Sashe 43
Zanyi Biyayya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Fita tayi tareda gyara fuskar ta ta nufi dakin iyayen nata, A zaune tasamu mahaifin nata wanda ya ke sanye shima cikin shiga ta Alfarma bazakace shine Bello bakanike ba ya zama Alhaji bello yanzu Alhmdulillah rayuwar su ta inganta sanadin Alhaji Al Ameen, ba Abinda suka rasa yanzu,
Samun gefe daya tayi ga kannen ta biyu mata sai matashin namiji wanda yake karamin su a ciki, ta gaida baban ta fuskar ta akasa, " Amina, "na am ta Amsa, " me kike jira da maganar fitarda miji? Duk kannen ki sunfito da nasu nadakatar dasu saboda banaso inyi musu Aure ke kina gida,
Nasan dai ba masoya kika rasa ba meye dalilin rsshin tsaida gwani guda daya? Wani irin faduwa taji gaban ta yayi Allah yasani ita Sadiq takeso Amma tayaya zata fito ta fadawa baban ta hakan, tsawar da mama HAJARA ta buga mata tasa ta dago cikeda tsoro, " iya shege badake ake magana ba, in kina da Abin fada ki fada inbabu tashi Kibawa mutane wuri, Alhaji samu zakayi cikin yaran ku na wurin aiki maiso yazo abashi nidai bazata zauna min a gida ba in kannin ta sunyi Aure,
"Bi a hankali maman yara A lallaba ta kawai ta tsaida mutum guda cikin mane manta, " idan kabi ta yarinyar nan bazata taba fitowa da wani tace gashi ba don mugun korar wulakanci take musu bansan dalili ba, don haka idan kaji tatawa wallahi katsayar Kawai da kanka,
Kuka tasa mai karfi tareda zabura " wallahi nidai karku hadani Aure da wani ni wallahi banason kowa ni akyale ni inkuma akayi zan kashe kaina kowa ya huta, bazan taba iya zama da wani namiji ba ku kyale ni, ta fita da gudu tabar dakin,
Wani irin tukukin bakin ciki ne ya rufe mama Hajara yau Y'ar da ta Haifa ke fadar irin wa innan Kalamai a gaban ta? Lallai duniya dama anfada komai biyadin biyadin ne Inkayi sai anyi maka, a yau tasan zafin irin bijirewar ya'ya agaban iyayen su, Alkhairin Allah yakaiwa iyayen ta a duk inda suke, ita da ya shuka rashin mutunci buhu buhu Yau gashi Y'ar ta batayi irin nataba Amma taji ciwon kalaman,
Wasu irin hawayen takaici tareda nadamar rayuwar ta ta Y'an matan ci da sam bata da riba don haka dole ta takawa Y'ar ta birki don ita batada hakuri irin nasu inna,
Kallon ta Alhaji bello yayi " kibi ta a hankali Karki ce mata komai ni zan zabo mata miji karyar shegan taka takeyi kuma kutashi ku tafi, yafadawa kannen da sukayi tsit a wurin,
Abin yayi mugun damun HAJARA don haka mikewa tayi ta nufi dakin ta ta kulle tareda daukar wayar ta ta kira Y'ar uwar ta kuma Abokiyar shawarar ta a kullum mai hangen nesa,
A zaune take a ofishin ta na likita sanye cikin lab cot dinta fara kal tareda farin glashin ido, kana ganin ta zakasan tagama samun duniya saura goben ta kawai tayi fess da ita ta waye karshen aji,
Leshin dake jikinta kawai zaka Kalla Kasan matar manya ce ita,
Daukar wayar ta tayi datayi kara tasa akunne a cikin sauri tace "yaya barka da rana,
"Barka dai RAHAMA ya aiki? Alhmdulillah, yaya lafiya najiki cikin damuwa? " Hmm Y'ar kice, a anan ta fada mata komai tareda cewa " yau ta sa na tuna irin bijirewar da nayiwa su inna Allah ya gafarta musu RAHAMA Ashe haka Abin keda ciwo, wallahi yanzu haka zuciya ta har wani irin tafasa takeyi akan ta zan iya shake Y'ar nan kowa ya huta,
"Yi hakuri yaya kibita a hankali yanzu ki zaunar da ita kibata misali da rayuwar mu ita kadai ta isheta darasi, kuma nima zankirata gobe weekend inmata Nasiha insha Allahu yaya kibi komai A hankali,
"Toh tace tareda yin Ajiyar zuciya ta kashe wayar, tanajin sanyi tareda godiya da Allah yabata Y'ar uwa irin RAHAMA,
Tashi tayi ta nufi dakin yaran nata, tace kannin sufita zatayi magana da yayar su wadda ta hada kai da guiwa tana kukan bakin ciki, zama tayi gefen ta "Meenal, kina jina, dago kanki, tafada cikin taushin murya, ta dago duk fuskar ta fara tayi ja sumar dake kwance a gefen fuskar ta dake kara mata kyau duk sun jike da zufa, meenal photo copy din maman tace sai dai tafi HAJARA kira sosai don ita Allah ya hore mata dukiyar fulani da kuma hips kamar zasuyi magana wanda duk Lafiyayyan namiji zaiso mallakar mace kamar ta, ga ta fara tass kamar kataba jini ya fito,
Kallon maman ta tayi tana share hawaye tareda shashsheka, " me kike son ki zama a rayuwar ki? "Ya' tagari ko batacciya? Ayau inaso ki kalli rayuwar mu nida Y'ar uwata kafin a sameku akwai kalubale da muka fuskanta a cikin rayuwar mu, Karki cigaba da wannan halin da kika fara nunawa yau zamanin ki ba irin namu bane halin iyayen ki daban da nawa kije kitanbayi momyn ku irin Abin da nayi a baya wanda banci ribar shi ba don haka ki gyara wallahi Karki ma fara musu da mu bazata haifar miki da da' mai ido ba,
Ta mike gobe ki shirya kije gidan Su Aishan momyn ku nason ganin ki, tafita daga dakin,
Karfe biyu momy RAHAMA ta kira mijinta lokacin ya taso shima daga bakin aikin shi, tace "Allahu ya kiyaye min kai zuciyar RAHAMA, "hhhh yayi dariya " Karki rika fasa min kai fa shiyasa na kasa kara Aure har gobe saboda inada ke Hajiya ta, " hhh yanzu dai kana ina?
" ina hanyar shigowa Asibitin ki kifito mutafi gidan momy na ko, bansan neman da take mana ba, mikewa tayi Kawai tana gyara mayafin ta tareda cire lab cot din tafita, ma aikata sai gaida ita sukeyi domin matar nada kima da sanin darajar Mutane koda nakasan tane don haka kullum rayuwar ta keci gaba ta gefen taimako ma kullum Asibitin ta mutane tururuwa sukeyi har Asibitin taimako ake kiran shi,
Tundaga nesa ta hango katotuwar motar shi tafara taku cikin natsuwa tana jin wani irin dadi, har ta isa kusa da motar ta yayi saurin fitowa tareda sakin fuska, yana nan cikin gayun shi saidai girma da ya nuna afuskar shi yayi sauri ya bude mata motar "bismilah hajiya ta, ta shiga ta gyara zama shima ya zagaya ya shiga saida ya zauna, " ina driver yau? " ai nasan bakyaso shiyasa nazo nikadai tunda convoy dina ma kinsan sundaina bina, " uhm ai baida Amfani ne mutum kamar yana nuna kanshi ne a duniya kuma fariyar tayi yawa, duk ka cika gida da motoci,
"Yazakiyi da D'an ki da yake jera mota Biyar a bayan shi kuma yanzu? " shima ima mai surutu Kasan momy goyon bayan shi takeyi don haka nakyale su, yanzu ma karkaji da wai zancen shi ne zatayi tace muzo,
Dariya yayi kawai yana kallon hanyar fita daga tangamemen Asibitin nata mai dauke da sunan Al RAHAMA private hospital,
Direct gidan momy suka nufa lokacin ita kadaice a falon ta sanye da hijabin ta da carbi sai Y'an aikin ta dake kai kawo,.
Suka shigo da Sallama, suka zauna RAHAMA ta mike tareda cewa " momy ke kadai don Allah ki koma gidan mu Kudaina zaman kadaicin nan haka kina ganin part dinki na nan kullum sainasa An gyara shi tunda aka Gina kinki yarda ki koma,
"Hmm banason inbar dakin mijina ne Y'ar nan inajin dadi na a nan da kun kyale ni kawai, "aa momy inji Al Ameen gaskiya ki shirya kawai ki koma meye Amfanin zaman naki kekadai bayan ina raye inada gida wanda zai dauke duka zuri'ar mu ba tareda takura ba ace kina zaman kadaici,
Toh yazanyi Al Ameen ya'yan kune sunki su zauna dani saidai suzo su isheni su wuce ita Husna kuwa Kasan dakyar ma Ali yake barin ya'yan gwal dinshi na fita suzo ma duk su isheni, dazu ma nan da nasir da takwaran malam da kuma na Alhaji suka Zo suka isheni saida dodon su yazo suka bar gidan,
Kitchen RAHAMA ta shiga ta hado musu Abin motsa baki ta fito, ta ajiye ga tsakiyar su, "momy Kince kina kiran mu Allah yasa lafiya? "Eh lafiya ba lafiya ba, zancen sadiq ne yazomin da wata magana dazu,
Yace infada maka yanason Aure, don haka tun wuri kayi mai tunda yafada kuma yanada Abin yi, yanada karfin rike mata hudu ma ba daya ba,
Rike baki Al Ameen yayi "yanzu momy shine sadiq din da kanshi yafito yace ayi mai Aure? Wata irin kunya ta rufe RAHAMA wai Aure lallai ma yaron nan baida kunya, "yanzu don girman Allah momy sadiq ne za ayiwa Aure? "Eh nadai fada maka sakone na isar kuyi duk Abinda kuka ga dama, "yanzu momy koni lokacina ai ku kuka sa nayi Aure bantaba fadar irin haka ba bare shi "karka hada kanka dashi inbaso kake inyi maka tone tone ba,
"Ayi hakuri zanduba yafada yana daukar juice din da Aka Ajiye mai ya kurba yana tunanin tabbas shima badon baida lafiya ba lokacin shi kila da ya nemi Auren kila irin halittar shi sadiq din yakeda,
A natse RAHAMA ta gyara zama " momy yafada miki yasamu mata ne? "Aa yace zai nema ko a nemo mai Amma wai sweet sixteen fa, tsaki Al Ameen yayi " yanason Aure za abashi karamar yarinya don yana mugu, inya shirya ya Nemo sai inyi mai,
"Inada shawara momy, RAHAMA tafada, cikda hikima tafara cewa "ni ina ganin da an hadashi da Y'ar uwar shi duk da shekarun su daya amma hakan kamar yafi tunda ta mallaki hankalin kanta,
Wani irin washe fuska momy tayi "nadade ina hango wannan hadin to kinsan halin d'an gidan nawa bayason babbar mace wai sun bude ido kiji min shirme fa,
Al Ameen yace "indai batada miji tsayayye zan yi magana da Alhaji bello mu tsaida zance a bashi ita a wuce wurin, "toh ku tattauna inkun gama komai sai infada mai
Amma akwai tsiya fa kasan halinka ya dakko harma yafika kafiya sadiq karyazo ya sa Y'ar mutane a gaba ya wulakanta,
Samun gefe daya tayi ga kannen ta biyu mata sai matashin namiji wanda yake karamin su a ciki, ta gaida baban ta fuskar ta akasa, " Amina, "na am ta Amsa, " me kike jira da maganar fitarda miji? Duk kannen ki sunfito da nasu nadakatar dasu saboda banaso inyi musu Aure ke kina gida,
Nasan dai ba masoya kika rasa ba meye dalilin rsshin tsaida gwani guda daya? Wani irin faduwa taji gaban ta yayi Allah yasani ita Sadiq takeso Amma tayaya zata fito ta fadawa baban ta hakan, tsawar da mama HAJARA ta buga mata tasa ta dago cikeda tsoro, " iya shege badake ake magana ba, in kina da Abin fada ki fada inbabu tashi Kibawa mutane wuri, Alhaji samu zakayi cikin yaran ku na wurin aiki maiso yazo abashi nidai bazata zauna min a gida ba in kannin ta sunyi Aure,
"Bi a hankali maman yara A lallaba ta kawai ta tsaida mutum guda cikin mane manta, " idan kabi ta yarinyar nan bazata taba fitowa da wani tace gashi ba don mugun korar wulakanci take musu bansan dalili ba, don haka idan kaji tatawa wallahi katsayar Kawai da kanka,
Kuka tasa mai karfi tareda zabura " wallahi nidai karku hadani Aure da wani ni wallahi banason kowa ni akyale ni inkuma akayi zan kashe kaina kowa ya huta, bazan taba iya zama da wani namiji ba ku kyale ni, ta fita da gudu tabar dakin,
Wani irin tukukin bakin ciki ne ya rufe mama Hajara yau Y'ar da ta Haifa ke fadar irin wa innan Kalamai a gaban ta? Lallai duniya dama anfada komai biyadin biyadin ne Inkayi sai anyi maka, a yau tasan zafin irin bijirewar ya'ya agaban iyayen su, Alkhairin Allah yakaiwa iyayen ta a duk inda suke, ita da ya shuka rashin mutunci buhu buhu Yau gashi Y'ar ta batayi irin nataba Amma taji ciwon kalaman,
Wasu irin hawayen takaici tareda nadamar rayuwar ta ta Y'an matan ci da sam bata da riba don haka dole ta takawa Y'ar ta birki don ita batada hakuri irin nasu inna,
Kallon ta Alhaji bello yayi " kibi ta a hankali Karki ce mata komai ni zan zabo mata miji karyar shegan taka takeyi kuma kutashi ku tafi, yafadawa kannen da sukayi tsit a wurin,
Abin yayi mugun damun HAJARA don haka mikewa tayi ta nufi dakin ta ta kulle tareda daukar wayar ta ta kira Y'ar uwar ta kuma Abokiyar shawarar ta a kullum mai hangen nesa,
A zaune take a ofishin ta na likita sanye cikin lab cot dinta fara kal tareda farin glashin ido, kana ganin ta zakasan tagama samun duniya saura goben ta kawai tayi fess da ita ta waye karshen aji,
Leshin dake jikinta kawai zaka Kalla Kasan matar manya ce ita,
Daukar wayar ta tayi datayi kara tasa akunne a cikin sauri tace "yaya barka da rana,
"Barka dai RAHAMA ya aiki? Alhmdulillah, yaya lafiya najiki cikin damuwa? " Hmm Y'ar kice, a anan ta fada mata komai tareda cewa " yau ta sa na tuna irin bijirewar da nayiwa su inna Allah ya gafarta musu RAHAMA Ashe haka Abin keda ciwo, wallahi yanzu haka zuciya ta har wani irin tafasa takeyi akan ta zan iya shake Y'ar nan kowa ya huta,
"Yi hakuri yaya kibita a hankali yanzu ki zaunar da ita kibata misali da rayuwar mu ita kadai ta isheta darasi, kuma nima zankirata gobe weekend inmata Nasiha insha Allahu yaya kibi komai A hankali,
"Toh tace tareda yin Ajiyar zuciya ta kashe wayar, tanajin sanyi tareda godiya da Allah yabata Y'ar uwa irin RAHAMA,
Tashi tayi ta nufi dakin yaran nata, tace kannin sufita zatayi magana da yayar su wadda ta hada kai da guiwa tana kukan bakin ciki, zama tayi gefen ta "Meenal, kina jina, dago kanki, tafada cikin taushin murya, ta dago duk fuskar ta fara tayi ja sumar dake kwance a gefen fuskar ta dake kara mata kyau duk sun jike da zufa, meenal photo copy din maman tace sai dai tafi HAJARA kira sosai don ita Allah ya hore mata dukiyar fulani da kuma hips kamar zasuyi magana wanda duk Lafiyayyan namiji zaiso mallakar mace kamar ta, ga ta fara tass kamar kataba jini ya fito,
Kallon maman ta tayi tana share hawaye tareda shashsheka, " me kike son ki zama a rayuwar ki? "Ya' tagari ko batacciya? Ayau inaso ki kalli rayuwar mu nida Y'ar uwata kafin a sameku akwai kalubale da muka fuskanta a cikin rayuwar mu, Karki cigaba da wannan halin da kika fara nunawa yau zamanin ki ba irin namu bane halin iyayen ki daban da nawa kije kitanbayi momyn ku irin Abin da nayi a baya wanda banci ribar shi ba don haka ki gyara wallahi Karki ma fara musu da mu bazata haifar miki da da' mai ido ba,
Ta mike gobe ki shirya kije gidan Su Aishan momyn ku nason ganin ki, tafita daga dakin,
Karfe biyu momy RAHAMA ta kira mijinta lokacin ya taso shima daga bakin aikin shi, tace "Allahu ya kiyaye min kai zuciyar RAHAMA, "hhhh yayi dariya " Karki rika fasa min kai fa shiyasa na kasa kara Aure har gobe saboda inada ke Hajiya ta, " hhh yanzu dai kana ina?
" ina hanyar shigowa Asibitin ki kifito mutafi gidan momy na ko, bansan neman da take mana ba, mikewa tayi Kawai tana gyara mayafin ta tareda cire lab cot din tafita, ma aikata sai gaida ita sukeyi domin matar nada kima da sanin darajar Mutane koda nakasan tane don haka kullum rayuwar ta keci gaba ta gefen taimako ma kullum Asibitin ta mutane tururuwa sukeyi har Asibitin taimako ake kiran shi,
Tundaga nesa ta hango katotuwar motar shi tafara taku cikin natsuwa tana jin wani irin dadi, har ta isa kusa da motar ta yayi saurin fitowa tareda sakin fuska, yana nan cikin gayun shi saidai girma da ya nuna afuskar shi yayi sauri ya bude mata motar "bismilah hajiya ta, ta shiga ta gyara zama shima ya zagaya ya shiga saida ya zauna, " ina driver yau? " ai nasan bakyaso shiyasa nazo nikadai tunda convoy dina ma kinsan sundaina bina, " uhm ai baida Amfani ne mutum kamar yana nuna kanshi ne a duniya kuma fariyar tayi yawa, duk ka cika gida da motoci,
"Yazakiyi da D'an ki da yake jera mota Biyar a bayan shi kuma yanzu? " shima ima mai surutu Kasan momy goyon bayan shi takeyi don haka nakyale su, yanzu ma karkaji da wai zancen shi ne zatayi tace muzo,
Dariya yayi kawai yana kallon hanyar fita daga tangamemen Asibitin nata mai dauke da sunan Al RAHAMA private hospital,
Direct gidan momy suka nufa lokacin ita kadaice a falon ta sanye da hijabin ta da carbi sai Y'an aikin ta dake kai kawo,.
Suka shigo da Sallama, suka zauna RAHAMA ta mike tareda cewa " momy ke kadai don Allah ki koma gidan mu Kudaina zaman kadaicin nan haka kina ganin part dinki na nan kullum sainasa An gyara shi tunda aka Gina kinki yarda ki koma,
"Hmm banason inbar dakin mijina ne Y'ar nan inajin dadi na a nan da kun kyale ni kawai, "aa momy inji Al Ameen gaskiya ki shirya kawai ki koma meye Amfanin zaman naki kekadai bayan ina raye inada gida wanda zai dauke duka zuri'ar mu ba tareda takura ba ace kina zaman kadaici,
Toh yazanyi Al Ameen ya'yan kune sunki su zauna dani saidai suzo su isheni su wuce ita Husna kuwa Kasan dakyar ma Ali yake barin ya'yan gwal dinshi na fita suzo ma duk su isheni, dazu ma nan da nasir da takwaran malam da kuma na Alhaji suka Zo suka isheni saida dodon su yazo suka bar gidan,
Kitchen RAHAMA ta shiga ta hado musu Abin motsa baki ta fito, ta ajiye ga tsakiyar su, "momy Kince kina kiran mu Allah yasa lafiya? "Eh lafiya ba lafiya ba, zancen sadiq ne yazomin da wata magana dazu,
Yace infada maka yanason Aure, don haka tun wuri kayi mai tunda yafada kuma yanada Abin yi, yanada karfin rike mata hudu ma ba daya ba,
Rike baki Al Ameen yayi "yanzu momy shine sadiq din da kanshi yafito yace ayi mai Aure? Wata irin kunya ta rufe RAHAMA wai Aure lallai ma yaron nan baida kunya, "yanzu don girman Allah momy sadiq ne za ayiwa Aure? "Eh nadai fada maka sakone na isar kuyi duk Abinda kuka ga dama, "yanzu momy koni lokacina ai ku kuka sa nayi Aure bantaba fadar irin haka ba bare shi "karka hada kanka dashi inbaso kake inyi maka tone tone ba,
"Ayi hakuri zanduba yafada yana daukar juice din da Aka Ajiye mai ya kurba yana tunanin tabbas shima badon baida lafiya ba lokacin shi kila da ya nemi Auren kila irin halittar shi sadiq din yakeda,
A natse RAHAMA ta gyara zama " momy yafada miki yasamu mata ne? "Aa yace zai nema ko a nemo mai Amma wai sweet sixteen fa, tsaki Al Ameen yayi " yanason Aure za abashi karamar yarinya don yana mugu, inya shirya ya Nemo sai inyi mai,
"Inada shawara momy, RAHAMA tafada, cikda hikima tafara cewa "ni ina ganin da an hadashi da Y'ar uwar shi duk da shekarun su daya amma hakan kamar yafi tunda ta mallaki hankalin kanta,
Wani irin washe fuska momy tayi "nadade ina hango wannan hadin to kinsan halin d'an gidan nawa bayason babbar mace wai sun bude ido kiji min shirme fa,
Al Ameen yace "indai batada miji tsayayye zan yi magana da Alhaji bello mu tsaida zance a bashi ita a wuce wurin, "toh ku tattauna inkun gama komai sai infada mai
Amma akwai tsiya fa kasan halinka ya dakko harma yafika kafiya sadiq karyazo ya sa Y'ar mutane a gaba ya wulakanta,