← Book details Zanyi Biyayya Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 44 OF 60

Sashe 44

Zanyi Biyayya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Zankoci mutuncin shi inya wulakanta min ya wallahi, inji RAHAMA don haka zan bashi mugun gargadi akan Y'ar nan kafin ma a daura, "toh Adai fara tanbayar ubanta muji sai ka kira su Husna da Aliyu ku tsara Abinku nidai ina gefe, tafada cikeda farin ciki ranta yagani har ana zancen Auren jikanta,........ 🖊

*Matar Soja*
2/28/21, 6:17 PM - Q: 🌻🌻
*ZANYI BIYAYYA*
🌻🌻

*By FENERH*

6⃣3⃣&6⃣4⃣

A kwance yake akan wani tafkeken gado yana faman juyi shikadai domin tunjiya yakasa bacci, hannu yasa yana dafe kasan shi tareda jan numfashi na wuya, ko runtsawa baiyi ba tsabar wahala a daren jiya, don haka wayar shi ya janyo yana nishi dakyar, bugun farko ta daga, saida ya gyara murya yace "grandma kinfadawa Dady? Banji me take fada ba yace "gakiya suyi sauri nidai su min Aure kafin in mutu wallahi nakasa bacci tunjiya marata ciwo takeyi grandma, yafada yana nishi, "kuma ni banason Y'ar jami'a budurwa nakeso wallahi wadda zanbude da kaina,

Datse call din yayi jin ya kunna kakar tashi tafara ruwan fada, yace "Allah ya barmin ke grandma, dakyar ya mike ko iya tsayawa straight baiyi saboda yanda yakejin ciwon marar tashi,
Wanka yayi tareda shiryawa cikin native wear ya fito yana baza kamshi da Annuri fadin haduwar wannan gayen ba a magana domin ya gaji kyau ta koina,

Motar shi ya fada ya nufi hanyar gidan su daga quarters din da yake nasu na ma'aikata yana tafe yana tunanin yanda zai hada ido da momyn shi, don yasan ba wani iya sakewa takeyi a tareda shiba saboda kunyar ta, tundaga gate masu gadi suka fara miko gaisuwa, hannu yake daga musu kawai har yayi parking ya sauka, masu aikin gidan ta ko ina suna harkar su,
Katon falon ya shiga wanda ya samu momyn shi da dadyn a zaune, gab da juna daga gani hira suke mai dad'i kamar koda yaushe, rayuwar iyayen nashi na matukar burgeshi, tun tasowsr shi bai tabaji ko ganin fadan su ba he pray Allah yasa shima yasamu Abokiyar zama mai hakuri irin momyn shi,

Yanayin Sallama suka d'an gyara zama, ya dukar da kanshi har zuwa gaban su, "good morning Dady, momy good morning, yafada a jere, "how are you? Baban ya Amsa tareda zuba mai ido " naji sakon ka wurin momy na, me yasa kakeson damun matar nan ne kai, wato bazaka iya zuwa kai tsaye kafada min ba ko? good kaje ka shirya mungama magana end month za a daura maka Aure da meenal,
Wani irin zabura yayi ya kalli dadyn nashi, "Dady wace meenal din? " Amina Y'ar uwar ka, "please Dady bana sonta she is my mate fa haba, ina ma laifin Aisha ko kanwar ta but meenal da tare ma muka gama school nidai Dady nama fasa Auren,

"Saboda kafita daraja ko me kake nufi,? Inji momyn nashi, "toh kafita idona in rufe tunda ka iya bude baki kace Aure to Angama get ready yanda dadyn ku yace haka za ayi, kuma wallahi zamu hadu dakai inka wulakanta min ya'
Katashi ka wuce, tafada tana mikewa, tabar musu falon, dukar da kanshi yayi domin bayason fushin momy sam ita bata mai sauki Amma Dady yana lallashin shi domin Allah ya dora mai son shi sosai,

Lallashin shi yafarayi tareda fada mai yayi BIYAYYA zaiyi farin ciki, Auren biyayya nada riba Abubakar zakayi farin ciki insha Allahu kaji, ya aikin naku? "Alhmdulillah yafada ciki ciki, Allah yasani he is not happy at all duk da Auren yakeso shi baya son saura gaskiya budurwa yakeso shi wannan yarinyar ma baisan ya takeba don bai taba tsayawa ya kalleta na minti biyu ba a fisge yake ganin ta ya wuce,
Wallahi da yasan ita za ace za abashi da ya hakura da zancen Auren saidai sha'awa ta kashe shi da dai ya Auri macen da har ta kammala degree,

Shifa yana son Auren under age ka more sadakin ka yanda kakeso Amma ka Auri Y'ar jami'a ai kai zata more,
Mikewa yayi ya nufi dakin shi dake cikin gidan tareda fadawa mai aiki takawo mai breakfast, dakin shi ya tafi fadawa yayi kan kujera ya rufe ido yana ya mutsa sumar kanshi, "I don't want her yafada can kasan makoshi,
Har saida mai aikin ta yi Sallama ta shigo tareda ajiye mai Abincin ta juya, ya gyara zama ya fara taimakawa kanshi,

Karfe goma na safe ta iso gidan na momy RAHAMA, tun shigowar ta ta hango motar shi wani irin farin ciki taji ya mugun rufeta, zata ganshi a arha yau bayan ta kwana tunanin shi, bata taba tunanin ganin shi a gidan ba tasan yafi rayuwa a gidan grandma shiyasa tanason zuwa gidan duk da zata iya zuwa sau goma bata ganshi ba,
Cikin natsuwar ta ta isa cikin gidan tanajin kamar anyaye mata duk wata damuwa da ta kwana da ita domin jiya sam bata iya runtsawa ba saboda tunanin in har anhada ta Aure da wani to akwai babbar matsala kuwa a rayuwar ta, domin soyayyar sadiq tayi mata karan tsaye a zuciyar ta,

Dakin su Aisha ta nufa wanda ta samesu suna maida bacci, ta buga kafaafun su "ku har yanzu gari bai waye muku ba?
" dakyar suka iya bude idanun su " Aunty meenal yau ba school to bari mu huta kawai ni har na tashi zan fita naji shigowar dodo gidan mu dole na hakura nadawo inji Fatima ,

"Ai ni ina jin kamshin Arnen turaren shi nace wahayi ya sauka, Amma kunsan ni da son jin gulma, naji ana zancen wai Aure yakeso kiji d'an rainin wayau shida bai kallon mata, wace macen cema zata yarda ta Aure shi,
Wani irin faduwar gaba Meenal taji tayi saurin mikewa " ina momy? Tace musu, "inaga takoma dakinta kije kigani nidai yau ina daki sai ya sadiq yabar gidan nan, tafada tana koma kwanciya,

Fita meenal tayi cikin wani irin tashin hankali "Aure yakeso that' means yanada wadda yakeso kenan, wani irin tukukin kishi da bakin ciki ya rufe mata zuciya, Wallahi batason taga ko wata mace ya Kalla bare zancen Aure bazata iya jurewa ba gaskiya zuciyar ta zata buga,

Jin muryar momy yasa ta shiga taitayin ta, " Amina kinzo? "Eh momy ina kwana tafada tana saita tunanin ta, "lafiya kalau zo muje daga ciki, bin bayan ta tayi har cikin part din ta, a falon ta suka zauna, "bakya bukatar komai? kije ki nemi Abun motsa baki a kitchen, "na Koshi sai zuwa Anjima tafada tana dukar dakai,

"Amina kinsan me yasa nakiraki? Girgiza kai tayi, " ok inaso inbaki wani misali ne sannan ke ki yankewa kanki hukunci da karan kanki idan kinso zaki yi farin ciki nan gaba idan kin bijire zaki yi kuka da kanki, wanda shine banaso,
Kintaba sanin cewa dadyn su Aisha shine aka fara zabawa Yaya HAJARA ta bijire?
Dago kanta tayi ta kalli RAHAMA a natse take fada mata yanda maman ta ta bijire daga baya tadawo tana data sani saboda zugar kawa, datakai ta tabaro,
Banyi niyayyar fada miki ba Amma yaya tasa infada miki komai domin karkuyi kuskure irin nata,

Na Auri dadyn su Aisha lokacin batareda inaso ba Amma BIYAYYA da kuma son rufawa iyayen mu asiri yakawoni wannan matsayin wanda nasan idan kikayi BIYAYYA kema wata rana zaki fimu farin ciki, don haka yanzu kiyiwa kanki duk hukuncin da kikaga shine dai dai,

Wasu irin hawaye masu zafi suka zubo mata ta share tareda dago kanta ta kalli RAHAMA " momy I promise you nima zanyi biyayya insha Allahu domin insamu dacewa duniya da lahira koda yau su baba sunbani miji zan karba bazanso inyi kuskuren da mama tayi ba, koda kuwa Auren zai zamo Ajalina, tafada tana faahewa da wani irin kuka,

Tuni RAHAMA taji tausayin ta ya rufeta ba Abinda ta tuna sai lokacin da aka ce ta Auri Al Ameen, Allah kadai yasan irin Abinda ta hadiya ita kadai sai d'an Uwan ta da ya kwantar mata da hankali,
Allah sarki yaya Aliyu, tafada tana tuna baya, yau gasu sanadin ta, duka suna farin ciki, rungume Meenal tayi cikeda rarrashi tace "ya isa ko insha Allahu zakiyi farin ciki like me wata rana,

Daga kai tayi Kawai ta mike tace momy nagode sosai, ta fita tana tunanin da badan komai a rubuce yake ba datace maman ta tayiwa kanta sosai domin ita kanta tana mugun sha'awar rayuwar gidan momyn rayuwa ce data ginu a kan tsari na Addini da tsantsar tarbiya ga daula kuma wadda suma suna lasawa,

Zatayi iya kokarin ta taga ta zare soyayyar sadiq a ranta kodan ta tsira da mutuncin ta domin tasan bazai taba sontaba, Amma kuma tayaya zata iya cire son da batasan lokacin da ya shigeta ba,
Dakin kannen nata ta koma ta samu sun tashi yanzu har suna gyara dakin nasu,
Tace "ina brother DJ? Wato kamar yanda nafada yaran RAHAMA su hudu ne a yanzu Sadiq da kanin shi Auwal sai Aisha da Fatima, wadda itace karamar duk da kusan kansu daya kamar Y'an biyu saboda bawani tazara a tsakanin su duka ya'yan nata kaida kai ta haifesu,

"Ai yaya Auwal na gidan Auncle Aliyu kinsan harkar su tafi tafiya shida sa an shi abokin burmin shi, yaya nasir, d'an murmushi tayi kadan tasan bazasu taba rabuwa ba koda yaushe suna tare bama ka gane ba uwa daya sukeba saboda kamar jini da sukeda, kamar ba kannen taba saboda maza yanzu suke saurin girma,

Wayar ta taciro ta kira number nasir domin tanaso ya maida ita gida don napep ta biyo, a kwance suke a dakin nashi suna hira, " wallahi dude da badon yaya Sadiq da ya min karan tsaye ba ko tsab zan iya fitowa infada wa momy ni inason meenal yarinyar taji kaya malam,
Wani irin mugun kallo Auwal ya watsa mai "amma bakada kunya wallahi inazaka kai ta yayar kace fa? "To sai me niba namiji bane ai ina fada maka tunda ya sadiq baiyi Aureba muma bamu isa mufito mufada ba Amma yau dazaiyi Aure wallahi ballo ruwa zanyi abani ita in more, kai dude mace cefa har da Rabi infada maka,
Chapter 44 · 0% Book details