← Book details Tattalin So Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 32 OF 44

Sashe 32

Tattalin So Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read

Saratu tace, to kinga inada kudi dubu goma shabiyar, zan
sai super nan taki dasu, tunda ta zamata hannu, saina je
miki gidan malam da kudin.Mansura tace, to
shikenan.Saratu ta fita da super ta kaita dinki, tana cewa
aranta.Me shegiyar rowar tsiya, inba da hakaba bazakaci
komai nata ba.Tace, na fara jin tausayinki, yanzu zanje nayi
mikitaimako daya, don ta hanyar ne kawai Aliyu
zaisaurareta, wannan uban zuciyar.Daga nan saita wuce
ofis din daddyn zainab, yacelafiya saratu kika zo nan?Cikin
ladabi tace, wallahi daddy daman akanabunda mansura
tayiwa zainab ne nazo karabaka hakuri, wallahi mansura
tayi nadama sosai,don Allah daddy kayi hakuri, kasa Aliyu
ya mayarda ita dakinta.Daddy yace banganeba, kina nufin
wai mansurabata gidan Aliyu?Tace wallahi daddy tun sanda
tayiwa zainab abunnan ya korata gida. Har yanzu tana
nan.Iyayenmu kuma sunce ba ruwansu, donsukunyarku
suke ji.Ba zasu tunkareku da maganar ba.Daddy ya rinka
salati yana cewa, wallahi daga shihar iyayensa basu san
haka ba.Abu wajen wata uku, ace tana zaune a gida,
Aliyuyayi kuruciya, yace kije saratu yanzun nan zannemi
Aliyu a waya, a satin nan mansura zatakoma
dakinta.Saratu ta taso tanata godiya.Tana zuwa gida ta
cewa mansura ai malaminyace, ta kwantar da hankalinta,
acikin satin nanALiyu zai zo da kansa bikonta, tace, yace
ammadaya zo kibishi, idan kika ce zaki tsaya jan aji, tokuwa
ajin zai tsinke miki, ke kika jiyo wannankuma ba
ruwana.Mansura tace, um ni abun mafa ya fara banitsoro,
Allah yasa dai yazo din.Can kuma Saratu na fita daddy ya
kira Aliyu,ringin daya tayi Aliyu ya dauka, da saurinsa
yarissina yana gaishe shi, saika ce agabanshi yake.Yace
haba Aliyu kai danake ganin hankalinka,zakayi wannan
danyen aikin? Ka ajiye mace agidansu tsawon wata uku,
baka waiwaiyeta ba?Kuma dagani har yayana bamu sani
ba, ai sai arinka zarginmu ace don mun aura maka
tamunemuka sa ka wulakanta 'yar mutane.Banji dadin
abunda kayi ba Aliyu kwata-kwata.Aliyu yace kayi hakuri
daddy, Allah ya hucizuciyarka.Yace na hakura Aliyu, amma
kazo da kanka, kajekayo bikon matarka, yace to Abba
zanzo.Kazo fa acikin satinnan, bana so a kuma
daukanlokaci.Yace "to daddy insha Allahu jibi karshen
satizanzo.To Allah kaimu.Sukayi sallama yana yi masa
godiya suka kashewayar.Kanta yana kan cinyarsa tana so
tayi bacci, tabude idonta tace, yaya me kayiwa daddy,
duyanda kuke shiri dashi yake cewa yau bakakyauta ba?
Yace akan maganar auntynki ne yake min fada,naje na
dawo da ita gidana.Yaya wai ina ta tafine?Gidansu na
turata, take ta zama, tace kai yayaauntyn tawa? Ni wallahi
dana san tana gidansuda tuni naje da kaina nayo
bikonta.Meyasa yaya kayi mata haka.To ya zanyi mata
zeeyta? Ta tabamin tauraruwarmatana, ai dole in nuna mata
kurenta.Amma kuma yaya saika barta a gidansu
kowayasan tana gida?To zeeyta ai bani da abinda zan mata
daya fihakan, don in nace dukanta zanyi bansan waniirin
mugun duka zanyi mata ba.Kuma in na daketa mutane
saisu manta abundatayi min, ace na daketa akan kanwata,
yanzukuwa kinga ba duka ba zagi, nasan ta horu.Tayi dan
murmushinta mai kashe zuciya tace"yaya jibin da wuri
zamu tafi ko?Yace ina? Keda fita ai sai ranar da kika
zamamace.Yaya yanzu ni ba mace bace?Yanzu ke muna
mace ce, baki zama cikakkiyarmace ba tukunna.Yaya to
yaushe zan zamo macen?Du ranar da kika so zaki
zama.Tayi shiru tana tunani me kalmar tasa ke nufi,
saikawai ta share maganar, bata kuma zancen zatabishin
ba.Sai da safe bayan sun gama break, yake ce mata,sadik
tuntuni sun taho, suna kan hanya, zai kawomiki talatu nan
zata ci gaba da zama dake,kwana uku zanyi na dawo.Ta
zumbura baki ta mike tsaye tana bubbugakafa, ta tafi wajen
labule zata bude ta fita.Ya kirata, zeeyta meye haka?To
yaya kai kadai zaka tafi, ni bazaka tafi daniba, naga su
Abba da dady ba?Don Allah yaya ka tafi dani kaji?Ya girgiza
kai, kiyi zamanki a gida, kwana ukukawai zanyi. Ta juya ta
hada kanta da bango takama kuka, ya taso ya jawota
jikinsa, yanararrashinta, yi hakuri zeeyta keda kike
'yargatana, ga sadik nan shida talatu zasu zaunadake, har
na dawo, tunda sadik yana cikin hutuzai zauna idan
nadawo, sai ya tafi, talatu kuwaanan zata zauna ta ringa
taimaka miki.Ko bakya son zuwan sadik din? Tace
inaso.To yi shiru share hawayenki, bazan dade ba
kinjizeeyta.Ta daga masa kai, to yi dariya.Tasa dariya,
yauwa zeeyta. Dai-dai lokacin daake kwankwasa kofa ta
bude da sauri, wadandatake zato su dinne, ta kankame
sadik tana murna,ta riko hannun talatu tana yi musu sannu
dazuwa.Lokaci kankani ta cika musu gabansu da
kayanciye-ciye, sannan ta zauna suna gaisawa, tatambayi
wannan ta tambayi wancan.Sukuma sunata cin abubuwa
data kawo musu,suna gamawa suka mika suna zaga
gidan.Sadik ya rinka santin gidan, gskya yaya ka
gamahutawa wannn tanfatsetsen gidan, gashi yajikayan
kawata gida kaman a turai? Aliyu yayimurmushi yace Allah
sarki sadik, to idan ka tashiaure irinsa zan gina maka.

Sadik yayi dariya yace, yaya nan dashekara sha biyar fa."au
kace saika kusa zama tuzuru,sannan zakayi auren?Dai-dai
lokacin da suka shigo boyskwatas yace to ga inda zaka
zauna.Aliyu ya gama shirinsa, zainab taratayo jakarsa ta
taho zata yi masarakiya, har zuwa wajen mota.Ya shiga
motar ya zauna, ta sakomasa jakar idonta yayi rau-rau
tanakokarin zubo da hawayen nata.Ya jawota kan cinyarsa,
haba zeeytabazaki yi min addu'a ba, sai kuka,kina so ki
daga min hankalina, nakasa tukin? Tace yi hakuri
yaya,Allah ya kiyaye hanya ya dawo dakailafiya.Yace
yauwa zeeytah, maza tafi gidadon bazan iya tafiya na barki
aharabar gidan nan ke kadai ba.Ta juya tana dan gudunta
da tsalle-tsallenta, tana dariya tana daga masahannu,
alamar bye-bye, ya dauko yawayarsa ya ringa daukarta a
bidiyo,tana ganin yana daukarta, tasadariya ta juya tayi
cikin gida tanacewa yaya saika dawo.Yayi dariya ya kashe
wayar yasata aaljihu.Yaja motar ya tafi.A hanya ya tsaya
yayi musu uwartsaraba. Yana isa gida, ya samu suAbba da
daddy dasu mama, sunatahiransu cikin nishadi.Yayi
sallama cikin falon, suka amsamama da ummi suna ga
Aliyu gaAliyu.Ya rissina ya gaishesu, daddy yaceAliyu jeka,
ka nutsu ka dan huta inanijima kaje ka dawo da matarka.To
daddy nagode, ya mike ya fitayasa me gadinsu dame wanki
sukashishigar da kayan.Ya shiga motarsa yaja sai gidansu
dazeey.Yana shiga gidan, wannan dadadankamshi yana
nan, ya rasa wannansirrin kamshi na zeey dinshi.Ya fada
toilet yayi wanka yayi sallah,yana fitowa ya tarar hamzaya
kawo masa abinci daga gida.Yaci ya kwanta a gado don ya
danhuta, yana so yayi bacci, amma sai yakasa rintsawa
tunanin yaji zeeydinshi a manne a kirjinsa yadameshi.Ya
jawo wayarsa ya buga mata,ringin daya ta dauka, hello
yayanakaje lafiya?Nazo lafiya, gashi har naci abinci,nayi
wanka, nayi sallah na kwantawai don na dan huta, tunaninki
yahanani bacci.Cikin shgwaba tace, um ba kainekayi
tafiyarka ka barni ba?Yaya ka jawo min sai nayi awasaba'in
da biyu ban ganka ba, yacezeeyta ke rashin ganina ne
kawai, nikuwa rashin jin dumin jikinki yafikomai daga min
hankali.Zeeyta wai yaushe zaki bani dama nakusanceki?
Tace yaya me kake so nayi maka, mekake so na baka
yayana? Komai kakeso yaya zanyi mka.Matsayinka da
darajarka a wajenakafi karfin komai yayana.Yace zeeyta
ina matukar so ki banihakkina na jikinki, amma fa sai
kinara'ayi, don wallahi in zamu shekaragoma a haka bazan
taba takura mikiba, ko nayi miki dole.Kuma kada kiyi
tunanin kina dahakki a wajen ubangiji, a'a tsananinkaunar
danake yi miki bazata bari nakullace ki ba.Kona yi fushi
dake ba, na yafe mikizeeyta.Kayi hakuri yayana, na amince
maka,na baka dama du sanda kaso kayira'ayi yayana, ka
karbi hakkinka,yace dagaske zeeyta? Kada kisa nayitsuntsu
na taho yanzu.Tace a'a yayana kada ka dawo yanzu,ka
zauna ka kula da auntyna ka batahakkinta, ka rarrasheta, ka
batahakuri kan abunda kayi mata.Ina jiranka yayana nanda
kwanauku, kamar yanda kace, Allah yadawo min da kai
lafiya. Ka kulaminda auntyna ka bata hakuri, kararrasheta
ka lallbata harta huce, kashafamin kan Amadina. Kayi
hakuriyaya, don Allah kada ka damu, zankashe kada na
cinyewa auntynalokaci, don nasan yau sabon amarezaku
zama, kayi mata kalamai masusanyi da tausasa zuciya, ka
nunamata tattalin so yayana saida safe.Dif ta kashe wayar,
ya rinka juyawayar a hannunsa yana murmushi,yarinya
karama ta iya kalamai maisanyaya zuciya.Ya kunna bidiyo
wayar ya rinkakallonta sanda tayi masa rakiya, dangudun
data keyi tanata tsalle-tsallenta, tana dariya, du dai dontasa
shi nishadi ta kuwa shashi, donkifa wayar yayi a fuskarsa,
yana jinzuciyarsa wasai, cike da nishadi bacciya rinka
fusgarshi ya kashe wayar yakwanta.**** ***** ***mansura
taga shiru har mangaribaba Aliyu, tace yaya saratu anya
kuwaAliyu zai zo, kinji shiru har yanzu?Saratu tace ke
kinfiya wutar ciki, dukudin da kike kashewa wanne
kikasamu nasara kamar wannan?Kina gani kanin babanshi
yazo yaitabawa Alh hakuri, yana cewa basu sanhakaba.To
ko Aliyu baizoba idan daddynzainab ya sake zuwa basai ki
komadakinki ba, inya ji ya dawo dake aidole yazo inda
kike.Bayan sunyi sallar isha'i suna cinabinci, hajiya ta shigo
take gayamata, taje falon baki inji babanta.Mansura ta tashi
da saurinta tawanke hannunta, ta yafa mayafinta,ta nufi
falon babanta.Wani mayataccen kamshine taji yadaki
hanncinta, a hankali tayisallama, ta zauna ta cewa
babantagani. Ya mike tsaye yace, game songaninki nan sai
a sannan ta dagakanta ta ga bakon da yake zaune.Aliyunta
ne cikin shiga na alfarma,ya kara murjewa da kyau, ya
karahaske da kwarjini, fatarsa har wanidaukan ido yake
yi.Yana ta zuba kamshi mai dadi,idonsa yana sanye da
farin glass.Du saita raina kanta taga ta muzantaa gabanshi,
me Aliyu yake ci dayakara wannan kyan, da kwarjini?Lallai
Aliyunta ya kara samun canjinrayuwa, ma'ana kudi sun
sake zamamishi.A hankali tace masa ina wuni?
.
Chapter 32 · 0% Book details