addabi hancinta ji take kmr tajita a kusa dashi .
sallama Yayi aciki.
ta amsa tare da sunkuyar da kanta kasa har ya wuceta yasoma taka step bata dago da kanta ba, sai da tabbatar da tadaina jin motsen takunsa" sannan ta dago tana sauke ajiyar zuciya tare dafe kirjinta tace wayoooo Allah kirjina .
dan ita kadai tasan yadda ta dinga ji .
can taji sautin shigowar sako a wayar Ummi " ,sharewa tayi tunaninta ko yan network ne.
Dan haka ta maida hankalinta kan shirin da'ake gabatarwa a TV.
minti biyar tsakani taji wayar ta dauki kara ta dauki wayar tana dubawa .
Wata bakuwar number tagani" yana yawo akan screen din .
Dan haka ta manna wayar a kunneta tare yin sallama .
muryar da tafi so da tsoro ne "ta daki dodon kunneta hakan yasa jikinta ya sake daukar rawa gabanta yashiga faduwa da sauri .
,yace ke dan iskanci da rainin wayo bakiga sako na bane ?
Muryarta A sanyaye tace ban gani ba Amman kayi hakuri dan Allah tsaki yaja tare da kashe wayarsa .
Da sauri tashiga in box din tasoma duba sakon
Kisame ni a dakina yanzu " abinda tagani kennan .
,take gabanta yacigaba da faduwa , duk da tana cikin fargaba hakan bai hanata ,mutunta kanta
da son janyowa kanta martabarta ta Diya mace .
Sai da ta dauki mintina tukun ta mike cikin sanyin jiki ta nufi dakin shi .
tsaye take akan kafafunta a bakin kofar dakinsa zuciyarta na dokawa .
tsoro taji yana shigarta sai ta daura hannuta kan handle din kofar .
sai tacire hannuta da sauri .
,da kyar tasamu tattaro duk wani kuzarin dake jikinta .
,karfin hali tayi wanje murda handle din kofar da iya karfinta tashiga parlour'n da sallamarta .
shr parlour bakajin komai sai karar TV tsayawa tayi tana jirashi kusan 5 minti bata ga alamunsa ba ko jin motsensa batayi ba . dan haka ta yanke shawarar shiga Bedroom dinsa.
tana shiga dakin gabanta ya tsananta faduwa , cikin sanyin murya ta sake yin sallama .ya amsa da kyar km a ciki .
Zaune taganshi yana operating system sanye cikon wando three counter da pure whit singlet , ahankali take takowa har inda yake yayinda kanta ke sunkuye .
tsugunnawa tayi a gabansa muryata na rawa tace Gani Yaya .
GA TSARABARKU TA KANO BA YAWA KUYI MANAGE 😃😃😃
MMN SUDAIS CE
💗💗💗💗💗
AUREN SIRRI
💖💖💖
💗💗💗💗💗
AYSHA A BAGUDO
Page 25- 26
Bai ko kalli inda take ba hasali ma operating din system dinsa yacigaba dayi.
" tayi kusan minti goma tsugunne a gabansa batare daya dago idanunshi ya kalleta ba .
Shr Tayi tare da" sunkuyar da kanta kasa .
Yayinda zuciyarta ke tsananta bugawa .
cikin daddaden muryarsa may cike da dadin sauraro "fiyye da komai datafi kauna .
Yace tun yaushe kike tare da wance sakaran Dana ganku shekaranjiya ?
Batasan sanda ta zauna ba ,dan tsabar frigice da tsoron daya shigeta na lokaci guda .
,zuciyarta ce tasoma rawa...rawa tare dokawa .tarasa yadda me za tace.
cikin ya'n sakanni nan hankalinta yayi matukar mugun tashi. kwakwaluwarta "tashiga tariyo mata abinda ya faru a shekaranjiya din .
gabadaya tagama
frigita da tmbyr daya jiho mata, tunaninta ya ta'alaka ne akan ya manta da abinda yagani din .
dan ganin ya share Bai nuna koda a fuskarsa ba .
da kyar ta iya bude bakita tare da son nuna masa , itama batasan inda zancesa ya nufa ba.
, muryarta cike da rudani tace wa kenan ?
Sai Lokacin ne ya dago rikitattun idanunshi ya dubeta dasu .
,tare da zabgamata wata uwar harara .
cikin sanyayyayiyar muryarsa, ta isa ya sake yin magana Yace wawa ..... .ni zaki waskewa ya nuna kirjinsa da yatsansa
bakaramin laifi zaki karawa kanki wajen nuna min bakisan abinda nake nufi ba .
Domin bana bukatar
rainin hankali ko karyata min abinda idanuna suka gane me .
Amsa tmbyta kawai nake da bukata .
ita kanta tasan tayi babban kuskure sosai wajen tura masa text ,dan tasha jin yadda yake yawan yi complain akan tura masa sako ko kiran wayarsa yayinda yake kan aiki ,
Sai dashi duk lokacin daya gadama zai kiraka idan km baka dauka ba yazama matsala .
dan haka tayi shr kawai tana fidda numfashi sama sama .
Tsawon lokaci tana kwance "tana tunanin abinda zai biyo baya idan yaga sakonta , addu'a take Allah yasa ba karawa kanta laifi tayi ba agurinsa .
take tsoro da fargaba suka taru suka dira mata " alokaci daya.
Idanunta a lumshe har lokacin tana saka da warwara deeni dan ra'ayi baka masa dole ballanantana ta tursashi .
can taji alamun shigowar sako a zaburi ta mike" ta rarumi wayar jikinta har rawa yake .
idanunta ne suka ci karo da reply dinsa .
hankalinta a tashe tasoma karanta text din .
Ke ... Banida lokacin karanta wannan shirmen naki na baza , aikina yana da mahimmanci a wajena banida lokacin hada aikina da zantuttukan marasa ma'ana dan haka ki kiyaye gaba ..
Tana gama karantawa ta sauke ajiyar zuciya sannan ta sulale takoma ta kwanta tare da lumshe idanunta.
Tabbas tasan ta daukarwa kanta abinda yafi karfinta .
tayi shr ,tana son tayi nazari akan kalamansa tasan dai yakaranta sakonta sarai .
tsabar rainin wayo ne da miskilanci irin nasa .
yasa ya nuna kmr bai da lokacinta .
tayi juyi tana mai tausayawa kanta na nacewa auren DEENi.
yanzu Gabadaya son aurensa ya sire mata ya fita akanta.
, tsoro aurensa take km sai yanzu maganganun Ummi ke sake shigarta .
Inda tace zeenat ,kin fahimtata ne kawai deeni dana ne dana haifa a cikina.
baki fini sonshi ba sanin halin miskilancinsa da girman kai irin nasa yasa kikaga naki amincewa da aurenku wahala kawai zakisha a hannushi .
, gara yaje waje can ya nemo matarsa.
batayi aune ba taji saukar hawaye nabin kuncinta" bata hana su zubowa ba ,domin ita kanta zata fi so ta zubar dasu ,kodan samun natsuwarta.
Km ko ba komai hakan zaisa taji sanyi da ragewa kanta radadin abinda ke nukurkusan ruhinta.
Jikinta yayi matukar yin tsanyi ahankali tasoma sambatu ..
Wayo Allahna... ni zeenat yaya zanyi da zuciyata data ta makance akan kaunarka.
Ina sonka yaya deeni har bansan yadda zan misalta tarin soyayyata gareka ba.
kaunarka ajinina da ruhina yake .
daita Allah ya hallice . bazan iya daina sonka ba muddin rai .
koda baka sona ni Ina sonka km zan iya jurar komai akanka ,raba zuciyata da soyayyarka tamkar rasa numfashina ne .
Haka tayi surutai har sanda Tajiyo motsen shigowar Ummi .
tayi shr tare da saurin juya mata baya.
tana cigaba kukanta, kasa kasa batare Ummi ta Gane halin da take ciki ba .
Zuciyarta ke mata wani irin ciwo da radadi mai zafi .
Washegari ma sukusuku ta tashi tamkar wace batada lfy ta rame sosai " idanunta a kumbure kallo daya Ummi tayi mata ,ta Gane kuka tayi .
km daman tana lura daita jiya bawani baccin kirki tayi ba .
taji wani irin tausayinta ya tsarga mata har cikin zuciyarta "dan tasan tunda ta kwallafawa ranta auren DEENi , ta hadu da babban aiki .
km sai ta hadu da abinda yafi haka.a addu'a dai zata cigaba dayi musu Allah ya kauda fitana atsakaninsu.
Ahankali Ummi takira sunanta ...ta dago da kumburarun idanunta tana kallon Ummi dasu batare da tace mata komai ba byn gaisuwar datayi mata .
,Ummi tace meke damunki ne zeenat naga duk idanunki duk sun kunbura" sai naga ma kmr kuka kikayi .
Zeenat ta danyi murmushi dole sannan tace kai Ummi bbu komai fa, idanuna kemin ciwo ,km jiya da ciwon kai na kwana .
ta fadi hakan da hankalin Ummi ya kwanta .
Ummi tayi shr kusan minti goma tana kallonta sai da tagama nazarinta tsab sannan ta numfasa tace shikennan Allah ya sawake kinsha magani ?
Zeenat ta girgiza kai kawai.
Ummi tace maza ki tashi kije daki ki dauko magani kisha.
a sanyaye ta mike jikinta babu kwari tace to ...
tare da shigewa kitchen dan bataji zata iya shan wani magani a halin datake ciki yanzu ,dan tasan ko tasha bazai taba yi mata maganin damuwarta.
kusan duk dare sai bacci ya katse mata sakamakon tunanin DEENI da hali ko in kula da yake nuna mata .
, shi sam mutun ne da babu ruwanshi da wani damuwa harakar gabansa kawai yakeyi hankalinsa kwance .
tayi shr cikin zullumi irin zaman da zatayi da DEENi,a zahirin ce tagama duk wani tunani da zatayi akansa ,amman sam bata hango wani jin dadi ko kulawa da za samu aurenta dashi ba .
Sai yanzun take gane manufar Ummi" tana guje mata wahala ne yayinda ita km ta kasa fahimtar hska . gashi yanzu lokaci ya kure mata bata da daman tace ta fasa .
Misalin karfe takwas na dare .
kwance take a parlour kan doguwar kujerar three site .
hannuta rike da wayar Ummi ta juyata idanunta kuru akan TV .zaka dauka ko kallo take .
amman a hakikanin gaskiya kallo daya zaka mata ka gane Gabadaya hankali bai gurin TV .
tana can ta lula cikin duniyar tunani tunani .
, kamshin turarensa ne ya ankarar daita ,take tayi firgigib da dawo duniyar kasa dan tasan tunda Tajiyo kamshinsa yana kusa kennan dan haka ahankali ta dan juyo tsaitin datake jiyo kamshin nasa , ahankali idanunta suka cin karo da kyakkyawan fuskarsa ko kallonta inda take baiyi ba , yakarasa shigowa parlour fuskar nan tashi a daure tamkar zaki .
,take taji zuciyarta ta tsinke tasoma rawa wata irin zazzafar kaunarshi ce ta dinga taso mata tamkar ta tarwatsa mata zuciya , lokacin data daura idanunta kansa.
kamshin turarensa ya addabi hancinta ji take kmr tajita a kusa dashi .
sallama Yayi aciki.
ta amsa tare da sunkuyar da kanta kasa har ya wuceta yasoma taka step bata dago da kanta ba, sai da tabbatar da tadaina jin motsen takunsa" sannan ta dago tana sauke ajiyar zuciya tare dafe kirjinta tace wayoooo Allah kirjina .
dan ita kadai tasan yadda ta dinga ji .
can taji sautin shigowar sako a wayar Ummi " ,sharewa tayi tunaninta ko yan network ne.
Dan haka ta maida hankalinta kan shirin da'ake gabatarwa a TV.
minti biyar tsakani taji wayar ta dauki kara ta dauki wayar tana dubawa .
Wata bakuwar number tagani" yana yawo akan screen din .
Dan haka ta manna wayar a kunneta tare yin sallama .
muryar da tafi so da tsoro ne "ta daki dodon kunneta hakan yasa jikinta ya sake daukar rawa gabanta yashiga faduwa da sauri .
,yace ke dan iskanci da rainin wayo bakiga sako na bane ?
Muryarta A sanyaye tace ban gani ba Amman kayi hakuri dan Allah tsaki yaja tare da kashe wayarsa .
Da sauri tashiga in box din tasoma duba sakon
Kisame ni a dakina yanzu " abinda tagani kennan .
,take gabanta yacigaba da faduwa , duk da tana cikin fargaba hakan bai hanata ,mutunta kanta
da son janyowa kanta martabarta ta Diya mace .
Sai da ta dauki mintina tukun ta mike cikin sanyin jiki ta nufi dakin shi .
tsaye take akan kafafunta a bakin kofar dakinsa zuciyarta na dokawa .
tsoro taji yana shigarta sai ta daura hannuta kan handle din kofar .
sai tacire hannuta da sauri .
,da kyar tasamu tattaro duk wani kuzarin dake jikinta .
,karfin hali tayi wanje murda handle din kofar da iya karfinta tashiga parlour'n da sallamarta .
shr parlour bakajin komai sai karar TV tsayawa tayi tana jirashi kusan 5 minti bata ga alamunsa ba ko jin motsensa batayi ba . dan haka ta yanke shawarar shiga Bedroom dinsa.
tana shiga dakin gabanta ya tsananta faduwa , cikin sanyin murya ta sake yin sallama .ya amsa da kyar km a ciki .
Zaune taganshi yana operating system sanye cikon wando three counter da pure whit singlet , ahankali take takowa har inda yake yayinda kanta ke sunkuye .
tsugunnawa tayi a gabansa muryata na rawa tace Gani Yaya .
GA TSARABARKU TA KANO BA YAWA KUYI MANAGE 😃😃😃
MMN SUDAIS CE
💗💗💗💗💗
AUREN SIRRI
💖💖💖
💗💗💗💗💗
AYSHA A BAGUDO
Page 25- 26
Bai ko kalli inda take ba hasali ma operating din system dinsa yacigaba dayi.
" tayi kusan minti goma tsugunne a gabansa batare daya dago idanunshi ya kalleta ba .
Shr Tayi tare da" sunkuyar da kanta kasa .
Yayinda zuciyarta ke tsananta bugawa .
cikin daddaden muryarsa may cike da dadin sauraro "fiyye da komai datafi kauna .
Yace tun yaushe kike tare da wance sakaran Dana ganku shekaranjiya ?
Batasan sanda ta zauna ba ,dan tsabar frigice da tsoron daya shigeta na lokaci guda .
,zuciyarta ce tasoma rawa...rawa tare dokawa .tarasa yadda me za tace.
cikin ya'n sakanni nan hankalinta yayi matukar mugun tashi. kwakwaluwarta "tashiga tariyo mata abinda ya faru a shekaranjiya din .
gabadaya tagama
frigita da tmbyr daya jiho mata, tunaninta ya ta'alaka ne akan ya manta da abinda yagani din .
dan ganin ya share Bai nuna koda a fuskarsa ba .
da kyar ta iya bude bakita tare da son nuna masa , itama batasan inda zancesa ya nufa ba.
, muryarta cike da rudani tace wa kenan ?
Sai Lokacin ne ya dago rikitattun idanunshi ya dubeta dasu .
,tare da zabgamata wata uwar harara .
cikin sanyayyayiyar muryarsa, ta isa ya sake yin magana Yace wawa ..... .ni zaki waskewa ya nuna kirjinsa da yatsansa
bakaramin laifi zaki karawa kanki wajen nuna min bakisan abinda nake nufi ba .
Domin bana bukatar
rainin hankali ko karyata min abinda idanuna suka gane me .
Amsa tmbyta kawai nake da bukata .