← Book details Zanyi Biyayya Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 34 OF 60

Sashe 34

Zanyi Biyayya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Husna ma a ranar aka dangana ta da gidan ta, taro dai Alhmdulillah saidai muyi musu fatan Alkhairi,
RAHAMA taso taje gidan su domin raka Y'ar uwar ta Amma jikinta ya hanata, haka ta kwanta a dakin Husna da yazama empty yanzu wanda sunyi kukan rabuwa duk da gidan su dai zata koma Amma dai ance sabo turken wawa,

Hajara kuwa tundaga kofar gidan nasu bala jikin ta yayi sanyi gidan ko plasta babu, a haka aka d'an gana da ita da sasan su da dakuna uku ke ciki na maman shi da kuma kishiyar ta sai kuma nasu dake gefe,

Baba yayi matukar kokari wajen gyara mata dakinta kamar ko wace Y'ar gata wanda tayi matukar mamakin hakan domin taji gargadin shi sosai musamman da taje musu bankwana fadan shi ya kara da kakkausar murya, akan ko yaji tayi bazai yafe mata ba,

Kuka kuwa tayi har taba uku lada, gashi batada kwakkwaran kawa yanzu Ladidi ko labarin ta bataji yanzu, wanda take godiya ga Allah da ya sa ma tafita a rayuwar ta domin ita din jaraba ce a rayuwar ta,

Tunda aka kawota taga yanda ake tururuwar shigowa dakin nata yara da manya, ta saki baki tana tunanin ko mutanen Unguwar ne kab nan kuwa d'an gin mijin ta ne, karfe goma da Rabi ango ya shigo tareda Abokan shi yana rawar kafa tareda washe baki,
Sukayi surutan su na al ada suka fita, rakasu yayi ya dawo tareda zubawa jikinta ido ganin ta cikin wani irin daddatse tsen less da RAHAMA ta dinka mata da kuma gyale mai kyau tana tashin kamshi ga hannayen ta sunsha Lalle ya yi kabbara kamar zai kira sallah

"Allahu Akbar farar mace Alkyabbar mata hajaru uwar gidan bello kuma Amarya, kai ni nagama sa'a yafada tareda janyo ledar balangun shi mai zafi da madarar peak, ya ce toh ki bude gyalen ingane ki, ga kuma madarat gwangwani saboda ke na sayo ta,

Saida ya sa hannu ya cire gyalen yana kan kabbara tareda cewa "gaskiya hajaru kin keru Allah yasa ki haihwa min d'iya masu kyawo irin naki,
Yafada yana debo tsokar balangu tareda nufar bakin ta dashi,
Ta dan kauda kai domin akwai kunya irin ta Amare,

"Hhhhhh kai kunya kikaji to bari inci inbar miki saura, zama yayi ya ci naman shi tareda fasa mata madara da key yace "to kisha wannan ko,
Girgiza kai kawai tayi ya kafa kai saida ya Shanye tas ya ajiye gwangonin,
Yaja gyatsa,

Bin shi take da kallon mamaki har ya mike tana tunanin wane irij miji take Aure?
Batasha mamaki ba saida ya nemi hauke mata kamar ba budurwa ba, tanaji tana gani ba wani salla ko Addu a ya nemi hanya batareda ko d'an aike ba, kamar yanda Annabi Muhammad S. A. W yafada,

Taji jiki sosai tayi kuka kamar zata mutu shi kuwa baiko tausaya mata ba, kamar ya samu tuwo ranar haka ya kwana aiki, tuni tayi muguwar gajiya kuka kuwa har idanun ta sunfir fito saboda kunburi

Da Asuba dole tayi kokarin tashi ta rarrafa domin duba plask dinta data gani, ai kuwa taga ruwa mai zafi wanda aikin kishiyar maman bello ne data zuba tunda yamma,
Ta zuba a butar ta sabuwa tareda juye sauran tayi waje domin babu bayi a dakin nasu ciki da falo, wanda basuda wani girma, kayan kitchen dinta ma duk suna kwali,

Dakyar ta gano bayin tayi sauri ta tsarkake kanta tareda gasa kasan ta saida taji d'an sauki ta fito daure da Alwala
Saida ta shiga dakin ta ta fara buga gefen gadon ya tashi zaune ya zuba mata ido tareda washe baki,

"Wai har kinyi me? Wallahi hajaru ke shayar dani ruwan mamaki jiya Ashe ke ruhe kike? Dut girman ga naki ke rike mutuncin ki gaskiya ke burge ni Allah yai miki Albarka ya sa nayi miki ciki a yau,

Dauke kanta tayi domin maganar shi sam haushi take da ita Amma ita waye da zata nuna, batason ta nuna damuwa ko raina mijin da take Aure Amma ita tasani bello mukaddarin rayuwar tane, yau itace ke Auren miji irin shi? Duniya kenan

Fita yayi shima yayi wanka ya fita masallaci, da sassafe yara Duka fara afko mata daki wanda tuni ta kintsa dakinta tareda caba ado Abinta, wani yaro ya shigo mata da bredi da shayi a cup yace inji bello,....... 🖊

Wallahi dauriya nayi saboda Alkwari na d'an yi typing din nan ga wulakancin nepa I have only 50 pcnt nayi typing,
And inaso intabo rayuwar Hajara domin labarin ya faro saboda itane yakamata Y'an mata su dauki izina kodan yanda rayuwar ta tafaro don haka kuci gaba da biyoni domin jin karshen yanda rayuwar su zata sauya

*Matar Soja*
2/28/21, 6:17 PM - Q: 🌻🌻
*ZANYI BIYAYYA*
🌻🌻

*By FENERH*

*ga masu bukatar biya ku hanzarta kar Abaku labari ku biya ku karanta cikin Aminci,katin Airtel 200 zaku turo normal vip 500 kuturo katin ku ta wannan numbar 09011251444 ko ta Asusun banki na 7304736012 nafisa sani Fcmb don Allah vip Kudaina turomin kati idan kana son vip kutura min ta banki katin nayimin yawa sosai in bakuda Account kibayar a pos don Allah sucire charges dinsu a ciki, Y'an Niger 🇳🇪 masu bukatar biya ku nemi wanna number +225 48 15 39 03*

4⃣7⃣&4⃣8⃣

Haka suka cika mata daki makil wasu yaran ma butu butu, dole batada yanda zatayi ta kyale su, ta fita gidan domin tasan akwai mutane kuma ita ya kamata taje ta gaida su, tafara da dakin farko na Abokiyar zaman uwar mijin mace ce mai d'an saukin kai da kuma ganewa, ta tarbeta da "aa Amarya baki bari muzo gaisuwar? Tace bakomai ai itace karama, ta nuna mata tace kije dakin yaya kigaishe ta,
Haka ta tafi inda ta karbeta ba yabo ba fallasa tareda, fada mata duk ranar girkin ta ita zata rikayi don bai yuwuwa inada sarakkuwa ace ina aza tukunya gidan ga,
Tace toh tareda tashi ta tafi tana jimamin yanda zatayi rayuwa a cikin gidan nan,

Haka dai ta yini ganin bakin cikin gidan har lokacin da aka kawo mata gara mai din bin yawa daga Alhaji Shuaibu, domin iri daya ya musu da Husna, wanda saida mutanen Unguwar ma sukayi mamakin irin kayan da aka kawo, don lokacin da aka fara shigo da buhu huwa ma uwar bello harda fitowa tana guda, "Allah ya gwadamin rai kuma ya gwadamin, dana yayi goshi irin wagga garan arziki,

Dakin ta tasa aka tura su Duka su jarkokin mai katon katon na Maggie harma da su tali ya komai dai masha Allah, wanda ita kanta tasan daga inda, suka fito, mijin da ta yiwa kanta bakin ciki dai har gobe tana ganin Alkhairin shi, wanda duk daular nan RAHAMA ce ke moreta, saurin kawar da zuciyar ta tayi daga tunanin Abin domin sam ko a mafarki bataso ta kuma nunawa Y'ar uwar ta hassada,

Ganin wannan uwar gara yasa kowa ya san cewa mai gata ce Ita saidai kaddara da kuma tsananin rabo yasa ta shigo gidan su, don ko yanayin jikinta ya isa agane ita din Y'ar hutu ce, duk da ma ta d'an lalace,

Kadaran kadahan tuni ta rungumi Abinda tasan dole dashi zata rayu wato mijin ta wanda bata son ko shi ya furta tabar gidan shi domin furucin baba bare kuma ita da kanta ta nemi fitar, tuni tasawa kanta hakurin zama da kowa tayi BIYAYYA ta kuma kauda kai da duk wani Y'ar hayaniyar cikin gidan idan ta gama ayyukan ta ta dawo daki ta dauki wayar ta tana game ko kuma chart, itada RAHAMA,

Wadda a yanzu suke shirin dagawa India itada Al Ameen, gashi Allah ya taimake ta cikin baida wani fitinannen laulayi, saidai tashin zuciya lokaci lokaci sai kuma bacci,
Wanda yazama mata jiki da kuma kasala da ta hanata aikin da take kauna a yanzu, wanda har tsokanar ta momy keyi " RAHAMA mai ciwon aiki ta zama mai ciwon bacci,
Saidai tayi dariya, har zuwa ranarda suka daga zuwa India,
Bayan sunje sunyi wa su inna Sallama tareda leka gidan Amarya Husna wadda tace tayi fushi, tunda bataje gidan taba, ita kuwa tace tayi hakuri in har suka dawo lafiya zatazo suyi wuni saidai in yayan ki ya hana ni.
Toh sai muyi Addu ar Allah ya bawa oga Al Ameen lafiya, yasamu Abinda yake nema akoda yaushe,

Sun isa birnin na Mumbai lafiya, wanda suka sauka a masauki, cikin wani tafkeken gida da yasaba sauka akoda yaushe na wani Abokin shi ne ba indiye,
Domin Al ummar Hindu sun san darajar bako sosai, wanda ita kanta taji dadin ganin ta a cikin birnin, saida suka kwana suka huta da safe ya fadawa likitan shi ya iso,
Yaso ta bishi suje, ina bacci ya hanata dole ya tabi ya barta bayan ya manna mata kiss a cikin yace " this my baby ko zanyi maganin shi idan na samu lafiya, yafada tareda fita Abun shi ya barta,

**************
Alhmdulillah komai natafiya dai dai cikin kudurar ubangiji Al Ameen yafara samun canji a jikin shi domin sun dorashi akan gwaji daban daban kuma anyi nasara,
Wani irin feelings yakeji yanzu na tashin hankali ga dokar likita na sai ya cika sati biyu ya gama magun gunan da aka dorashi kafin a kuma gwada shi , sannan komai ya dawo dai dai,
Ita kanta ta gano ya gama samun lafiyar domin wani irin jagwal gwala take sha na fitar hankali a kwanan nan,
Domin ko cikin bacci kullum sai ya lalabe ta sai ta tashi,
Haka zai karaci kwazabar shi ba halin nutso,
Chapter 34 · 0% Book details