Sashe 7
Tattalin So Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
*** ****
karfe shidda 'yan makaranta sun dawo, suna cin abinci ba dadewa akayi mangariba, suna idar da sallah hajiya ta rungumo zainab jikinta tana shafa kanta, tace "zainab yanzu fa yayanki zai zo zai tafi dake gidansa, zaki ci gaba da zama acan."
zainab tasa kuka tace, nidai hajiya bazan jeba nace, yai tamin fada koma ya dokeni, hajiya tace bazai dokeki ba, kuma fada ma ya daina yi miki. Kije ki zauna kinji zainab? Ta make kafada, um-um, ni ba zanje ba."
suna haka taji yo sallamarsa, da sauri ta tashi da gudu tai cikin dakin hajiya. Aliyu ya shigo ya sake gaida hajiya, hajiya tace masa "zainab dai tace baza taje ba, ka ganta can harda kuka."
ya kwala mata kira ta fito a tsorace, tazo ta durkusa a gabansa
yace "shine kika ce bazaki gidana ba? Ta girgiza kai alamar cewa, a'a yace to meye nayin kukan? Yi min shiru. Tasa hannunta ta toshe bakinta ta hadiye kukan.
Yace ki goge hawayenki kije, kiyi wa Abba da daddy sallama." tace to, ta goge fuskarta. Ta shiga bangaren su umma ta tarar da Abba da umma da ummi suna falo, Abba yace yaki 'yata tazo ta zauna a jikinsa." yace menene naga idonki alamar kinyi kuka? Tace bakomai, Abba sallama nazo inyi muku zan koma gidan yaya."
Abban yace "zainab bana son abunda zai takuraki, in bakya son zuwa ni zansa ya kyaleki kiyi zamanki." tace a'a Abba zanje." yace to shikenan zainab, Allah yayi miki Albarka, kici gaba da maida kai da kokari a makaranta, tanan ne zaku fi shiri da yayan naki kinji 'yata?
Tace "to Abba nagode." ta mike ta shiga wajen daddynta, ta daura kanta akan cinyarsa tana kuka. Yasa hannunsa yana shafa kanta yace "kiyi hakuri zainab, nasan bakya son tafiya. Zainab ko yaushe kina raina, dana ganki saikin tunamin da mamanki. Zainab du ina tausaya mana ni dake na rashin mamanki.
Kiyi hakuri zainab kiyi zamanki, nasan zai rikeki da amana kamar ni. Kiyi masa biyayya shida matarsa, banda rashin kunya kinji? Tace "to daddy zan kiyaye." ya bude firij ya dauko rubutu a roba ya bata, ungo shanye rubutunki maganin tsari da kariya daga shaidanu." ta karba tayi bisimilla ta shanye, ya karba yasa ruwa ya dauraye mata, ta karba tasha, ragowar ya zuba a hannunsa ya shafa mata a kanta da fuskarta.
Yaita mata nasiha mai shiga jiki, yace ta daina kuka ta tashi taje su tafi." hajiya dasu ni'ima su sadik har gindin mota suka rakota suna hawaye tana hawaye.
Surayya
[1:23PM, 04/05/2017] 💞@lh@ji💞: TATTALIN SO 1**11
HAJIYA tana rungume da ita tana rarrashinta suka bude mata gaban mota ta shiga, ta dunkufar da kanta akan gwiwoyinta tana ci gaba da kukanta kasa-kasa, Aliyu ya sallame su du yaraba musu kudi, yace su koma gida, suna tunanin 'yar uwarsu wai anrabata da gidansu kenan.
Ya kalleta au baki daina kukan ba? Tayi saurin hadiye kukan nata, ta goge idanuwanta. Tafiya kadan suka isa gidansa, suka fito har daki ya kaita, "nan shine dakinki, talatuwa zata rinka taya ki kwana." dakin yayi kyau, a yau dinan ya sayo mata gadon silba da madubi, sai kwaba ta jikin bango, sai labuye da jan kafet, shikenan ba wani shirgi, sai toilet aciki dake gefe, tace "to yaya." ya fita ya nufi sashinsa, zainab itama ta shiga dakin aunty mansura.
Zainab ta kwantar da hankalinta tana zaune a gidan yayanta, tsakaninta da abinci saita ga damar ci, ko yaushe yayan nata yana cikin siyo musu ice-cream, youghot su biskit da cakulet, da yake abinci bai dami zainab ba, ita hakan saya fiye mata dadi.
Ita kuwa mansura ta fiya lalaci da sangarta, bata wani iya girki ba, shikuwa Aliyu dan gaye ne mai aji, gashi da kyankyami, don haka bazai iya cin abincin mai aiki ba.
Don haka inya zo garin ma saidai yaje gida yaci abinci, don a gidansa inna laraba ita take yin girki. Babbar mace ce amma da kwarinta, don bata wuce yin aure ba, sai 'yar budurwa wato talatuwa, ita take yi mata shara dasu goge-goge da gyaran gado, inta yi baki ta kula dasu. Don wata wauta ta mansura dai-dai da mijin ma inya nason wani abu sai dai ta kira talatuwa.
Don haka ma ko meye ya gwammace yayi da kansa, abinci kuwa saiya je gidansu sannan yaci. A gidansu su umma har fada suke yi masa, don me zai rinka baro girkin matarsa baya son ci.
Sai dai yayi murmushi kawai yace musu bakomai. Bama yanzu da mansura take fama da laulayi. Da safe yana zaune a falo da wando iya gwiwa da farar shirt, yana lumshe idanuwarsa kamar mai jin barci. Mansura tana zaune kusa dashi tana cin wainar kwai da dankalin turawa, ta zuba shayi a kofi yana ta turiri, gashi yayi kauri da hadin madara da naskofi da dai sauransu.
Zainab ta fito sanye cikin shirin makaranta, ta durkusa ta gaishe da yayan nata da mansura. Ta mike a gurguje take, dan takusa makara. Ta dauki shanyin gaban auntyn nata tadan kurba, tace "wai aunty wannan kaurin ai yayi yawa, bakya tsoron ya kulle miki ciki?
Mansura tayi dariya tace, laifin babynku ne ba ruwana. Zainab tayi dariya tace ai, "ai gwanda ki dinga ci sosai don ki haifa mana katon baby in rinka daukarsa da kyar." ta nufi firij ta dauko ice-cream da youghot da cake, tazo ta wuce su da sauri saboda yayan nata, tace aunty natafi makaranta." kafin tayi magana Aliyu ya kirata "zainab."
tayi saurin juyowa tare da amsawa, a sanyaye tace na'am yaya." zo nan. Ta dawo ta durkusa a gabansa. Yace haka zaki tafi makaranta baki karya ba? Tace yaya zanci cake da ice-cream da youghot a mota." yace wato har yanzu kina nan dakin cin abincin ki ko sai kayan kwadayi? Ke wace iri ce ne? Da safe ma sai kin sha sanyi bazaki ci abinda zai dumama miki ciki ba?
Mansura tace wallahi haka nake fama da ita, bata son cin abinci, daga shan kayan zaki sai shan kayan sanyi." yace ina break din nata? Mansura ta kwalawa talatuwa kira, tace mata ina break din zainab? Talatuwa ta shiga dakin zainab da sauri ta dauko break din data kai mata, yanda ta ajiyeshi haka yake, ko budawa bata yiba. Ta ajiye a gaban zainab din.
Aliyu ya kalleta yace to maza ki cinye shi yanzun nan." idonta yayi rau-rau alamar sonyin kuka. Shikuwa sai ya jingina da kujera ma ya lumshe shanyayyun idanuwansa kamar zaiyi barci. Ba yanda zata yi, haka ta rinka tura dankalin nan da kwai tana shan ruwan shayin.
Cikinta ya cika taji kokarin yin amai take yi, tace a hankalin cikin sanyin muryanta, "yaya ya dago kai yayi mata wani kallo, bata iya fada masa komai ba, ta sake sunkuyar da kanta, ya sake lumshe idonsa.
Haka taci gaba da ci tana hawaye, saida ta cinye du. Dakyar ta iya tashi tsaye, tace yaya na cinye, na tafi? Ya bude ido daya yayi mata alama da hannu wai ta tafi. Ta fice inda direba yake jiranta ta shiga ta tafi.
Mansura tace gaskiya Aliyu kana matsawa yarinyar nan, da nice saika bata min rai kace ina takurawa kanwarka." ya bude ido daya yace karki manta shekaranta goma sha daya, yanzu ta shiga sakandari aji daya, har yanzu ita yarinya ce, idan bana matsamata taci abinci sai yunwa ta kamata."
ta tabe baki tana gunguni, "in rashin cin abinci ne ai a wurinka ta gado, tunda kaima baka cin na gidanka." ya kwanto akan cinyarta yace, kiyi min da kanki mana, du rashin dadinsa ai zanci. Amma zaki rinka sa tsohuwar mutane wahalar girki, sannan kisa wata yarinya daban itace mai bani abinci, kallon yarinyar nan kadai tayar min da zuciya yake."
ta zumburi baki bata ce komai ba, ya shafa cikinta yana cewa, "i luv u baby, yaushe zaka iso kaga daddynka? Tace ai kuwa zai jima baiga daddyn ba, sai nan da wata biyar." ya gyada kanshi, Allah kawo minshi lafiya."
tadan rankwafo kanshi tace, "Aliyu dan Allah zaka danyi min tausa?
karfe shidda 'yan makaranta sun dawo, suna cin abinci ba dadewa akayi mangariba, suna idar da sallah hajiya ta rungumo zainab jikinta tana shafa kanta, tace "zainab yanzu fa yayanki zai zo zai tafi dake gidansa, zaki ci gaba da zama acan."
zainab tasa kuka tace, nidai hajiya bazan jeba nace, yai tamin fada koma ya dokeni, hajiya tace bazai dokeki ba, kuma fada ma ya daina yi miki. Kije ki zauna kinji zainab? Ta make kafada, um-um, ni ba zanje ba."
suna haka taji yo sallamarsa, da sauri ta tashi da gudu tai cikin dakin hajiya. Aliyu ya shigo ya sake gaida hajiya, hajiya tace masa "zainab dai tace baza taje ba, ka ganta can harda kuka."
ya kwala mata kira ta fito a tsorace, tazo ta durkusa a gabansa
yace "shine kika ce bazaki gidana ba? Ta girgiza kai alamar cewa, a'a yace to meye nayin kukan? Yi min shiru. Tasa hannunta ta toshe bakinta ta hadiye kukan.
Yace ki goge hawayenki kije, kiyi wa Abba da daddy sallama." tace to, ta goge fuskarta. Ta shiga bangaren su umma ta tarar da Abba da umma da ummi suna falo, Abba yace yaki 'yata tazo ta zauna a jikinsa." yace menene naga idonki alamar kinyi kuka? Tace bakomai, Abba sallama nazo inyi muku zan koma gidan yaya."
Abban yace "zainab bana son abunda zai takuraki, in bakya son zuwa ni zansa ya kyaleki kiyi zamanki." tace a'a Abba zanje." yace to shikenan zainab, Allah yayi miki Albarka, kici gaba da maida kai da kokari a makaranta, tanan ne zaku fi shiri da yayan naki kinji 'yata?
Tace "to Abba nagode." ta mike ta shiga wajen daddynta, ta daura kanta akan cinyarsa tana kuka. Yasa hannunsa yana shafa kanta yace "kiyi hakuri zainab, nasan bakya son tafiya. Zainab ko yaushe kina raina, dana ganki saikin tunamin da mamanki. Zainab du ina tausaya mana ni dake na rashin mamanki.
Kiyi hakuri zainab kiyi zamanki, nasan zai rikeki da amana kamar ni. Kiyi masa biyayya shida matarsa, banda rashin kunya kinji? Tace "to daddy zan kiyaye." ya bude firij ya dauko rubutu a roba ya bata, ungo shanye rubutunki maganin tsari da kariya daga shaidanu." ta karba tayi bisimilla ta shanye, ya karba yasa ruwa ya dauraye mata, ta karba tasha, ragowar ya zuba a hannunsa ya shafa mata a kanta da fuskarta.
Yaita mata nasiha mai shiga jiki, yace ta daina kuka ta tashi taje su tafi." hajiya dasu ni'ima su sadik har gindin mota suka rakota suna hawaye tana hawaye.
Surayya
[1:23PM, 04/05/2017] 💞@lh@ji💞: TATTALIN SO 1**11
HAJIYA tana rungume da ita tana rarrashinta suka bude mata gaban mota ta shiga, ta dunkufar da kanta akan gwiwoyinta tana ci gaba da kukanta kasa-kasa, Aliyu ya sallame su du yaraba musu kudi, yace su koma gida, suna tunanin 'yar uwarsu wai anrabata da gidansu kenan.
Ya kalleta au baki daina kukan ba? Tayi saurin hadiye kukan nata, ta goge idanuwanta. Tafiya kadan suka isa gidansa, suka fito har daki ya kaita, "nan shine dakinki, talatuwa zata rinka taya ki kwana." dakin yayi kyau, a yau dinan ya sayo mata gadon silba da madubi, sai kwaba ta jikin bango, sai labuye da jan kafet, shikenan ba wani shirgi, sai toilet aciki dake gefe, tace "to yaya." ya fita ya nufi sashinsa, zainab itama ta shiga dakin aunty mansura.
Zainab ta kwantar da hankalinta tana zaune a gidan yayanta, tsakaninta da abinci saita ga damar ci, ko yaushe yayan nata yana cikin siyo musu ice-cream, youghot su biskit da cakulet, da yake abinci bai dami zainab ba, ita hakan saya fiye mata dadi.
Ita kuwa mansura ta fiya lalaci da sangarta, bata wani iya girki ba, shikuwa Aliyu dan gaye ne mai aji, gashi da kyankyami, don haka bazai iya cin abincin mai aiki ba.
Don haka inya zo garin ma saidai yaje gida yaci abinci, don a gidansa inna laraba ita take yin girki. Babbar mace ce amma da kwarinta, don bata wuce yin aure ba, sai 'yar budurwa wato talatuwa, ita take yi mata shara dasu goge-goge da gyaran gado, inta yi baki ta kula dasu. Don wata wauta ta mansura dai-dai da mijin ma inya nason wani abu sai dai ta kira talatuwa.
Don haka ma ko meye ya gwammace yayi da kansa, abinci kuwa saiya je gidansu sannan yaci. A gidansu su umma har fada suke yi masa, don me zai rinka baro girkin matarsa baya son ci.
Sai dai yayi murmushi kawai yace musu bakomai. Bama yanzu da mansura take fama da laulayi. Da safe yana zaune a falo da wando iya gwiwa da farar shirt, yana lumshe idanuwarsa kamar mai jin barci. Mansura tana zaune kusa dashi tana cin wainar kwai da dankalin turawa, ta zuba shayi a kofi yana ta turiri, gashi yayi kauri da hadin madara da naskofi da dai sauransu.
Zainab ta fito sanye cikin shirin makaranta, ta durkusa ta gaishe da yayan nata da mansura. Ta mike a gurguje take, dan takusa makara. Ta dauki shanyin gaban auntyn nata tadan kurba, tace "wai aunty wannan kaurin ai yayi yawa, bakya tsoron ya kulle miki ciki?
Mansura tayi dariya tace, laifin babynku ne ba ruwana. Zainab tayi dariya tace ai, "ai gwanda ki dinga ci sosai don ki haifa mana katon baby in rinka daukarsa da kyar." ta nufi firij ta dauko ice-cream da youghot da cake, tazo ta wuce su da sauri saboda yayan nata, tace aunty natafi makaranta." kafin tayi magana Aliyu ya kirata "zainab."
tayi saurin juyowa tare da amsawa, a sanyaye tace na'am yaya." zo nan. Ta dawo ta durkusa a gabansa. Yace haka zaki tafi makaranta baki karya ba? Tace yaya zanci cake da ice-cream da youghot a mota." yace wato har yanzu kina nan dakin cin abincin ki ko sai kayan kwadayi? Ke wace iri ce ne? Da safe ma sai kin sha sanyi bazaki ci abinda zai dumama miki ciki ba?
Mansura tace wallahi haka nake fama da ita, bata son cin abinci, daga shan kayan zaki sai shan kayan sanyi." yace ina break din nata? Mansura ta kwalawa talatuwa kira, tace mata ina break din zainab? Talatuwa ta shiga dakin zainab da sauri ta dauko break din data kai mata, yanda ta ajiyeshi haka yake, ko budawa bata yiba. Ta ajiye a gaban zainab din.
Aliyu ya kalleta yace to maza ki cinye shi yanzun nan." idonta yayi rau-rau alamar sonyin kuka. Shikuwa sai ya jingina da kujera ma ya lumshe shanyayyun idanuwansa kamar zaiyi barci. Ba yanda zata yi, haka ta rinka tura dankalin nan da kwai tana shan ruwan shayin.
Cikinta ya cika taji kokarin yin amai take yi, tace a hankalin cikin sanyin muryanta, "yaya ya dago kai yayi mata wani kallo, bata iya fada masa komai ba, ta sake sunkuyar da kanta, ya sake lumshe idonsa.
Haka taci gaba da ci tana hawaye, saida ta cinye du. Dakyar ta iya tashi tsaye, tace yaya na cinye, na tafi? Ya bude ido daya yayi mata alama da hannu wai ta tafi. Ta fice inda direba yake jiranta ta shiga ta tafi.
Mansura tace gaskiya Aliyu kana matsawa yarinyar nan, da nice saika bata min rai kace ina takurawa kanwarka." ya bude ido daya yace karki manta shekaranta goma sha daya, yanzu ta shiga sakandari aji daya, har yanzu ita yarinya ce, idan bana matsamata taci abinci sai yunwa ta kamata."
ta tabe baki tana gunguni, "in rashin cin abinci ne ai a wurinka ta gado, tunda kaima baka cin na gidanka." ya kwanto akan cinyarta yace, kiyi min da kanki mana, du rashin dadinsa ai zanci. Amma zaki rinka sa tsohuwar mutane wahalar girki, sannan kisa wata yarinya daban itace mai bani abinci, kallon yarinyar nan kadai tayar min da zuciya yake."
ta zumburi baki bata ce komai ba, ya shafa cikinta yana cewa, "i luv u baby, yaushe zaka iso kaga daddynka? Tace ai kuwa zai jima baiga daddyn ba, sai nan da wata biyar." ya gyada kanshi, Allah kawo minshi lafiya."
tadan rankwafo kanshi tace, "Aliyu dan Allah zaka danyi min tausa?