Sashe 19
Tattalin So Part 1 Complete Hausa Novel · about 5 min read
DU sanda ka sake yiwa matata waya saina daureka bbu
beli. Kuma yanzu ma ka saurari zuwan kana nan sojoji,
zasu zo su koya maka
hankali." ya cire wayar da kunnansa yayi cilli da ita ta daki
bango ta tarwatse, ya karasa gurin ya ciro sim card din ciki
ya kakkarya shi gutsi-gutsi ya
watsar a wajen. Ya dago kansa yana mata wani
irin kallo, yace wannan ya zamo na karshe, idan
na kuma gani kina waya ko kina magana da wani
sai ranki ya baci." ya juya ya fita.
Ta dafe kanta tana kukanta. Ni'ima ta dawo
dakin da tun shigowar yaya Aliyu data ga sababin
da yake yi ta zame jikinta ta gudu, don kada ya
huce akanta."
ni'ima ta zauna kusa da ita ta dafa ta, tace meye
na kuka, ke matsalarki kenan saurin kuka."
tace, haba yaya ni'ima, kin san sarai yaya Aliyu
ya fiya saurin fushi da zafin zuciya, ni kuma bana
so naga bacin ransa balle kuma ace ni na bata
masa, taya za ayi zaman aure a haka?
Ni'ima tace haba zainab kefa mai hakuri ce zaki
iya zama da yaya Aliyu, don kinfi kowa iya gudun
bacin ransa. Ni sai yanzu ma na fahimta ashe du
tsanani da yaya yake yi miki soyayya ce da
kishinki da yake yi, ni wallahi ban taba ganin
amarya da ango da suka dace da juna ba irin ke
da yaya."
idonta yayi narai-narai hawaye ya sake zubowa
tace, "ke yaya ni'ima haka zaki rinka yi min?
Ta fashe da kukanta. Ni'ima ta rungumota tana
rarrashinta, "to shikenan kiyi hakuri na daina, ba
zan kuma ba."
du wayanci kawayen zainab ta gayyace su bikin
ni'ima, to da abun ya zamo haka ya hade da
nata, sai babbar kawarta hauwa Rabi'u ta rinka
yiwa kawayensu waya tana sanar musu tare da
basu hakuri na rashin ganin kati. Du da haka
saida Aliyu ya sanar a gidajen radio, saboda na
nesa kawayenta da basu sani ba.
Ranar jumma'a akayi mata kamu, kamun da ya
bada mamaki saboda cikar kawayenta da 'yan
uwanta suka yi, sai da aka fara saukar Qur'ani
sannan aka kamata."
daga nan wata malama ta bude filin da dan
wa'azinta (kusan hakkin miji akan matarsa ne
wa'azin kuma inaga munyi a baya basai na
maimaita ba).
Malamar nan tai ta wa'azi da fadakarwa akan
aure, wanda tunda aka fara zainab take kuka, dan
jikinta har rawa yake yi. Du da tasan hakkokin
miji akan matarsa babu abunda malamansu na
islamiya basu koya musu ba, amma wa'azin
malamar nan ya shigeta.
Yanzu taya zata hada jiki da yayanta Aliyu harta
kwanta gado daya dashi? Ya salam! Allah kaika
san abunda kake nufi da auren nan, Allah ka bani
ikon biyayya ga mijina.
Ranar asabar tun asuba akayi wa zainab da
ni'ima gyaran jiki, inda jikinsu ya fara laushi da
tsantsi, fuskarsu kuwa kamar kwan lantarki dan
kyau.
A wajen walima shiga iri daya akayi musu, wani
dankareren abu me kyalli da walwali pink, da
gwagwaro pink, dutsen da suka sa a hannu da
wuya duk pink, takalmi da jaka duk pink, sunyi
kyau sosai.
Walimar ta tara kyawawan 'yan mata gogaggu
masu takama da ayar Allah.
Domin ayau ma wani wa'azin aka kuma yi mai
shigarwa, daga nan wani babban malami yayi
lakca wadda ya ladftar da zuciyar mai saurare, ya
dasa tsoron Allah a zukatan wanda suka saurara.
Daga karshe aka rufe da addu'a, aka yiwa
angwaye da amare addu'ar Allah basu zaman
lafiya. Amaren suka rinka zagaye tebir-tebir suna
gaisawa da kawayensu, suna yi musu godiya da
damar da suka samu ta hallartar bikinsu.
Aunty sadiya tana ta raba manyan bokitai da
farantai, da kofunan shayi na tangaram. Sun so
yin kalanda, Aliyu ya hana wai baza aje a lika
masa hoton matarsa a wani waje ba, wani gardin
ya kalleta yayi sha'awarta ba.
Da mangariba daddyn zainab ya kira Aliyu ya
tambayeshi ya maganar mansura? Aliyu ya gaya
masa yanda sukayi, yace randa ta gaji da zaman
gidan nasu saita dawo.
Daddy yace, "ashsha haba Aliyu yaushe zaka
daka shirme na mata, ai hakuri zakayi ka
rarrasheta tunda kai ka tabota, kayi mata laifi
babba, don su mata wannan shine babban laifi da
zakayi wa matarka."
don haka ni yanzu zanje wajen babanta mu
tattauna na bashi hakuri kai kuma da daddare
saika je ka tafi da matarka."
Aliyu ya rissina ya amsa masa tare da yi masa
godiya.
Daddy yayi sallama gidan Alh haruna, alh ya fito
da fara'arsa, ya bude dakin saukar bakinsa suka
shiga, bayan su gaisa daddy yake cewa, "nazo
bikon mansura ne, na tambaya dazu aka cemin ai
har yanzu tana gida bata koma dakinta ba."
Alh haruna mutumin arziki, yace kasan halin mata
sai hakuri, hauka tayi masa yace tayi zamanta a
gidansu. To in banda rashin hankali ma ya za'ayi
da hukuncin ubangiji. Allah ya kaddara hakan tun
fil azal, towa ya isa yaja da hukuncin ubangiji?
Daddy yace"hakane fa don wallahi naso na sa shi
ya hakura da auren zainab ya rinka yi min
magiya dana hakura na kyaleshi, to ya za ayi da
hukuncin ubangiji. Don Allah kuyi hakuri Alh, in
ajima Aliyu zai zo ya duketa su tafi gida." Alh ya
washe baki yace, wallahi bakomai saiya zo din."
da Aliyu yazo Alh ya hadasu da mansura yayi
musu fada. Ya dauko mansura suka taho gida.
Tunda suka taho take yi masa kuka, yace "haba
mansura, kin san bana son kuka, laifi ne kince
nayi kuma na baki hakuri ba sai ki yafe minba."
beli. Kuma yanzu ma ka saurari zuwan kana nan sojoji,
zasu zo su koya maka
hankali." ya cire wayar da kunnansa yayi cilli da ita ta daki
bango ta tarwatse, ya karasa gurin ya ciro sim card din ciki
ya kakkarya shi gutsi-gutsi ya
watsar a wajen. Ya dago kansa yana mata wani
irin kallo, yace wannan ya zamo na karshe, idan
na kuma gani kina waya ko kina magana da wani
sai ranki ya baci." ya juya ya fita.
Ta dafe kanta tana kukanta. Ni'ima ta dawo
dakin da tun shigowar yaya Aliyu data ga sababin
da yake yi ta zame jikinta ta gudu, don kada ya
huce akanta."
ni'ima ta zauna kusa da ita ta dafa ta, tace meye
na kuka, ke matsalarki kenan saurin kuka."
tace, haba yaya ni'ima, kin san sarai yaya Aliyu
ya fiya saurin fushi da zafin zuciya, ni kuma bana
so naga bacin ransa balle kuma ace ni na bata
masa, taya za ayi zaman aure a haka?
Ni'ima tace haba zainab kefa mai hakuri ce zaki
iya zama da yaya Aliyu, don kinfi kowa iya gudun
bacin ransa. Ni sai yanzu ma na fahimta ashe du
tsanani da yaya yake yi miki soyayya ce da
kishinki da yake yi, ni wallahi ban taba ganin
amarya da ango da suka dace da juna ba irin ke
da yaya."
idonta yayi narai-narai hawaye ya sake zubowa
tace, "ke yaya ni'ima haka zaki rinka yi min?
Ta fashe da kukanta. Ni'ima ta rungumota tana
rarrashinta, "to shikenan kiyi hakuri na daina, ba
zan kuma ba."
du wayanci kawayen zainab ta gayyace su bikin
ni'ima, to da abun ya zamo haka ya hade da
nata, sai babbar kawarta hauwa Rabi'u ta rinka
yiwa kawayensu waya tana sanar musu tare da
basu hakuri na rashin ganin kati. Du da haka
saida Aliyu ya sanar a gidajen radio, saboda na
nesa kawayenta da basu sani ba.
Ranar jumma'a akayi mata kamu, kamun da ya
bada mamaki saboda cikar kawayenta da 'yan
uwanta suka yi, sai da aka fara saukar Qur'ani
sannan aka kamata."
daga nan wata malama ta bude filin da dan
wa'azinta (kusan hakkin miji akan matarsa ne
wa'azin kuma inaga munyi a baya basai na
maimaita ba).
Malamar nan tai ta wa'azi da fadakarwa akan
aure, wanda tunda aka fara zainab take kuka, dan
jikinta har rawa yake yi. Du da tasan hakkokin
miji akan matarsa babu abunda malamansu na
islamiya basu koya musu ba, amma wa'azin
malamar nan ya shigeta.
Yanzu taya zata hada jiki da yayanta Aliyu harta
kwanta gado daya dashi? Ya salam! Allah kaika
san abunda kake nufi da auren nan, Allah ka bani
ikon biyayya ga mijina.
Ranar asabar tun asuba akayi wa zainab da
ni'ima gyaran jiki, inda jikinsu ya fara laushi da
tsantsi, fuskarsu kuwa kamar kwan lantarki dan
kyau.
A wajen walima shiga iri daya akayi musu, wani
dankareren abu me kyalli da walwali pink, da
gwagwaro pink, dutsen da suka sa a hannu da
wuya duk pink, takalmi da jaka duk pink, sunyi
kyau sosai.
Walimar ta tara kyawawan 'yan mata gogaggu
masu takama da ayar Allah.
Domin ayau ma wani wa'azin aka kuma yi mai
shigarwa, daga nan wani babban malami yayi
lakca wadda ya ladftar da zuciyar mai saurare, ya
dasa tsoron Allah a zukatan wanda suka saurara.
Daga karshe aka rufe da addu'a, aka yiwa
angwaye da amare addu'ar Allah basu zaman
lafiya. Amaren suka rinka zagaye tebir-tebir suna
gaisawa da kawayensu, suna yi musu godiya da
damar da suka samu ta hallartar bikinsu.
Aunty sadiya tana ta raba manyan bokitai da
farantai, da kofunan shayi na tangaram. Sun so
yin kalanda, Aliyu ya hana wai baza aje a lika
masa hoton matarsa a wani waje ba, wani gardin
ya kalleta yayi sha'awarta ba.
Da mangariba daddyn zainab ya kira Aliyu ya
tambayeshi ya maganar mansura? Aliyu ya gaya
masa yanda sukayi, yace randa ta gaji da zaman
gidan nasu saita dawo.
Daddy yace, "ashsha haba Aliyu yaushe zaka
daka shirme na mata, ai hakuri zakayi ka
rarrasheta tunda kai ka tabota, kayi mata laifi
babba, don su mata wannan shine babban laifi da
zakayi wa matarka."
don haka ni yanzu zanje wajen babanta mu
tattauna na bashi hakuri kai kuma da daddare
saika je ka tafi da matarka."
Aliyu ya rissina ya amsa masa tare da yi masa
godiya.
Daddy yayi sallama gidan Alh haruna, alh ya fito
da fara'arsa, ya bude dakin saukar bakinsa suka
shiga, bayan su gaisa daddy yake cewa, "nazo
bikon mansura ne, na tambaya dazu aka cemin ai
har yanzu tana gida bata koma dakinta ba."
Alh haruna mutumin arziki, yace kasan halin mata
sai hakuri, hauka tayi masa yace tayi zamanta a
gidansu. To in banda rashin hankali ma ya za'ayi
da hukuncin ubangiji. Allah ya kaddara hakan tun
fil azal, towa ya isa yaja da hukuncin ubangiji?
Daddy yace"hakane fa don wallahi naso na sa shi
ya hakura da auren zainab ya rinka yi min
magiya dana hakura na kyaleshi, to ya za ayi da
hukuncin ubangiji. Don Allah kuyi hakuri Alh, in
ajima Aliyu zai zo ya duketa su tafi gida." Alh ya
washe baki yace, wallahi bakomai saiya zo din."
da Aliyu yazo Alh ya hadasu da mansura yayi
musu fada. Ya dauko mansura suka taho gida.
Tunda suka taho take yi masa kuka, yace "haba
mansura, kin san bana son kuka, laifi ne kince
nayi kuma na baki hakuri ba sai ki yafe minba."